< Jérémie 36 >

1 Or il arriva, en la quatrième année de Jéhojakim fils de Josias Roi de Juda, que cette parole fut [adressée] par l'Eternel à Jérémie, en disant:
A shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji cewa,
2 Prends-toi un rouleau de livre, et y écris toutes les paroles que je t'ai dites contre Israël, et contre Juda, et contre toutes les nations, depuis le jour que je t'ai parlé, [c'est-à-dire], depuis les jours de Josias, jusqu’à aujourd'hui.
“Ka ɗauki littafi ka rubuta dukan maganganun da na yi maka game da Isra’ila, Yahuda da kuma dukan sauran al’ummai daga lokacin da na fara maka magana a mulkin Yosiya har zuwa yanzu.
3 Peut-être que la maison de Juda fera attention à tout le mal que je pense de leur faire, afin que chacun se détourne de sa mauvaise voie, et que je leur pardonne leur iniquité, et leur péché.
Wataƙila sa’ad da mutanen Yahuda suka ji game da kowace masifar da na shirya in auka musu, kowa ya juya daga muguwar hanyarsa; sa’an nan in gafarta musu muguntarsu da kuma zunubinsu.”
4 Jérémie donc appela Baruc, fils de Nérija, et Baruc écrivit de la bouche de Jérémie dans le rouleau de livre toutes les paroles de l'Eternel, lesquelles il lui dicta.
Saboda haka Irmiya ya kira Baruk ɗan Neriya, yayinda Irmiya yake fadar dukan waɗannan maganganun da Ubangiji ya faɗa masa, Baruk ya rubuta su a littafin.
5 Puis Jérémie donna charge à Baruc, en disant: je suis retenu, [et] je ne puis entrer dans la maison de l'Eternel.
Sai Irmiya ya ce wa Baruk, “An hana ni, ba zan tafi haikalin Ubangiji ba.
6 Tu y entreras donc, et tu liras dans le rouleau que tu as écrit, [et que je t'ai dicté] de ma bouche, les paroles de l'Eternel, le peuple l'entendant, en la maison de l'Eternel, au jour du jeûne; tu les liras, dis-je, tous ceux de Juda, qui seront venus de leurs villes, l'entendant.
Saboda haka ka tafi gidan Ubangiji a ranar azumi ka karanta wa mutane daga littafin maganar Ubangiji da na shibta maka ka rubuta. Ka karanta su ga dukan mutanen Yahuda waɗanda suka zo daga garuruwansu.
7 Peut-être que leur supplication sera reçue devant l'Eternel, et que chacun se détournera de sa mauvaise voie; car la colère et la fureur que l'Eternel a déclarée contre ce peuple [est] grande.
Wataƙila za su kawo kukansu a gaban Ubangiji, kowanne kuma ya juya daga muguwar hanyarsa, gama fushi da hasalar da Ubangiji ya furta a kan mutanen nan yana da girma.”
8 Baruc donc fils de Nérija fit selon tout ce que Jérémie le Prophète lui avait commandé, lisant dans le livre les paroles de l'Eternel, en la maison de l'Eternel.
Sai Baruk ɗan Neriya ya yi dukan abin da annabi Irmiya ya ce ya yi; a haikalin Ubangiji kuwa ya karanta maganar Ubangiji daga littafin
9 Or il arriva en la cinquième année de Jéhojakim fils de Josias Roi de Juda, au neuvième mois, qu'on publia le jeûne en la présence de l'Eternel à tout le peuple de Jérusalem et à tout le peuple qui était venu des villes de Juda à Jérusalem.
A watan tara na shekara ta biyar ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, an yi shela a yi azumi a gaban Ubangiji ga dukan mutanen Urushalima da waɗanda suka zo daga garuruwan Yahuda.
10 Et Baruc lut dans le livre les paroles de Jérémie, en la maison de l'Eternel, dans la chambre de Guémaria fils de Saphan, Secrétaire, dans le haut parvis, à l'entrée de la porte neuve de la maison de l'Eternel, tout le peuple l'entendant.
Daga ɗakin Gemariya ɗan Shafan magatakarda, wanda yake a fili na bisa a mashigin Sabuwar Ƙofar haikali, Baruk ya karanta wa dukan mutane a haikalin Ubangiji maganar Irmiya daga littafin.
11 Et quand Michée fils de Guémaria, fils de Saphan, eut ouï [par la lecture] du livre toutes les paroles de l'Eternel;
Sa’ad da Mikahiya ɗan Gemariya, ɗan Shafan, ya ji dukan maganar Ubangiji daga littafin,
12 Il descendit en la maison du Roi vers la chambre du Secrétaire, et voici tous les principaux y étaient assis, [savoir] Elisamah le Secrétaire, et Délaia fils de Sémahia, Elnathan fils de Hacbor, et Guémaria fils de Saphan, et Sédécias fils de Hanania, et tous les principaux.
sai ya sauka zuwa ɗakin magatakarda a fada, inda dukan fadawa suke zaune, Elishama magatakarda, Delahiya ɗan Shemahiya, Elnatan ɗan Akbor, Gemariya ɗan Shafan, Zedekiya ɗan Hananiya, da dukan sauran fadawa.
13 Et Michée leur rapporta toutes les paroles qu'il avait ouïes quand Baruc lisait au livre le peuple l'entendant.
Bayan Mikahiya ya faɗa musu kome da ya ji Baruk ya karanta wa mutane daga littafin,
14 C'est pourquoi tous les principaux envoyèrent vers Baruc, Jéhudi, fils de Néthania, fils de Sélemja, fils de Cusci, pour lui dire: prends en ta main le rouleau dans lequel tu as lu, le peuple l'entendant, et viens ici. Baruch donc fils de Nérija prit le rouleau en sa main, et vint vers eux.
sai dukan fadawan suka aiki Yehudi ɗan Netaniya, ɗan Shelemiya, ɗan Kushi, ya ce wa Baruk, “Ka zo tare da littafin da ka karanta wa mutane.” Saboda haka Baruk ɗan Neriya ya tafi wurinsu tare da littafin a hannunsa.
15 Et ils lui dirent: assieds-toi maintenant, et y lis, nous l'entendant; et Baruc lut, eux l'écoutant.
Suka ce masa, “Zauna, ka karanta mana littafin.” Sai Baruk ya karanta musu littafin.
16 Et il arriva que sitôt qu'ils eurent ouï toutes ces paroles, ils furent effrayés entre eux, et dirent à Baruc: nous ne manquerons point de rapporter au Roi toutes ces paroles.
Da suka ji dukan maganar, sai suka dubi juna a firgice suka ce wa Baruk, “Dole mu sanar da dukan maganan nan ga sarki.”
17 Et ils interrogèrent Baruc, en disant: déclare-nous maintenant comment tu as écrit toutes ces paroles-là de sa bouche.
Sa’an nan suka ce wa Baruk, “Faɗa mana yadda ka yi ka rubuta dukan wannan. Irmiya ne ya yi maka shibtar ta?”
18 Et Baruc leur dit: il me dictait de sa bouche toutes ces paroles, et je les écrivais avec de l'encre dans le livre.
Baruk ya amsa ya ce, “I, shi ne ya faɗa mini dukan wannan magana, na kuwa rubuta su a takarda.”
19 Alors les principaux dirent à Baruc: va, et te cache, toi et Jérémie, et que personne ne sache où vous serez.
Sa’an nan fadawan suka ce wa Baruk, “Kai da Irmiya ku je ku ɓuya. Kada ku bari wani ya san inda kuke.”
20 Puis ils s'en allèrent vers le Roi au parvis, mais ils mirent en garde le rouleau dans la chambre d'Elisamah le Secrétaire; et ils racontèrent toutes ces paroles, le Roi l'entendant.
Bayan da suka ajiye littafin a ɗakin Elishama magatakarda, sai suka tafi wurin sarki a fili suka sanar da shi kome.
21 Et le Roi envoya Jéhudi pour prendre le rouleau; et quand Jéhudi l'eut pris de la chambre d'Elisamah le Secrétaire, il le lut, le Roi et tous les principaux qui assistaient autour de lui l'entendant.
Sai sarki ya aiki Yehudi ya kawo littafin daga ɗakin Elishama magatakarda ya kuma karanta wa sarki da kuma dukan fadawan da suke tsaye kusa da shi.
22 Or le Roi était assis dans l'appartement d'hiver, au neuvième mois, et [il y avait] devant lui un brasier ardent.
A watan tara ne sarki kuwa yana zaune a gidansa na rani, wuta kuwa tana ci a kasko a gabansa.
23 Et il arriva qu'aussitôt que Jéhudi en eut lu trois ou quatre pages, le Roi le coupa avec le canif du Secrétaire, et le jeta au feu du brasier, jusqu'à ce que tout le rouleau fût consumé au feu qui [était] dans le brasier.
Duk sa’ad da Yehudi ya karanta sashi uku ko huɗu na littafin, sai sarkin ya sa wuƙa ya yanke su, ya zuba a wutar da take ci a kasko, da haka ya ƙone dukan littafin.
24 Et ni le Roi ni tous ses serviteurs qui entendirent toutes ces paroles n'en furent point effrayés, et ne déchirèrent point leurs vêtements.
Sai sarki da dukan masu yin masa hidima waɗanda suke jin maganan nan ba su firgita ba, balle su keta rigunansu.
25 Toutefois Elnathan, et Délaia, et Guémaria intercédèrent envers le Roi, afin qu'il ne brûlât point le rouleau, mais il ne les écouta point.
Ko da yake Elnatan, Delahiya da Gemariya sun roƙi sarki kada yă ƙone littafin, bai saurare su ba.
26 Même le Roi commanda à Jérahméel fils de Hammélec, et à Séraja fils de Hazriel, et à Sélemja fils de Habdéel, de saisir Baruc le secrétaire, et Jérémie le Prophète; mais l'Eternel les cacha.
A maimakon haka, sai sarki ya umarci Yerameyel ɗan sarki, Serahiya ɗan Azriyel da Shelemiya ɗan Abdeyel su kama Baruk marubuci da Irmiya annabi. Amma Ubangiji ya ɓoye su.
27 Et la parole de l'Eternel fut [adressée] à Jérémie, après que le Roi eut brûlé le rouleau, et les paroles que Baruc avait écrites de la bouche de Jérémie, en disant:
Bayan sarki ya ƙone littafin da ya ƙunshi maganar da Baruk ya rubuta daga shibtar Irmiya, sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
28 Prends encore un autre rouleau, et y écris toutes les premières paroles qui étaient dans le premier rouleau que Jéhojakim Roi de Juda a brûlé.
“Ka ɗauki wani littafi ka rubuta a kansa dukan maganar da littafi na farin ya ƙunsa, wanda Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone.
29 Et tu diras à Jéhojakim Roi de Juda: ainsi a dit l'Eternel: tu as brûlé ce rouleau, et tu as dit: pourquoi y as-tu écrit, en disant que le Roi de Babylone viendra certainement, et qu'il ravagera ce pays, et en exterminera les hommes et les bêtes?
Ka kuma faɗa wa Yehohiyakim sarkin Yahuda cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka ƙone wancan littafin ka kuma ce, “Don me ka rubuta a cikinsa, cewa lalle sarkin Babilon zai zo ya hallaka wannan ƙasa, zai kashe mutum duk da dabba?”
30 C'est pourquoi ainsi a dit l'Eternel touchant Jéhojakim Roi de Juda: il n'aura personne qui soit assis sur le trône de David, et son corps mort sera jeté de jour à la chaleur, et de nuit à la gelée.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji yana cewa game da Yehohiyakim sarkin Yahuda. Ba zai kasance da wani wanda zai zauna a kan gadon sarautar Dawuda ba; za a jefar da gawarsa ta sha zafi da rana da dare kuma ta sha matsanancin sanyi.
31 Je visiterai donc sur lui, et sur sa postérité, et sur ses serviteurs, leur iniquité; et je ferai venir sur eux, et sur les habitants de Jérusalem, et sur les hommes de Juda, tout le mal que je leur ai prononcé, et qu'ils n'ont point écouté.
Zan hukunta shi da kuma’ya’yansa da masu hidimarsa saboda muguntarsu; zan kawo kowace masifar da na furta a kansu da kuma waɗanda suke zama a Urushalima da na Yahuda, domin sun ƙi su saurara.’”
32 Jérémie donc prit un autre rouleau, et le donna à Baruc fils de Nérija Secrétaire, lequel y écrivit de la bouche de Jérémie toutes les paroles du livre que Jéhojakim Roi de Juda avait brûlé au feu, et plusieurs paroles semblables y furent encore ajoutées.
Sai Irmiya ta ɗauko wani littafi ya ba wa Baruk ɗan Neriya marubuci, kuma yayinda Irmiya yake shibtawa, Baruk ya rubuta a littafin dukan maganar da take a littafin da Yehohiyakim sarkin Yahuda ya ƙone. Ya kuma ƙara ire-iren maganganun nan a kansu.

< Jérémie 36 >