< Ézéchiel 47 >

1 Puis il me fit retourner vers l'entrée de la maison, et voici des eaux qui sortaient de dessous le seuil de la maison vers l'Orient, car le devant de la maison [était vers] l'Orient; et ces eaux-là descendaient de dessous, du côté droit de la maison de devers le côté Méridional de l'autel.
Mutumin ya komo da ni zuwa mashigin haikalin, sai na kuwa ga ruwa yana malalowa daga ƙarƙashin madogarar ƙofar haikalin wajen gabas (gama haikalin yana fuskantar gabas). Ruwan yana malalowa daga ƙarƙashin gefen kudun haikalin, kudu da bagaden.
2 Puis il me fit sortir par le chemin de la porte qui regardait vers le Septentrion, et me fit faire le tour par le chemin extérieur jusqu'à la porte extérieure, [même jusques] au chemin qui regardait l'Orient, et voici, les eaux coulaient du côté droit.
Sai ya fitar da ni ta ƙofar arewa ya kewaye da ni ta waje zuwa ƙofar da take waje mai fuskantar gabas, ruwan kuwa yana malalowa daga wajen kudu.
3 Quand cet homme commença de s'avancer vers l'Orient, il avait en sa main un cordeau, et il en mesura mille coudées; puis il me fit passer au travers de ces eaux-là, et elles me venaient jusqu'aux deux chevilles des pieds.
Yayinda mutumin ya yi wajen gabas da karan awo a hannunsa, sai ya auna kamu dubu ya kuma bi da ni ta ruwan da zurfinsa ya kama ni a idon ƙafa.
4 Puis il mesura mille [autres coudées]; et il me fit passer au travers de ces eaux-là, et elles me venaient jusqu'aux deux genoux; puis il mesura mille [autres coudées]; et il me fit passer au travers de ces eaux-là, et elles me venaient jusques aux reins.
Ya auna wani kamu dubu ya kuma bi da ni a ruwan da zurfinsa ya kai ni gwiwa. Ya sāke auna kamu dubu ya kuma bi da ni a ruwan da zurfinsa kama ni a gindi.
5 Puis il mesura mille [autres] coudées; mais ces eaux-là étaient déjà] un torrent, que je ne pouvais passer à gué; car ces eaux-là s'étaient enflées, c'étaient des eaux qu'il fallait passer à la nage, et un torrent que l'on ne pouvait passer à gué.
Ya auna wani kamu dubu, amma a yanzu ruwan ya zama kogin da ban iya hayewa ba, domin ruwan ya taso ya kuma yi zurfin da ya isa a yi iyo a ciki, kogin da ba za a iya hayewa ba.
6 Alors il me dit: fils d'homme, as-tu vu? puis il me fit aller plus outre, et me fit revenir vers le bord du torrent.
Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga wannan?” Sa’an nan ya komo da ni zuwa bakin kogin.
7 Quand j'y fus revenu, voilà un fort grand nombre d'arbres sur les deux bords du torrent.
Sa’ad da na iso can, sai na ga itatuwa masu yawa a kowane gefen kogin.
8 Puis il me dit: ces eaux-ci se vont rendre dans la Galilée Orientale, et elles descendront à la campagne, puis elles entreront dans la mer, et quand elles se seront rendues dans la mer, les eaux en deviendront saines.
Sai ya ce mini, “Wannan ruwa yana malalowa zuwa yankin gabas ya kuma gangaro zuwa cikin Araba, inda zai shiga Teku. Sa’ad da ya shiga cikin Tekun sai ruwan a can ya zama mai daɗi.
9 Et il arrivera que tout animal vivant, qui se traînera partout où entrera chacun des deux torrents, vivra, et il y aura une fort grande quantité de poissons. Lors donc que ces eaux seront entrées là, [les autres en] seront rendues saines, et tout vivra là où ce torrent sera entré.
Tarin halittu masu rai za su rayu a duk inda ruwan ya malalo. Za a kasance da kifi masu yawa, domin wannan ruwa yana malalowa a can yana kuma mai da ruwan gishiri yă zama ruwa mai daɗi; saboda haka duk inda ruwan ya malalo, kome zai rayu.
10 Pareillement il arrivera que les pêcheurs se tiendront le long de cette mer, depuis Henguédi jusques à Henhéglajim; [tellement que tout ce circuit] sera plein de filets tous étendus pour prendre du poisson, et le poisson qu'on y pêchera sera en fort grand nombre, chacun selon son espèce, comme le poisson qu'on pêche dans la grande mer.
Masunta za su tsaya a gaɓar; daga En Gedi zuwa En Eglayim, za a kasance da wuraren jefa abin kamun kifi. Za a sami kifayen iri-iri, kamar kifaye Bahar Rum.
11 Ses marais et ses fosses ont été assignées pour y faire le sel, à cause qu'elles ne seront point rendues saines.
Amma fadamun da tafkunan ba za su zama masu daɗi ba; za a bar su a gishirinsu.
12 Et auprès de ce torrent, [et] sur ses deux bords il croîtra des arbres fruitiers de toutes sortes, dont le feuillage ne flétrira point, et où l'on trouvera toujours du fruit; dans tous leurs mois ils produiront des fruits hâtifs, parce que les eaux de ce torrent sortent du Sanctuaire, et à cause de cela leur fruit sera bon à manger, et leur feuillage servira de remède.
’Ya’yan itatuwa na kowane iri za su yi girma a kowane gefen kogin. Ganyayensu ba su bushe ba, ba kuwa za su fasa yin’ya’ya ba. Kowane wata za su ba da’ya’ya domin ruwa daga wuri mai tsarki yana malalo musu.’Ya’yansu za su zama abinci, ganyayensu kuma za su zama magani.”
13 Ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: [ce sont] ici les frontières du pays dont vous vous rendrez possesseurs en titre d'héritage, selon les douze Tribus d'Israël; Joseph [en aura deux] portions.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Waɗannan su ne iyakokin da za ku raba ƙasar gādo cikin kabilan Isra’ila goma sha biyu, da rabo biyu don Yusuf.
14 Or vous l'hériterez l'un comme l'autre, le pays touchant lequel j'ai levé ma main de le donner à vos pères; et ce pays-là vous écherra en héritage.
Za ku raba ta daidai a cikinsu. Gama na ɗaga hannu na rantse zan ba da ita ga kakanninku, wannan ƙasa za tă zama gādonku.
15 C'est donc ici la frontière du pays, du côté du Septentrion, vers la grande mer, [savoir] ce qui est du chemin d'Héthlon, au quartier par où l'on vient à Tsédad.
“Wannan ce za tă zama iyakar ƙasa. “A wajen arewa za tă fara daga Bahar Rum ta hanyar Hetlon ta wuce Lebo Hamat zuwa Zedad,
16 [Où sont] Hamath, [la contrée tirant] vers Béroth, [et] Sibrajim, qui est entre la frontière de Damas, et entre la frontière de Hamath, [et] les bourgs d'entre-deux, qui sont vers la frontière de Havran.
Berota da Sibrayim (wadda take a iyaka tsakanin Damaskus da Hamat), har zuwa Hazer-Hattikon, wadda take a iyakar Hauran.
17 La frontière donc [prise] de la mer sera Hatsar-henan; la frontière de Damas, et le Septentrion qui regarde [proprement] vers le Septentrion, savoir, la frontière de Hamath, et le canton du Septentrion.
Iyakar za tă miƙe daga teku zuwa Hazar-Enon, ta iyakar Damaskus, da iyakar Hamat a arewa. Wannan ita ce iyakar a wajen arewa.
18 Mais vous mesurerez le côté de l'Orient depuis ce qui est entre Havran, Damas, Galaad, et le pays d'Israël qui est delà le Jourdain, et depuis la frontière qui est vers la mer Orientale; et [ainsi vous mesurerez] le canton qui regarde [proprement] vers l'Orient.
A wajen gabas iyakar za tă kama tsakanin Hauran da Damaskus, ta bi ta Urdun tsakanin Gileyad da ƙasar Isra’ila, zuwa tekun gabas har zuwa Tamar. Wannan ita ce iyakar a wajen gabas.
19 Puis [vous mesurerez] le côté du Midi [qui regarde proprement] vers le vent d'Autan, depuis Tamar jusques aux eaux des débats de Kadès, le long du torrent jusques à la grande mer; [ainsi vous mesurerez] le canton qui regarde [proprement] vers le vent d'Autan, tirant vers le Midi.
A wajen kudu za tă fara daga Tamar har zuwa ruwan Meriba Kadesh, sa’an nan ta bi Rafin Masar zuwa Bahar Rum. Wannan ita ce iyakar a wajen kudu.
20 Or le côté de l'Occident sera la grande mer, depuis la frontière du [Midi] jusques à l'endroit de l'entrée de Hamath, ce sera là le côté de l'Occident.
A wajen yamma, Bahar Rum ne zai zama iyakar zuwa wani wuri ɗaura da Lebo Hamat. Wannan ita ce iyakar a wajen yamma.
21 Après cela vous vous partagerez ce pays-là selon les Tribus d'Israël.
“Za ku rarraba wannan ƙasa a tsakaninku bisa ga kabilan Isra’ila.
22 A condition toutefois que vous ferez que ce pays-là écherra en héritage à vous et aux étrangers qui habitent parmi vous, lesquels auront engendré des enfants parmi vous, et ils vous seront comme celui qui est né au pays entre les enfants d'Israël, tellement qu'ils viendront avec vous en partage de l'héritage parmi les Tribus d'Israël.
Za ku raba ta kamar gādo wa kanku da kuma wa baƙin da suka zauna a cikinku waɗanda suke da’ya’ya. Za ku ɗauka su kamar’yan ƙasa haifaffun Isra’ilawa; za su yi gādo tare da ku a cikin kabilan Isra’ila.
23 Et il arrivera que vous assignerez à l'étranger son héritage dans la Tribu en laquelle il demeurera, dit le Seigneur l'Eternel.
A duk kabilar da baƙon yake zama, a can za ku ba shi gādonsa,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.

< Ézéchiel 47 >