< Esther 9 >

1 Le douzième mois donc, qui est le mois d'Adar, le treizième jour de ce mois, auquel la parole du Roi et son ordonnance devait être exécutée, au jour que les ennemis des Juifs espéraient en être les maîtres, au lieu que le contraire devait arriver, [savoir] que les Juifs seraient maîtres de ceux qui les haïssaient;
A rana ta goma sha uku na watan goma sha biyu, wato, watan Adar ne za a aiwatar da dokar da sarki ya umarta. A wannan rana, abokan gāban Yahudawa suka sa zuciya za su sha ƙarfinsu, amma yanzu Zerzes ya canja, Yahudawa kuma suka yi galiba a bisa waɗanda suka ƙi jininsu.
2 Les Juifs s'assemblèrent dans leurs villes, par toutes les provinces du Roi Assuérus, pour mettre la main sur ceux qui cherchaient leur perte; mais nul ne put tenir ferme devant eux, parce que la frayeur qu'on avait d'eux avait saisi tous les peuples.
Yahudawa suka tattaru a cikin biranensu a dukan lardunan Sarki Zerzes don su kai wa waɗanda suka nemi a hallaka su hari. Babu wanda ya tasar musu domin mutanen dukan sauran al’ummai sun jin tsoronsu.
3 Et tous les principaux des provinces, et les Satrapes, et les Gouverneurs, et ceux qui maniaient les affaires du Roi, soutenaient les Juifs, parce que la frayeur qu'on avait de Mardochée les avait saisis.
Dukan sarakuna larduna, da hakimai, da gwamnoni da kuma ma’aikatan sarki suka taimaki Yahudawa, domin tsoron Mordekai ya kama su.
4 Car Mardochée était grand dans la maison du Roi, et sa réputation allait par toutes les provinces; parce que cet homme Mardochée allait en croissant.
Mordekai babban mutum ne a fada, sunansa ya kai ko’ina a lardunan, ikonsa ya yi ta ƙasaita gaba-gaba.
5 Les Juifs donc frappèrent tous leurs ennemis à coups d'épée, et en firent un grand carnage, de sorte qu'ils traitèrent selon leurs désirs ceux qui les haïssaient,
Yahudawa suka karkashe dukan abokan gābansu da takobi, suka karkashe waɗanda suka ƙi jininsu, suka kuma hallaka su yadda suka ga dama.
6 Et même dans Susan, la ville capitale, les Juifs tuèrent et firent périr cinq cents hommes.
A mazaunin masarautar a Shusha, Yahudawa suka karkashe, suka kuma hallaka mutum ɗari biyar.
7 Ils tuèrent aussi Parsandata, Dalphon, Aspatha,
Suka kuma kashe Farshandata, da Dalfon, da Asfata,
8 Poratha, Adalia, Aridatha.
da Forata, da Adaliya, da Aridata,
9 Parmastha, Arisaï, Aridaï, et Vajezatha;
da Farmashta, da Arisai, da Aridai da kuma Baizata,
10 Dix fils d'Haman fils d'Hammédatha, l'oppresseur des Juifs; mais ils ne mirent point leurs mains au pillage.
’ya’ya maza goma na Haman ɗan Hammedata, abokin gāban Yahudawa. Amma ba su taɓa dukiyarsu ba.
11 Et ce jour-là on rapporta au Roi le nombre de ceux qui avaient été tués dans Susan, la ville capitale.
A wannan rana, aka ba wa sarki rahoton yawan mutanen da aka kashe a mazaunin masarauta, a Shusha.
12 Et le Roi dit à la Reine Esther: Dans Susan la ville capitale, les Juifs ont tué et détruit cinq cents hommes, et les dix fils d'Haman, qu'auront-ils fait au reste des provinces du Roi? Toutefois quelle [est] ta demande? et elle te sera octroyée; et quelle est encore ta prière? et cela sera fait.
Sarki ya ce wa Sarauniya Esta, “Yahudawa sun karkashe, suka kuma hallaka mutum ɗari biyar, da kuma’ya’ya maza goma na Haman a mazaunin masarauta a Shusha. Me suka yi a sauran lardunan sarki? Yanzu kuma mene ne roƙonki? Za a ba ki. Mece ce bukatarki? Za a biya miki.”
13 Et Esther répondit: Si le Roi le trouve bon qu'il soit permis encore demain aux Juifs, qui sont à Susan, de faire selon ce qu'il avait été ordonné de faire aujourd'hui, et qu'on pende au gibet les dix fils d'Haman.
Esta ta ce, “In sarki ya yarda, yă ba wa Yahudawa da suke Shusha izini su aikata dokan nan gobe kuma, bari kuma a rataye’ya’ya maza goma na Haman a kan gumagumai.”
14 Et le Roi commanda que cela fût ainsi fait; de sorte que l'ordonnance fut publiée dans Susan, et on pendit les dix fils d'Haman.
Sai sarki ya ba da umarni a yi haka ɗin. Aka ba da doka a Shusha, aka kuma rataye’ya’ya maza goma na Haman.
15 Les Juifs donc qui étaient dans Susan, s'assemblèrent encore le quatorzième jour du mois d'Adar, et tuèrent dans Susan trois cents hommes; mais ils ne mirent point leurs mains au pillage.
Yahudawan da suke Shusha suka taru a ran goma sha huɗu na watan Adar suka kuma karkashe mutum ɗari uku a Shusha, amma ba su taɓa dukiyarsu ba.
16 Et le reste des Juifs qui étaient dans les provinces du Roi, s'assemblèrent, et se mirent en défense pour leur vie, et ils eurent du repos de leurs ennemis, et tuèrent soixante et quinze mille hommes de ceux qui les haïssaient; mais ils ne mirent point leurs mains au pillage.
Ana cikin haka, sai saura Yahudawa waɗanda suke lardunan sarki su ma suka taru domin su kāre kansu su kuma sami hutu daga abokan gābansu. Suka karkashe mutum dubu saba’in da biyar amma ba su taɓa dukiyarsu ba.
17 [Cela se fit] le treizième jour du mois d'Adar, mais le quatorzième du même [mois] ils se reposèrent, et ils le célébrèrent comme un jour de festin et de joie.
Wannan ya faru a ran goma sha uku na watan Adar. A rana ta goma sha huɗu kuwa suka huta, suka kuma mai da ita ranar biki da kuma ta farin ciki.
18 Et les Juifs qui étaient dans Susan, s'assemblèrent le treizième et le quatorzième jour du même mois, mais ils se reposèrent le quinzième, et le célébrèrent comme un jour de festin et de joie.
Amma Yahudawan da suke a Shusha suka taru a rana ta goma sha uku da ta sha huɗu, sa’an nan a rana ta goma sha biyar suka huta, suka kuma mai da ita ranar biki da ta farin ciki.
19 C'est pourquoi les Juifs des bourgs, qui habitent dans des villes non murées, emploient le quatorzième jour du mois d'Adar, en réjouissance, en festins, en jour de fête, et à envoyer des présents l'un à l'autre.
Shi ya sa Yahudawan ƙauyuka, waɗanda suke zama a karkara, suke kiyaye rana ta goma sha huɗu ta watan Adar a matsayin ranar farin ciki da ta biki, ranar ba da kyautai ga juna.
20 Car Mardochée écrivit ces choses, et en envoya les Lettres à tous les Juifs qui étaient dans toutes les provinces du Roi Assuérus, tant près que loin;
Sai Mordekai ya rubuta waɗannan abubuwa, ya kuma aika wasiƙu ga dukan Yahudawa ko’ina a lardunan Sarki Zerzes, na kusa da na nesa.
21 Leur ordonnant qu'ils célébrassent le quatorzième jour du mois d'Adar, et le quinzième jour du même [mois] chaque année.
Ya sa su yi bikin kowace shekara a ranaku goma sha huɗu da goma sha biyar na watan Adar
22 Selon les jours auxquels les Juifs avaient eu du repos de leurs ennemis, et selon le mois où leur angoisse fut changée en joie, et leur deuil en jour de fête, afin qu'ils les célébrassent comme des jours de festin et de joie, et en envoyant des présents l'un à l'autre, et des dons aux pauvres.
a matsayin lokacin da Yahudawa suka sami huta daga abokan gābansu, da kuma a matsayin watan da aka mai da baƙin cikinsu ya zama farin ciki, makokinsu kuma ya zama ranar biki. Ya rubuta musu su kiyaye ranakun a matsayin ranakun biki da na farin ciki. Su kuma ba da kyautai na abinci ga juna, da kuma kyautai ga matalauta.
23 Et chacun des Juifs se soumit à faire ce qu'on avait commencé, et ce que Mardochée leur avait écrit.
Ta haka, Yahudawa suka yarda su ci gaba da bikin da suka fara, suna aikata abin da Mordekai ya rubuta musu.
24 Parce qu'Haman fils d'Hammédatha Agagien, l'oppresseur de tous les Juifs, avait machiné contre les Juifs de les détruire, et qu'il avait jeté Pur, c'est-à-dire le sort, pour les défaire, et pour les détruire.
Haman ɗan Hammedata, mutumin Agag, abokin gāban dukan Yahudawa, ya ƙulla maƙarƙashiya game da Yahudawa, domin a hallaka su, ya kuma jefa fur (wato, ƙuri’a) don yă hallaka su.
25 Mais quand Esther fut venue devant le Roi, il commanda par Lettres que la méchante machination qu'[Haman] avait faite contre les Juifs, retombât sur sa tête, et qu'on le pendît, lui et ses fils, au gibet.
Amma sa’ad da sarki ya sami labarin maƙarƙashiyar, sai ya ba da umarnai a rubuce cewa mugun shirin da Haman ya ƙulla a kan Yahudawa yă komo kansa, kuma cewa a rataye shi da’ya’yansa maza a kan gumagumai.
26 C'est pourquoi on appelle ces jours-là Purim, du nom de Pur. Et suivant toutes les paroles de cette dépêche, et selon ce qu ils avaient vu sur cela, et ce qui leur était arrivé,
(Saboda haka, aka kira ranakun nan Furim, daga kalma fur). Saboda dukan abin da aka rubuta cikin wannan wasiƙa da kuma abin da suka gani, da abin da ya same su.
27 Les Juifs établirent et se soumirent, eux et leur postérité, et tous ceux qui se joindraient à eux, à ne manquer point de célébrer selon ce qui en avait été écrit, ces deux jours dans leur saison chaque année.
Yahudawa suka ɗauki nawayar kafa al’adar cewa su, da zuriyarsu, da dukan waɗanda suka haɗa hannun da su, za su kiyaye waɗannan kwanaki biyu, kowace shekara yadda aka tsara, a kuma lokacin da aka keɓe dominsu.
28 Et [ils ordonnèrent] que la mémoire de ces jours serait célébrée et solennisée dans chaque âge, dans chaque famille, dans chaque province et dans chaque ville; et qu'on n'abolirait point ces jours de Purim entre les Juifs, et que la mémoire de ces jours-là ne s'effacerait point en leur postérité.
Za a tuna, a kuma kiyaye waɗannan kwanaki a kowane zamani, cikin kowane iyali, da kuma cikin kowane lardi, da kowace birni. Kuma kada Yahudawa su fasa yin bikin waɗannan kwanakin Furim, ko su bar jikokinsu su manta da kiyaye waɗannan ranaku biyu.
29 La Reine Esther aussi, fille d'Abihaïl, avec Mardochée Juif écrivit tout ce qui était requis pour autoriser cette patente de Purim, pour la seconde fois.
Saboda haka Sarauniya Esta,’yar Abihayil, tare da Mordekai mutumin Yahuda, suka rubuta da cikakken iko, suka tabbatar da wannan wasiƙa ta biyu game da Furim.
30 Et on envoya des Lettres à tous les Juifs, dans les cent vingt-sept provinces du Royaume d'Assuérus, avec des paroles de paix et de vérité;
Mordekai kuwa ya aika da wasiƙu zuwa ga dukan Yahudawa cikin larduna 127 na masarautar Zerzes. Saƙon fatan alheri da na tabbaci,
31 Pour établir ces jours de Purim dans leur saison, comme Mardochée Juif, et la Reine Esther l'avaient établi; et comme ils les avaient établis pour eux-mêmes, et pour leur postérité, pour être des monuments de [leurs] jeûnes, et de leur cri.
don a kafa waɗannan ranakun Furim a keɓaɓɓen lokacinsu, kamar yadda Mordekai mutumin Yahuda da Sarauniya Esta suka dokace su. Yadda kuma suka kafa wa kansu da zuriyarsu, game da lokutansu na azumi da makoki.
32 Ainsi l'édit d'Esther autorisa cet arrêt-là de Purim; comme il est écrit dans ce Livre.
Dokar Esta ta tabbatar da waɗannan umarnai game da Furim, aka kuma rubuta ta cikin tarihi.

< Esther 9 >