< Ézéchiel 36 >

1 Et toi, fils d'homme, prophétise aussi touchant les montagnes d'Israël, et dis: montagnes d'Israël, écoutez la parole de l'Eternel.
“Ɗan mutum, ka yi annabci wa duwatsun Isra’ila ka ce, ‘Ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji.
2 Ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: parce que l'ennemi a dit contre vous: ha! ha! Tous les lieux haut élevés, qui même sont d'ancienneté, sont devenus notre possession.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa abokin gāba yana magana game da ku cewa, “Yauwa! Tsofaffin tuddai sun zama mallakarmu yanzu.”’
3 C'est pourquoi prophétise, et dis: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: parce, oui, parce qu'on vous a réduites en désolation, et que ceux d'alentour, vous ont englouties, afin que vous fussiez en possession au reste des nations, et qu'on vous a exposées à la langue et aux insultes des nations.
Saboda haka ka yi annabci ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin sun lalace ku suka kuma maishe ku kufai marar amfani a kowane gefe saboda ku zama mallakar sauran al’ummai da kuma abin magana da tsegumi ga mutane,
4 A cause de cela, montagnes d'Israël, écoutez la parole du Seigneur l'Eternel: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel aux montagnes, et aux coteaux, aux courants d'eaux, et aux vallées, aux lieux détruits et désolés, et aux villes abandonnées qui ont été en pillage et en moquerie au reste des nations qui sont tout à l'entour;
saboda haka, ya duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana faɗa wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, wa kufai da garuruwan da suka zama kango waɗanda aka washe aka wulaƙanta suka zama ganimar sauran al’ummai da suke kewaye da ku,
5 A cause de cela, [dis-je], ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: si je ne parle en l'ardeur de ma jalousie contre le reste des nations, et contre tous ceux d'Idumée qui se sont attribué ma terre en possession, avec une joie dont leur cœur était plein, et avec un mépris dont ils se faisaient un grand plaisir, pour la mettre au pillage.
ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa cikin kishina mai ƙuna na yi magana gāba da sauran al’ummai, da kuma gāba da Edom, gama da farin ciki da reni a zukatansu suka mai da ƙasata mallakarsu don su washe wuraren kiwonta.’
6 C'est pourquoi prophétise touchant la terre d'Israël, et dis aux montagnes, et aux coteaux, aux courants d'eaux, et aux vallées: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: voici, j'ai parlé en ma jalousie, et en ma fureur, parce que vous avez porté l'ignominie des nations.
Saboda haka ka yi annabci game da ƙasar Isra’ila ka kuma ce wa duwatsu da tuddai, wa kwazazzabai da kwaruruka, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ga shi, na yi magana da kishina da hasalata saboda sun sha zargi wurin al’ummai.
7 C'est pourquoi ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: j'ai levé ma main, si les nations qui sont tout autour de vous ne portent leur ignominie.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa na ɗaga hannuna sama na rantse cewa al’ummai da suke kewaye da ku za su sha ba’a.
8 Mais vous, montagnes d'Israël, vous pousserez vos branches, et vous porterez votre fruit pour mon peuple d'Israël; car ils sont prêts à venir.
“‘Amma ku, ya duwatsun Isra’ila, za ku miƙa rassanku ku ba da amfani ga mutanena Isra’ila, gama ba da daɗewa ba za su komo gida.
9 Car me voici, [je viens] à vous, et je retournerai vers vous, et vous serez labourées, et semées.
Na damu da ku kuma zan dube ku da tausayi; za ku nome ku kuma shuka,
10 Et je multiplierai les hommes sur vous, [savoir] la maison d'Israël tout entière, et les villes seront habitées, et les lieux déserts seront rebâtis.
zan kuma riɓaɓɓanya mutane a kanku, dukan gidan Isra’ila ke nan. Za a zauna a birane a kuma sāke gina rusassun wurare.
11 Et je multiplierai sur vous les hommes et les bêtes, qui y multiplieront, et fructifieront; je ferai que vous serez habités comme anciennement, et je vous ferai plus de bien que vous n'en avez eu au commencement; et vous saurez que je suis l'Eternel.
Zan sa mutane da dabbobi su yi yawa a kanku, za su kuma ba da’ya’ya su kuma yi yawa. Zan zaunar da mutane a kanku kamar dā zan kuma sa ku wadaita fiye da dā. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
12 Et je ferai marcher sur vous des hommes, [savoir] mon peuple d'Israël, qui vous posséderont, vous leur serez en héritage, et vous ne les consumerez plus.
Zan sa mutanena Isra’ila su yi tafiya a kanku. Za su mallake ku, za ku kuma zama gādonsu; ba za ku ƙara sa su rasa’ya’yansu ba.
13 Ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: parce qu'on dit de vous: tu es un pays qui dévore les hommes, et tu as consumé tes habitants;
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa domin mutane suna magana game da ku cewa, “Kun cinye mutane kuka kuma sa al’ummarku ta rasa’ya’yanta,”
14 A cause de cela tu ne dévoreras plus les hommes, et ne consumeras plus tes habitants, dit le Seigneur l'Eternel.
saboda haka ba za ku ƙara cinye mutane ko ku sa al’ummarku ta rasa’ya’ya ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
15 Et je ferai que tu n'entendras plus l'ignominie des nations, et que tu ne porteras plus l'opprobre des peuples; et tu ne feras plus périr tes habitants, dit le Seigneur l'Eternel.
Ba zan ƙara bari ku ji maganar banza ta al’ummai ba, ba kuwa za ku ƙara shan ba’ar mutane ko in sa al’ummarku ta fāɗi ba, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”
16 Puis la parole de l'Eternel me fut [adressée], en disant:
Maganar Ubangiji ta sāke zuwa mini cewa,
17 Fils d'homme, ceux de la maison d'Israël habitant en leur terre l'ont souillée par leur voie et par leurs actions; leur voie est devenue devant moi telle qu'est la souillure de la femme séparée à cause de son impureté;
“Ɗan mutum, sa’ad da mutanen Isra’ila suke zama a ƙasarsu, sun ƙazantar da ita ta wurin halinsu da kuma ayyukansu. Halinsu ya yi kamar rashin tsarkin mace a lokacin al’adarta a gabana.
18 Et j'ai répandu ma fureur sur eux à cause du sang qu'ils ont répandu sur le pays, et parce qu'ils l'ont souillé par leurs idoles.
Saboda haka na husata da su domin sun yi kisankai a ƙasar kuma domin sun ƙazantar da ita da gumakansu.
19 Et je les ai dispersés parmi les nations, et ils ont été répandus par les pays; je les ai jugés selon leur voie, et selon leurs actions.
Na warwatsa su cikin al’ummai, suka kuwa warwatsu cikin dukan ƙasashe; na hukunta su gwargwadon halinsu da ayyukansu.
20 Et étant venus parmi les nations au milieu desquelles ils sont venus, ils ont profané le Nom de ma Sainteté, en ce qu'on a dit d'eux: ceux-ci sont le peuple de l'Eternel, et cependant ils sont sortis de son pays.
Kuma ko’ina da suka tafi a cikin al’ummai sun ɓata sunana mai tsarki, gama an yi magana a kansu cewa, ‘Waɗannan mutanen Ubangiji ne, duk da haka dole su bar ƙasarsa.’
21 Mais j'ai épargné le Nom de ma Sainteté, lequel la maison d'Israël avait profané parmi les nations au milieu desquelles ils étaient venus.
Na damu saboda sunana mai tsarki, wanda gidan Isra’ila ya ɓata a cikin al’ummai inda suka tafi.
22 C'est pourquoi dis à la maison d'Israël: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: je ne [le] fais point à cause de vous, ô maison d'Israël! mais à cause du Nom de ma Sainteté, que vous avez profané parmi les nations au milieu desquelles vous êtes venus.
“Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba dominku ba ne, ya gidan Isra’ila da nake yin waɗannan abubuwa, amma saboda sunana ne mai tsarki, wanda kuka ɓata a cikin al’ummai inda kuka tafi.
23 Et je sanctifierai mon grand Nom, qui a été profané parmi les nations, et que vous avez profané parmi elles; et les nations sauront que je suis l'Eternel, dit le Seigneur l'Eternel, quand je serai sanctifié en vous, en leur présence.
Zan nuna tsarkin girman sunana, wanda aka ɓata a cikin al’umma, sunana da kuka ɓata a cikinsu. Sa’an nan al’ummai za su san cewa ni ne Ubangiji, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinku a idanunsu.
24 Je vous retirerai donc d'entre les nations, je vous rassemblerai de tous pays, et je vous ramènerai en votre terre.
“‘Gama zan fitar da ku daga al’ummai; zan tattara ku daga dukan ƙasashe in komo da ku zuwa ƙasarku.
25 Et je répandrai sur vous des eaux nettes, et vous serez nettoyés; je vous nettoierai de toutes vos souillures, et de toutes vos idoles.
Zan yayyafa muku ruwa mai tsabta, zan kuwa tsarkake ku daga dukan ƙazantarku daga kuma dukan gumakanku.
26 Je vous donnerai un nouveau cœur, je mettrai au dedans de vous un Esprit nouveau; j'ôterai de votre chair le cœur de pierre, et je vous donnerai un cœur de chair.
Zan ba ku sabuwa zuciya in kuma sa sabon ruhu a cikinku; zan fid da zuciyar dutse in kuma ba ku zuciyar nama.
27 Et je mettrai mon Esprit au dedans de vous, je ferai que vous marcherez dans mes statuts, et que vous garderez mes ordonnances, et les ferez.
Zan kuma sa Ruhuna a cikinku in kuma motsa ku ku bi ƙa’idodina ku kuma kiyaye dokokina.
28 Et vous demeurerez au pays que j'ai donné à vos pères, et vous serez mon peuple, et je serai votre Dieu.
Za ku zauna a ƙasar da na ba wa kakanninku; za ku zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnku.
29 Je vous délivrerai de toutes vos souillures, j'appellerai le froment, je le multiplierai, et je ne vous enverrai plus la famine;
Zan cece ku daga dukan rashin tsabtarku. Zan sa hatsi ya yi yalwa ba zan kawo yunwa a kanku ba.
30 Mais je multiplierai le fruit des arbres, et le revenu des champs, afin que vous ne portiez plus l'opprobre de la famine entre les nations.
Zan ƙara’ya’yan itatuwa da amfanin gona, saboda kada ku ƙara shan kunya a cikin al’ummai saboda yunwa.
31 Et vous vous souviendrez de votre mauvaise voie et de vos actions, qui n'étaient pas bonnes, et vous détesterez en vous-mêmes vos iniquités, et vos abominations.
Sa’an nan za ku tuna mugayen hanyoyinku da mugayen ayyukanku, za ku kuwa ji ƙyamar kanku saboda zunubanku da kuma ayyukanku na banƙyama.
32 Je ne le fais point pour l'amour de vous, dit le Seigneur l'Eternel, afin que vous le sachiez. Soyez honteux et confus à cause de votre voie, ô maison d'Israël!
Ina so ku san cewa ba na yi wannan saboda ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ku ji kunya ku kuma giggita saboda halinku, ya gidan Isra’ila!
33 Ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: au jour que je vous aurai purifiés de toutes vos iniquités je vous ferai habiter dans des villes, et les lieux déserts seront rebâtis.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar da na tsarkake ku daga dukan zunubanku, zan sāke zaunar da ku a garuruwanku, a kuma sāke gina kufai.
34 Et la terre désolée sera labourée, au lieu qu'elle n'a été que désolation, en la présence de tous les passants.
Ƙasar da take kango a dā za ku nome ta a maimakon zama kango a idon dukan masu ratsawa a cikinta.
35 Et on dira: cette terre-ci qui était désolée, est devenue comme le jardin d'Héden; et ces villes qui avaient été désertes, désolées, et détruites, sont fortifiées et habitées.
Za su ce, “Wannan ƙasar da take kango a dā ta zama kamar lambu Eden; biranen da dā suke kufai, kango da kuma aka lalata, yanzu suna da katanga ana kuma zama a ciki.”
36 Et les nations qui seront demeurées de reste autour de vous sauront que moi l'Eternel j'aurai rebâti les lieux détruits, et planté le pays désolé, moi l'Eternel j'ai parlé, et je le ferai.
Sa’an nan al’ummai kewaye da ku da suka rage za su san cewa Ni Ubangiji na sāke gina abin da aka lalace na kuma sāke shuka abin da yake kango. Ni Ubangiji na faɗa, kuma zan aikata.’
37 Ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: encore serai-je recherché par la maison d'Israël, pour leur faire ceci, [savoir] que je multiplie leurs hommes comme un troupeau de brebis.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa har yanzu zan ji roƙon gidan Isra’ila in kuma yi musu wannan. Zan sa mutanensu su yi yawa kamar tumaki,
38 Les villes qui sont désertes seront remplies de troupes d'hommes, tels que sont les troupeaux des bêtes sanctifiées, tels que sont les troupeaux des bêtes qu'on amène à Jérusalem en ses fêtes solennelles; et ils sauront que je suis l'Eternel.
yawansu ya yi kamar garken tumaki don hadaya a Urushalima a ƙayyadaddun lokuta bukukkuwarta. Haka biranen da suke kufai za su cika da ɗumbun mutane. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.”

< Ézéchiel 36 >