< Jérémie 21 >

1 La parole qui fut [adressée] à Jérémie de par l'Eternel, lorsque le Roi Sédécias envoya vers lui Pashur fils de Malkija, et Sophonie fils de Mahaséja Sacrificateur, pour [lui] dire:
Magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji sa’ad da Sarki Zedekiya ya aiki Fashhur ɗan Malkiya da firist Zefaniya ɗan Ma’asehiya gare shi. Suka ce masa,
2 Enquiers-toi maintenant de l'Eternel pour nous; car Nébucadnetsar Roi de Babylone combat contre nous; peut-être que l'Eternel agira pour nous selon toutes ses merveilles, et le fera retirer de nous.
“Yanzu ka roƙi mana Ubangiji saboda Nebukadnezzar sarkin Babilon yana kawo mana yaƙi. Wataƙila Ubangiji zai yi mana waɗansu abubuwa banmamaki kamar a lokacin baya don yă janye daga gare mu.”
3 Et Jérémie leur dit: vous direz ainsi à Sédécias:
Amma Irmiya ya amsa musu ya ce, “Ku faɗa wa Zedekiya cewa,
4 Ainsi a dit l'Eternel, le Dieu d'Israël: voici, je m'en vais faire retourner de dehors la muraille les instruments de guerre qui sont en vos mains, avec lesquels vous combattez contre le Roi de Babylone et contre les Caldéens qui vous assiègent, et je les ramasserai au milieu de cette ville.
‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yake cewa ina shirin juya kayan yaƙin da suke a hannuwanka a kanka, waɗanda kake amfani don ka yaƙi sarki Babilon da kuma Babiloniyawa waɗanda suka kewaye katangar birnin, zan kuwa tsiba kayan yaƙinka a tsakiyar birnin nan.
5 Et je combattrai contre vous avec une main étendue, et avec un bras puissant, avec colère, avec ardeur, et avec une grande indignation.
Ni da kaina zan yi yaƙi da kai da miƙaƙƙen hannu mai ƙarfi cikin fushi da hasala mai girma.
6 Et je frapperai les habitants de cette ville, les hommes, et les bêtes; [et] ils mourront d'une grande mortalité.
Zan kashe waɗanda suke zaune a wannan birni, mutane da dabbobi za su kuwa mutu da muguwar annoba.
7 Et après cela, dit l'Eternel, je livrerai Sédécias Roi de Juda, et ses serviteurs, et le peuple, et ceux qui seront demeurés de reste en cette ville de la mortalité, de l'épée, et de la famine, en la main de Nébucadnetsar Roi de Babylone, et en la main de leurs ennemis, et en la main de ceux qui cherchent leur vie; et il les frappera au tranchant de l'épée, il ne les épargnera point, il n'en aura point de compassion, il n'en aura point de pitié.
Bayan wannan, in ji Ubangiji, zan ba da Zedekiya sarkin Yahuda, fadawansa da kuma mutanen wannan birni waɗanda suka tsira daga annoba, takobi da kuma yunwa, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da kuma ga abokan gābansu waɗanda suke neman ransu. Zai kashe su da takobi; ba zai ji tausayinsu ko ya yi musu jinƙai ko ya yi juyayinsu ba.’
8 Tu diras aussi à ce peuple: ainsi a dit l'Eternel: voici, je mets devant vous le chemin de la vie, et le chemin de la mort.
“Bugu da ƙari, ka faɗa wa mutanen cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ga shi na sa a gabanku hanyar rai da hanyar mutuwa.
9 Quiconque se tiendra dans cette ville mourra par l'épée, ou par la famine, ou par la mortalité, mais celui qui en sortira, et se rendra aux Caldéens qui vous assiègent, vivra, et sa vie lui sera pour butin.
Duk wanda ya zauna a wannan birni zai mutu ta takobi, yunwa ko annoba. Amma duk wanda ya fita ya miƙa kansa ga Babiloniyawa waɗanda suka kewaye ku zai rayu; zai kuɓutar da ransa.
10 Car j'ai dressé ma face en mal et non en bien contre cette ville, dit l'Eternel, elle sera livrée en la main du Roi de Babylone, et il la brûlera par le feu.
Na ƙudura in yi wa wannan birni lahani ba alheri ba, in ji Ubangiji. Za a ba da shi a hannuwan sarki Babilon, zai kuwa hallaka shi da wuta.’
11 Et quant à la maison du Roi de Juda, écoutez la parole de l'Eternel.
“Ban haka ma, ka faɗa wa gidan sarauta na Yahuda cewa, ‘Ku saurari maganar Ubangiji;
12 Maison de David, ainsi a dit l'Eternel: faites justice dès le matin, et délivrez celui qui aura été pillé, d'entre les mains de celui qui lui fait tort, de peur que ma fureur ne sorte comme un feu, et qu'elle ne s'embrase, et qu'il n'y ait personne qui l'éteigne, à cause de la malice de vos actions.
Ya gidan Dawuda ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Ku yi gaskiya kowace safiya; ku kuɓuta daga hannun mai danniya wannan da aka yi wa fashi in ba haka ba hasalata za tă sauka ta kuma ci kamar wuta saboda muguntar da kuka aikata za tă ci babu wanda zai kashe ta.
13 Voici, j'en veux à toi, qui habites dans la vallée, [et qui es] le rocher du plat pays, dit l'Eternel; à vous qui dites: qui est-ce qui descendra contre nous, et qui entrera dans nos demeures?
Ina gāba da ku, mazaunan Urushalima, ku da kuke zama a bisa wannan kwari kan dutsen da yake a fili, in ji Ubangiji ku da kuke cewa, “Wa zai iya yaƙe mu? Wa zai iya shiga mafakarmu?”
14 Et je vous punirai selon le fruit de vos actions, dit l'Eternel; et j'allumerai le feu dans sa forêt, lequel consumera tout ce qui est à l'entour d'elle.
Zan hukunta ku gwargwadon ayyukanku, in ji Ubangiji. Zan sa wuta a kurminku da za tă cinye kome da yake kewaye da ku.’”

< Jérémie 21 >