< Josué 9 >

1 Or dès que tous les Rois qui étaient au deçà du Jourdain, en la montagne, et en la plaine, et sur tout le rivage de la grande mer, jusques contre le Liban, [savoir] les Héthiens, les Amorrhéens, les Cananéens, les Phérésiens, les Héviens, et les Jébusiens, eurent appris [ces choses],
To, sa’ad da dukan sarakunan yammancin Urdun suka ji waɗannan abubuwa, sai waɗanda suke kan tudu, da na cikin kwari a yammanci, da dukan waɗanda suke gefen Bahar Rum har zuwa Lebanon (sarakunan Hittiyawa, Amoriyawa, Kan’aniyawa, Ferizziyawa, Hiwiyawa da Yebusiyawa)
2 Ils s'assemblèrent tous pour faire la guerre à Josué et à Israël, d'un commun accord.
suka haɗa kansu don su yaƙi Yoshuwa da Isra’ila.
3 Mais les habitants de Gabaon ayant entendu ce que Josué avait fait à Jérico, et à Haï;
Amma da mutanen Gibeyon suka ji abin da Yoshuwa ya yi wa Yeriko da Ai,
4 Usèrent de finesse, car ils se mirent en chemin, et contrefirent les ambassadeurs, et prirent de vieux sacs sur leurs ânes, et de vieux outres de vin qui avaient été rompus, et qui étaient rapetassés.
sai suka shirya wata dabara ta ruɗu, suka shirya ɗan abinci don tafiya, suka ɗauki tsofaffin buhuna a kan jakunansu da tsofaffin salkuna na ruwan inabi, yagaggu da suka sha ɗinki.
5 Et [ils avaient] en leurs pieds de vieux souliers raccommodés, et de vieux habits sur eux; et tout le pain de leur provision était sec, et moisi.
Suka sa tsofaffin takalman da suka sha gyara, suka sa tsofaffin tufafi. Dukan abincinsu na tafiya ya bushe ya yi fumfuna.
6 Et étant venus à Josué au camp en Guilgal, ils lui dirent, et aux principaux d'Israël: Nous sommes venus d'un pays éloigné; maintenant donc traitez alliance avec nous.
Sai suka je wurin Yoshuwa a sansanin Gilgal suka ce masa da mutanen Isra’ila, “Daga ƙasa mai nisa muka fito, yanzu fa, sai ku yi alkawari da mu.”
7 Et les principaux d'Israël répondirent à ces Héviens: Peut-être que vous habitez parmi nous; et comment traiterions-nous alliance avec vous?
Mutanen Isra’ila kuwa suka ce wa Hiwiyawa, “Wataƙila kuna kusa da mu, ta yaya za mu yi alkawari da ku?”
8 Mais ils dirent à Josué: Nous sommes tes serviteurs. Alors Josué leur dit: Qui êtes-vous? et d'où venez-vous?
Suka ce wa Yoshuwa, “Mu bayinku ne.” Amma Yoshuwa ya tambaye su ya ce, “Ku wane ne, kuma daga ina kuka zo?”
9 Ils lui répondirent: Tes serviteurs sont venus d'un pays fort éloigné, sur la renommée de l'Eternel ton Dieu; car nous avons entendu sa renommée, et toutes les choses qu'il a faites en Egypte;
Suka amsa suka ce, “Bayinka sun zo ne daga ƙasa mai nisa gama Ubangiji Allahnka ya yi suna sosai. Gama mun ji labarin abubuwan da ya yi. Dukan abubuwan da ya yi a Masar
10 Et tout ce qu'il a fait aux deux Rois des Amorrhéens, qui étaient au delà du Jourdain, à Sihon Roi de Hesbon, et à Hog Roi de Basan qui [demeurait] à Hastaroth.
da kuma duk abubuwan da ya yi wa sarakuna biyu na Amoriyawa gabas da Urdun, Sihon sarkin Heshbon, da Og sarkin Bashan wanda ya yi mulki a Ashtarot.
11 Et nos anciens et tous les habitants de notre pays nous ont dit ces mêmes paroles-ci: Prenez avec vous de la provision pour le chemin, et allez au-devant d'eux, et leur dites: Nous sommes vos serviteurs, et maintenant traitez alliance avec nous.
Dattawanmu da duk mazaunan ƙasar, suka ce mana, ‘Ku ɗauki abincin tafiyar da za ku riƙe; ku je ku same su ku ce musu, “Mu bayinku ne, ku yi alkawari da mu.”’
12 C'est ici notre pain. Nous le prîmes de nos maisons tout chaud pour notre provision, le jour que nous en sortîmes pour venir vers vous; mais maintenant voici, il est devenu sec, et moisi.
Abincin tafiyan nan namu yana da ɗumi lokacin da muka kintsa tashi daga gida a ranar da za mu kama hanya zuwa wurinku. Amma yanzu duba yadda ya bushe, ya yi fumfuna.
13 Et ce sont ici les outres de vin que nous avions remplies tout neufs, et voici ils se sont rompus; et nos habits et nos souliers sont usés à cause du long chemin.
Waɗannan salkuna kuma da muka cika ruwan inabi, sababbi ne amma duba yadda suka yayyage. Tufafinmu da takalmanmu duk sun yayyage don doguwar tafiya.”
14 Ces hommes donc avaient pris de la provision; mais on ne consulta point la bouche de l'Eternel.
Mutanen Isra’ila suka ɗiba daga cikin abincin tafiyar amma ba su nemi nufin Ubangiji ba.
15 Car Josué fit la paix avec eux, et traita avec eux [cette] alliance, qu'il les laisserait vivre; et les principaux de l'assemblée leur en firent le serment.
Sa’an nan Yoshuwa ya yi alkawari zaman salama da su, cewa ba zai kashe su ba, sai shugabannin mutanen Isra’ila kuwa suka tabbatar musu da haka ta wurin yin rantsuwa.
16 Mais il arriva trois jours après l'alliance traitée avec eux, qu'ils apprirent que c'étaient leurs voisins, et qu'ils habitaient parmi eux.
Kwana uku bayan sun yi alkawari da Gibeyonawa, sai Isra’ilawa suka ji cewa Gibeyonawa maƙwabtansu ne, waɗanda suke zaune kurkusa da su.
17 Car les enfants d'Israël partirent, et vinrent en leurs villes le troisième jour. Or leurs villes étaient Gabaon, Képhira, Beeroth, et Kirjath-jéharim.
Saboda haka Isra’ilawa suka tashi a rana ta uku suke je biranen mutanen, wato, Gibeyon, Kefira, Beyerot da Kiriyat Yeyarim.
18 Et les enfants d'Israël ne les frappèrent point, parce que les principaux de l'assemblée leur avaient fait serment par l'Eternel le Dieu d'Israël; mais toute l'assemblée murmura contre les principaux.
Amma Isra’ilawa ba su kai musu hari ba domin shugabanninsu sun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila. Mutane Isra’ila duka kuwa suka yi gunaguni a kan shugabannin.
19 Alors tous les principaux dirent à toute l'assemblée: Nous leur avons fait serment par l'Eternel le Dieu d'Israël; c'est pourquoi nous ne les pouvons pas maintenant toucher.
Amma shugabanni suka amsa musu suka ce, “Mun rantse musu da sunan Ubangiji, Allah na Isra’ila, saboda haka ba za mu taɓa su ba yanzu.
20 Faisons leur ceci, et qu'on les laisse vivre, afin qu'il n'y ait point de colère contre nous, à cause du serment que nous leur avons fait.
Ga abin da za mu yi musu, za mu bar su da rai don kada fushin Allah yă sauka a kanmu gama mun riga mun rantse musu.”
21 Les principaux donc leur dirent qu'ils vivraient; mais ils furent employés à couper le bois, et à puiser l'eau pour toute l'assemblée, comme les principaux [le] leur dirent.
Suka ƙara da cewa, “Mu bar su da rai, amma bari su zama masu yankan itace da masu ɗibo mana ruwa.” Haka shugabannin suka cika alkawarinsu.
22 Car Josué les appela, et leur parla, en disant: Pourquoi nous avez-vous trompés, [en nous] disant: Nous sommes fort éloignés de vous; puisque vous habitez parmi nous?
Yoshuwa kuwa ya aika aka kira Gibeyonawa ya ce musu, “Don me kuka ruɗe mu kuka ce, ‘Mun zo ne daga wuri mai nisa,’ bayan kuwa kuna nan kurkusa da mu?
23 Maintenant donc vous êtes maudits, et il y aura toujours des esclaves d'entre vous, et des coupeurs de bois, et des puiseurs d'eau pour la maison de mon Dieu.
Yanzu ku la’anannu ne. Ba za ku daina zama mana masu yankan itace da kuma masu ɗebo ruwa domin haikalin Allahnmu ba.”
24 Et ils répondirent à Josué, et dirent: Après qu'il a été exactement rapporté à tes serviteurs, que l'Eternel ton Dieu avait commandé à Moïse son serviteur qu'on vous donnât tout le pays, et qu'on exterminât tous les habitants du pays de devant vous, nous avons craint extrêmement pour nos personnes à cause de vous, et nous avons fait ceci.
Suka amsa wa Yoshuwa suka ce, “An gaya wa bayinka dalla-dalla yadda Ubangiji Allahnka ya umarci bawansa Musa yă ba ka ƙasar duka, ka kuma kashe duk masu zama a cikinta, muka ji tsoro cewa za ka kashe mu shi ya sa muka yi haka.
25 Et maintenant nous voici entre tes mains, fais nous comme il te semblera bon et juste de nous faire.
Yanzu, a hannunka muke, ka yi duk abin da ka ga ya yi maka kyau.”
26 Il leur fit donc ainsi, et il les délivra de la main des enfants d'Israël, tellement qu'ils ne les tuèrent point.
Yoshuwa kuwa ya cece su daga hannun Isra’ilawa, har ba su kashe su ba.
27 Et en ce jour-là Josué les établit coupeurs de bois et puiseurs d'eau pour l'assemblée, et pour l'autel de l'Eternel, jusqu'à aujourd'hui dans le lieu qu'il choisirait.
A ranar Yoshuwa ya sa Gibeyonawa suka zama masu yankan itace da ɗebo ruwa wa jama’ar Isra’ila da kuma domin haikalin Ubangiji a inda Ubangiji zai zaɓa. Abin da suke ke nan har wa yau.

< Josué 9 >