< Isaïe 12 >

1 Et tu diras en ce jour-là; Eternel! je te célébrerai, parce qu'ayant été courroucé contre moi, ta colère s'est apaisée, et tu m'as consolé.
A wannan rana za ku ce, “Zan yabe ka, ya Ubangiji. Ko da yake a dā ka yi fushi da ni, amma yanzu ka daina fushi da ni ka kuwa ta’azantar da ni.
2 Voici, le [Dieu] Fort est ma délivrance, j'aurai confiance, et je ne serai point effrayé; car l'Eternel, l'Eternel [est] ma force et ma louange, et il a été mon Sauveur.
Tabbatacce Allah shi ne mai cetona; zan dogara gare shi ba kuwa zan ji tsoro ba. Ubangiji, Ubangiji, ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.”
3 Et vous puiserez des fontaines de cette délivrance des eaux avec joie.
Da farin ciki zan ɗebo ruwa daga rijiyoyin ceto.
4 Et vous direz en ce jour-là; Célébrez l'Eternel, réclamez son Nom, faites connaître parmi les peuples ses exploits, faites souvenir que son Nom est une haute retraite.
A wannan rana za ku ce, “Yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; a sanar da wannan abin da ya aikata a cikin al’ummai, a kuma yi shela cewa sunansa mai girma ne.
5 Psalmodiez à l'Eternel, car il a fait des choses magnifiques; cela est connu dans toute la terre.
Ku rera ga Ubangiji, gama ya aikata manyan abubuwa; bari a sanar da wannan ga dukan duniya.
6 Habitante de Sion, égaye-toi, et te réjouis avec chant de triomphe; car le Saint d'Israël est grand au milieu de toi.
Ku tā da murya ku kuma rera don farin ciki, ya ku mutanen Sihiyona, gama Mai Tsarki na Isra’ila da girma yake a cikinku.”

< Isaïe 12 >