< Esdras 8 >

1 Or ce sont ici les Chefs des pères, avec le dénombrement qui fut fait selon les généalogies, de ceux qui montèrent avec moi de Babylone, pendant le règne du Roi Artaxerxes;
Waɗannan su ne shugabannin iyalai, da kuma waɗanda suka dawo tare da ni daga Babilon a zamanin mulkin Sarki Artazerzes.
2 Des enfants de Phinées, Guersom; des enfants d'Ithamar, Daniel; des enfants de David, Hattus;
Daga zuriyar Finehas, Gershom ne shugaba; daga zuriyar Itamar, Daniyel ne shugaba; daga zuriyar Dawuda, Hattush
3 Des enfants de Sécania, qui était des enfants de Parhos, Zacharie, et avec lui, en faisant le dénombrement par leur généalogie selon les mâles, cent cinquante hommes.
ɗan zuriyar Shekaniya ne shugaba, daga zuriyar Farosh, Zakariya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 150;
4 Des enfants de Péhath-Moab, Eliehohénaï fils de Zérahia, et avec lui deux cents hommes;
daga Fahat-Mowab, Eliyehoyenai ɗan Zerahiya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 200;
5 Des enfants de Sécania, le fils de Jahaziël, et avec lui trois cents hommes;
daga zuriyar Zattu, Shekaniya ɗan Yahaziyel ne shugaba, tare da shi akwai mutum 300;
6 Des enfants de Hadin, Hébed fils de Jonathan, et avec lui cinquante hommes;
daga zuriyar Adin, Ebed ɗan Yonatan ne shugaba, tare da shi akwai mutum 50;
7 Des enfants de Hélam, Esaïe, fils de Hathalia, et avec lui soixante-dix hommes;
daga zuriyar Elam, Yeshahiya ɗan Ataliya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 70;
8 Des enfants de Sépharia, Zébadia fils de Micaël, et avec lui quatre-vingts hommes;
daga zuriyar Shefatiya, Zebadiya ɗan Mika’ilu ne shugaba, tare da shi akwai mutum 80;
9 Des enfants de Joab, Habadia fils de Jéhiël, et avec lui deux cent dix-huit hommes;
daga iyalin Yowab, Obadiya ɗan Yehiyel ne shugaba, tare da shi akwai mutum 218;
10 Des enfants de Sélomith, le fils de Josiphia, et avec lui cent soixante hommes;
daga Bani, Shelomit ɗan Yosifiya ne shugaba, tare da shi akwai mutum 160;
11 Des enfants de Bébaï, Zacharie fils de Bébaï, et avec lui vingt-huit hommes;
daga Bebai, Zakariya ɗan Bebai ne shugaba, tare da shi akwai mutum 28;
12 Des enfants de Hazgad, Johanan, fils de Katan, et avec lui cent et dix hommes;
daga iyalin Azgad, Yohanan ɗan Hakkatan ne shugaba, tare da shi akwai mutum 110;
13 Des enfants d'Adonicam, les derniers, desquels les noms sont Eliphelet, Jéhiël, et Sémahia, et avec eux soixante hommes.
zuriya ta Adonikam ne suka zo daga ƙarshe, sunayensu kuwa su ne Elifelet, Yehiyel da Shemahiya, tare da su akwai mutum 60;
14 Des enfants de Bigvaï, Huthaï, Zabbud, et avec eux soixante-dix hommes.
daga zuriyar Bigwai, Uttai da Zakkur ne shugabanni, tare da su akwai mutum 70.
15 Et je les assemblai près de la rivière, qui se rend à Ahava, et nous y demeurâmes trois jours. Puis je pris garde au peuple et aux Sacrificateurs, et je n'y trouvai aucun des enfants de Lévi.
Na kuma tattara su a bakin rafi wanda yake gangarawa zuwa Ahawa, muka kafa sansani a can kwana uku. Da na bincika cikin mutane da firistoci, sai na tarar babu Lawiyawa.
16 Et ainsi j'envoyai d'entre les principaux Elihéser, Ariel, Sémahia, Elnathan, Jarib, Elnathan, Nathan, Zacharie, et Mésullam, avec Jojarib et Elnathan, docteurs.
Saboda haka sai na aika a kira Eliyezer, da Ariyel, da Shemahiya, da Elnatan, da Yarib, da Natan, da Zakariya, da Meshullam waɗanda su ne shugabanni. Na kuma sa a kira Yohiyarib da Elnatan waɗanda masana ne.
17 Et je leur donnai des ordres pour Iddo, principal chef, [qui demeurait] dans le lieu de Casiphia; et je mis en leur bouche les paroles qu'ils devaient dire à Iddo, [et] à son frère, Néthiniens, dans le lieu de Casiphia, afin qu'ils nous fissent venir des ministres pour la maison de notre Dieu.
Na sa su je wurin Iddo wanda yake shugaba a Kasifiya. Aka gaya musu abin da za su gaya wa Iddo da’yan’uwansa masu aiki a haikali a Kasifiya don su aiko mana waɗanda za su yi mana hidima a haikalin Allahnmu.
18 Et ils nous amenèrent, selon que la main de notre Dieu était bonne sur nous, un homme intelligent, d'entre les enfants de Mahli, fils de Lévi, fils d'Israël; [savoir] Sérébia, avec ses fils et ses frères, [qui furent] dix-huit hommes.
Da yake Allah yana tare da mu, sai suka aiko mana da Sherebiya, wanda ya iya aiki, shi daga zuriyar Mali ɗan Lawi ne, ɗan Isra’ila. Sai ya zo tare da’ya’yansa da kuma’yan’uwansa. Dukansu dai mutum 18 ne.
19 Et Hasabia, et avec lui Esaïe, d'entre les enfants de Mérari, ses frères, et leurs enfants, vingt hommes.
Suka kuma aika da Hashabiya tare da Yeshahiya daga zuriyar Merari, da’yan’uwansu da kuma’ya’yansu, su kuma mutum 20 ne.
20 Et des Néthiniens, que David et les principaux du peuple avaient assignés pour le service des Lévites, deux cent et vingt Néthiniens, qui furent tous nommés par leurs noms.
Sun kuma kawo masu aiki a haikali mutum 220, ƙungiyar da Dawuda da abokan aikinsa suka keɓe don su taimaki Lawiyawa aiki. Duk aka rubuta waɗannan da sunayensu.
21 Et je publiai là le jeûne auprès de la rivière d'Ahava, afin de nous humilier devant notre Dieu, le priant de nous donner un heureux voyage pour nous, et pour nos familles, et pour tous nos biens.
A can, a bakin rafin Ahawa, na sa mu yi azumi, domin mu ƙasƙantar da kanmu a gaban Allah, mu kuma roƙe shi yă kiyaye mana hanya, da mu da’ya’yanmu da kayanmu duka.
22 Car j'eus honte de demander au Roi des forces et des gens de cheval pour nous défendre des ennemis par le chemin; à cause que nous avions dit au Roi en termes exprès: La main de notre Dieu est favorable à tous ceux qui l'invoquent; mais sa force et sa colère est contre ceux qui l'abandonnent.
Na ji kunya in roƙi sarki yă haɗa mu da sojoji da masu dawakai don su yi mana rakiya su kāre mu daga magabta a kan hanya, gama mun ce wa sarki, “Alherin Allah yana tare da duk wanda yake dogara gare shi, amma kuma fushinsa yana kan duk wanda ya juya masa baya.”
23 Nous jeûnâmes donc, et nous implorâmes [le secours] de notre Dieu à cause de cela; et il fut fléchi par nos prières.
Saboda haka sai muka yi azumi, muka kai roƙonmu a wurin Allah, ya kuwa amsa mana.
24 Alors je séparai douze des principaux des Sacrificateurs; avec Sérébia, Hasabia, et avec eux dix de leurs frères.
Sai na keɓe manyan firistoci guda goma sha biyu tare da Sherebiya, Hashabiya da kuma’yan’uwansu guda goma.
25 Et je leur pesai l'argent et l'or et les ustensiles, qui étaient l'offrande que le Roi, ses conseillers, ses gentilshommes, et tous ceux d'Israël qui s'[y] étaient trouvés, avaient faite à la maison de notre Dieu.
Na auna musu zinariya da azurfa, da kwanoni waɗanda sarki da mashawartansa, da sauran abokan aikinsa, da Isra’ilawan da suke can suka bayar domin haikalin Allahnmu.
26 Je leur pesai donc, et je leur délivrai six cent cinquante talents d'argent, et des plats d'argent [pesant] cent talents, et cent talents d'or.
Na auna musu talenti 650 na azurfa, talenti ɗari na kwanonin azurfa, talenti 100 na zinariya,
27 Et vingt plats d'or [montant] à mille drachmes, et deux ustensiles de cuivre resplendissant et fin, aussi précieux que s'ils eussent été d'or.
kwanonin zinariya guda 20 da darajarsu ya kai darik 1,000, da kwanoni biyu na gogaggen tagulla, wanda yake darajarsa daidai da zinariya.
28 Et je leur dis: Vous êtes sanctifiés à l'Eternel; et les ustensiles sont sanctifiés; et cet argent et cet or est une offrande volontaire faite à l'Eternel le Dieu de vos pères.
Na ce masa, “Ku da kayan nan tsarkaka ne ga Ubangiji. Azurfa da zinariya ɗin, bayarwa ce ta yardar rai ga Ubangiji, Allah na kakanninku.
29 Ayez-y l'œil et gardez-les, jusqu'à ce que vous les pesiez en la présence des principaux des Sacrificateurs et des Lévites, et devant les principaux des pères d'Israël à Jérusalem, dans les chambres de la maison de l'Eternel.
Ku lura da su da kyau har sai kun isa Urushalima. Ku auna su a shirayin haikalin Ubangiji a Urushalima, a gaban manyan firistoci, da Lawiyawa, da shugabannin iyalai na Isra’ila.”
30 Les Sacrificateurs donc et les Lévites reçurent le poids de l'argent, et de l'or, et des ustensiles, pour les apporter à Jérusalem, dans la maison de notre Dieu.
Sa’an nan sai firistoci, da Lawiyawa suka karɓi azurfa da zinariya da kuma tsarkakan kwanonin da aka auna don a kai haikalin Allahnmu a Urushalima.
31 Et nous partîmes de la rivière d'Ahava le douzième jour du premier mois, pour aller à Jérusalem; et la main de notre Dieu fut sur nous; et il nous délivra de la main des ennemis, et de [leurs] embûches sur le chemin.
A rana ta goma sha biyu ga watan farko, muka tashi daga bakin rafin Ahawa don mu tafi Urushalima. Alherin Allahnmu yana tare da mu, ya kuma kāre mu daga magabta da’yan fashi.
32 Puis nous arrivâmes à Jérusalem, et nous étant reposés trois jours,
Muka iso Urushalima, inda muka huta kwana uku.
33 Au quatrième jour nous pesâmes l'argent et l'or, et les ustensiles dans la maison de notre Dieu, et nous les délivrâmes à Mérémoth, fils d'Urija Sacrificateur, avec lequel [était] Eléazar fils de Phinées; et avec eux Jozabad fils de Jésuah, et Nohadia, fils de Binuï, Lévites.
A rana ta huɗu muka tafi haikalin Allah, muka auna azurfa, da zinariya, da tsarkakan kwanonin, muka ba Meremot ɗan Uriya firist, da Eleyazar ɗan Finehas yana tare da shi, da kuma Lawiyawan nan, wato, Yozabad ɗan Yeshuwa, da Nowadiya ɗan Binnuyi.
34 Selon le nombre et le poids de toutes ces choses, et tout le poids en fut mis alors par écrit.
Aka yi lissafi aka auna kome aka tarar yana nan daidai, aka kuma rubuta yawan nauyin a lokacin.
35 Et ceux qui avaient été transportés, [et] qui étaient retournés de la captivité, offrirent pour tout Israël, en holocauste au Dieu d'Israël, douze veaux, quatre-vingt-seize béliers, soixante-dix-sept agneaux, [et] douze boucs pour le péché; le tout en holocauste à l'Eternel.
Sa’an nan sai waɗanda suka dawo daga bauta suka miƙa hadaya ta ƙonawa ga Allah na Isra’ila. Wato, bijimai guda goma sha biyu don Isra’ilawa duka, raguna tasa’in da shida,’yan raguna saba’in da bakwai, bunsurai kuma guda goma sha biyu. Aka miƙa su hadaya don zunubi. Wannan duka hadaya ta ƙonawa ce ga Ubangiji.
36 Et ils remirent les ordonnances du Roi entre les mains des Satrapes du Roi et des Gouverneurs qui étaient au deçà du fleuve, lesquels favorisèrent le peuple, et la maison de Dieu.
Suka kuma kai saƙon sarki zuwa ga wakilansa, da kuma gwamnoni na Kewayen Kogin Yuferites waɗanda suka taimaki mutane da kuma gidan Allah.

< Esdras 8 >