< Jérémie 42 >

1 Alors tous les Capitaines des gens de guerre, et Johanan fils de Karéah, et Jézania fils de Hosahia, et tout le peuple, depuis le plus petit jusqu’au plus grand, s'approchèrent,
Sa’an nan dukan shugabannin sojoji, haɗe da Yohanan ɗan Kareya da Yezaniya ɗan Hoshahiya, da dukan mutane daga ƙarami zuwa babba, suka zo wurin
2 Et dirent à Jérémie le Prophète: que notre supplication soit reçue de toi, et fais requête à l'Eternel ton Dieu pour nous, [savoir] pour tout ce reste-ci; car de beaucoup [de monde que nous étions] nous sommes restés peu, comme tes yeux nous voient;
Irmiya annabi suka ce masa, “Muna roƙonka ka ji kukanmu ka kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnka saboda dukan wannan raguwar mutane. Gama kamar yadda kake gani yanzu, ko da yake dā muna da yawa, yanzu ɗan kaɗan muka rage.
3 Et que l'Eternel ton Dieu nous déclare le chemin par lequel nous aurons à marcher, et ce que nous avons à faire.
Ka yi addu’a cewa Ubangiji Allahnka zai faɗa mana inda za mu tafi da kuma abin da za mu yi.”
4 Et Jérémie le Prophète leur répondit: J'ai entendu [votre demande]; voici, je m'en vais faire requête à l'Eternel votre Dieu selon vos paroles; et il arrivera que je vous déclarerai tout ce que l'Eternel vous répondra, et je ne vous en cacherai pas un mot.
Sai Irmiya ya amsa ya ce, “Na ji ku, tabbatacce zan yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yadda kuka roƙa; zan faɗa muku duk abin da Ubangiji ya faɗa ba kuwa zan ɓoye muku kome ba.”
5 Et ils dirent à Jérémie: l'Eternel soit pour témoin véritable et fidèle entre nous, si nous ne faisons selon toutes les paroles, pour lesquelles l'Eternel ton Dieu t'aura envoyé vers nous.
Sa’an nan suka ce wa Irmiya, “Ubangiji ya zama shaida na gaskiya da kuma aminci a kanmu in ba mu yi bisa da duk abin da Ubangiji Allahnka ya aike ka ka faɗa mana ba.
6 Soit bien, soit mal, nous obéirons à la voix de l'Eternel notre Dieu, vers lequel nous t'envoyons; afin qu'il nous arrive du bien quand nous aurons obéi à la voix de l'Eternel notre Dieu.
Ko ya gamshe mu ko bai gamshe mu ba, za mu yi biyayya da Ubangiji Allahnmu, ga wanda muke aikan ka, saboda ya zama mana da amfani, gama za mu yi biyayya da Ubangiji Allahnmu.”
7 Et il arriva au bout de dix jours que la parole de l'Eternel fut [adressée] à Jérémie.
Bayan kwana goma sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya.
8 Et il appela Johanan fils de Karéah, et tous les Capitaines des gens de guerre qui étaient avec lui, et tout le peuple, depuis le plus petit jusqu'au plus grand;
Saboda haka ya kira Yohanan ɗan Kareya da dukan shugabannin sojoji waɗanda suke tare da shi da dukan jama’a daga ƙarami zuwa babba.
9 Et leur dit: Ainsi a dit l'Eternel, le Dieu d'Israël, vers lequel vous m'avez envoyé pour présenter votre supplication devant lui.
Ya ce musu, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, wanda kuka aike ni gare shi don in gabatar da kukanku, yana cewa,
10 Si vous continuez à demeurer dans ce pays, je vous rétablirai, et je ne vous détruirai point; je vous [y] planterai, et je ne vous arracherai point, car je me suis repenti du mal que je vous ai fait.
‘In kuka zauna a wannan ƙasa, zan gina ku ba zan kuwa rushe ku ba; zan dasa ku ba kuwa zan tumɓuke ku ba, gama ina baƙin ciki a kan masifar da na aukar a kanku.
11 N'ayez point peur du Roi de Babylone, duquel vous avez peur; n'en ayez point peur, dit l'Eternel, car je suis avec vous pour vous sauver, et pour vous délivrer de sa main.
Kada ku ji tsoron sarkin Babilon, wanda kuke tsoro a yanzu. Kada ku ji tsoronsa, in ji Ubangiji, gama ina tare da ku zan kuma cece ku daga hannuwansa.
12 Même je vous ferai obtenir miséricorde, tellement qu'il aura pitié de vous, et vous fera retourner en votre pays.
Zan nuna muku jinƙai don yă nuna muku jinƙai ya kuma maido da ku ƙasarku.’
13 Que si vous dites: nous ne demeurerons point en ce pays, et nous n'écouterons point la voix de l'Eternel notre Dieu;
“Amma fa, in kuka ce, ‘Ba za mu zauna a wannan ƙasa ba,’ ta haka kuka kuma nuna rashin biyayya ga Ubangiji Allahnku,
14 En disant: non; mais nous irons au pays d'Egypte, afin que nous ne voyions point de guerre, et que nous n'entendions point le son de la trompette, et que nous n'ayons point disette de pain; et nous demeurerons là.
in kuma kuka ce, ‘A’a, za mu tafi mu zauna a Masar, inda ba za mu ga yaƙi ko mu ji ƙarar ƙaho ko mu ji yunwa ba,’
15 A cause de cela écoutez maintenant la parole de l'Eternel, [vous] les restes de Juda. Ainsi a dit l'Eternel des armées, le Dieu d'Israël: si vous vous préparez pour aller en Egypte, et que vous y entriez pour y séjourner;
to, ku ji maganar Ubangiji, ya raguwar Yahuda. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘In kun ƙudura ku tafi Masar kuka kuma tafi kun zauna a can,
16 Il arrivera que l'épée dont vous avez peur vous attrapera là au pays d'Egypte; et la famine que vous craignez si fort vous suivra en Egypte, tellement que vous y mourrez.
takobin da kuke tsoro zai same ku a can, kuma yunwar da kuke tsoro za tă bi ku zuwa Masar, a can kuwa za ku mutu.
17 Et il arrivera que tous les hommes qui auront fait les démarches nécessaires pour entrer en Egypte afin d'y séjourner, mourront par l'épée, par la famine, et par la mortalité; nul d'eux ne restera, ni échappera de devant le mal que je m'en vais faire venir sur eux.
Tabbatacce, duk waɗanda suka ƙudura suka tafi Masar su zauna a can za su mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba; ba ko ɗayansu zai tsira ko ya kuɓuta wa masifar da zan aukar a kansu.’
18 Car ainsi a dit l'Eternel des armées, le Dieu d'Israël: comme ma colère et ma fureur a fondu sur les habitants de Jérusalem, ainsi ma fureur fondra sur vous, quand vous serez entrés en Egypte; et vous serez en exécration, et en étonnement, et en malédiction, et en opprobre; et vous ne verrez plus ce lieu-ci.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kamar yadda na kwararo fushina da hasalata a kan mazaunan Urushalima, haka kuma zan kwararo fushina a kanku sa’ad da kuka tafi Masar. Za ku zama abin la’ana da abin tsoro, abin ƙyama da abin ba’a; ba za ku ƙara ganin wannan wuri ba.’
19 Vous, les restes de Juda, l'Eternel a parlé contre vous: n'entrez point en Egypte, vous sentirez certainement que je vous en ai sommés aujourd'hui.
“Ya ku raguwar Yahuda, Ubangiji ya ce muku, ‘Kada ku je Masar.’ Ku tabbatar da wannan. Na gargaɗe ku yau
20 Car vous avez usé de fraude contre vous-mêmes quand vous m'avez envoyé vers l'Eternel votre Dieu, en me disant: fais requête pour nous envers l'Eternel notre Dieu, et nous déclare tout ce que l'Eternel notre Dieu te dira, et nous [le] ferons.
cewa in kun yi kuskure sa’ad da kuka aike ni wurin Ubangiji Allahnku kuka kuma ce, ‘Yi mana addu’a ga Ubangiji Allahnmu; ka faɗa mana duk abin da ya faɗa za mu kuwa aikata.’
21 Et je vous [l']ai déclaré aujourd'hui; mais vous n'avez point écouté la voix de l'Eternel votre Dieu, ni rien de tout ce pour quoi il m'a envoyé vers vous.
Na faɗa muku yau, amma har yanzu ba ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku cikin dukan abin da ya aiko ni in faɗa muku ba.
22 Maintenant donc sachez certainement que vous mourrez par l'épée, par la famine, et par la mortalité, au lieu auquel vous avez désiré d'entrer, pour y séjourner.
Saboda haka yanzu, ku tabbatar da wannan. Za ku mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba a wurin da kuke so ku tafi ku zauna.”

< Jérémie 42 >