< Daniel 6 >

1 Or il plut à Darius d'établir sur le Royaume six-vingts Satrapes pour être sur tout le Royaume.
Ya gamshi Dariyus ya naɗa muƙaddasai 120 su yi shugabanci a duk fāɗin masarautar,
2 Et au-dessus d'eux trois Gouverneurs, dont Daniel était l'un, auxquels ces Satrapes devaient rendre compte, afin que le Roi ne souffrît aucun préjudice.
ya naɗa mutum uku a bisa waɗannan muƙaddasan, Daniyel yana ɗaya daga cikin mutum ukun nan. Sai aka sa muƙaddasan nan a ƙarƙashin waɗannan uku ɗin domin kada sarki ya yi hasarar kome.
3 Mais Daniel excellait par-dessus les autres Gouverneurs et Satrapes, parce qu'il avait plus d'esprit qu'eux; et le Roi pensait à l'établir sur tout le Royaume.
To, Daniyel dai ya yi ficce a cikin shugabannin nan uku har da muƙaddasan ma, saboda waɗansu halaye nagari da yake da su, wanda ya sa sarki ya yi shiri ya ɗora shi a kan dukan mulkinsa.
4 Alors les Gouverneurs et les Satrapes cherchaient à trouver quelque occasion d'accuser Daniel touchant les affaires du Royaume; mais ils ne pouvaient trouver en lui aucune occasion ni aucun vice, parce qu'il était fidèle, et qu'il ne se trouvait en lui ni faute, ni vice.
A kan haka, shugabannin nan uku da muƙaddasan nan suka yi ƙoƙari su sami wani laifi a kan Daniyel a yadda yake tafiyar da aikin shugabancinsa, amma ba su samu ba. Ba su same shi da wani laifin cin hanci ba, domin shi amintacce ne kuma babu wani aibi a kansa ko rashin kula.
5 Ces hommes donc dirent: Nous ne trouverons point d'occasion d'accuser ce Daniel, si nous ne la trouvons dans ce qui regarde la Loi de son Dieu.
A ƙarshe waɗannan mutane suka ce; “Ba za mu taɓa samun wani laifin da za mu kama Daniyel da shi ba, sai dai ko abin ya shafi dokar Allahnsa.”
6 Alors ces Gouverneurs et ces Satrapes s'assemblèrent vers le Roi, et lui parlèrent ainsi: Roi Darius, vis éternellement!
Saboda haka shugabannin nan suka haɗu da muƙaddasan nan suka tafi wurin sarki a ƙungiyance suka ce, “Ya Sarki Dariyus, ranka yă daɗe!
7 Tous les Gouverneurs de ton Royaume, les Lieutenants, les Satrapes, les Conseillers, et les Capitaines sont d'avis d'établir une ordonnance royale, et de faire un décret ferme, que quiconque fera aucune requête à quelque Dieu, ou à quelque homme que ce soit, d'ici à trente jours, sinon à toi, ô Roi! qu'il soit jeté dans la fosse des lions.
Shugabannin masarauta, da masu mulki, da muƙaddasai, da mashawarta da gwamnoni duk sun amince cewa sarki yă kafa doka yă kuma yi umarni cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda ya yi addu’a ga wani allah ko mutum, in ba a gare ka ba, ya sarki, jefa shi cikin kogon zakoki.
8 Maintenant donc, ô Roi! établis ce décret, et fais en écrire des Lettres afin qu'on ne le change point, selon que la Loi des Mèdes et des Perses est irrévocable.
Yanzu, ya sarki, sai ka yi umarni ka kuma yi shi a rubuce saboda kada a canja shi, bisa ga dokar Medes da Farisa, waɗanda ba a iya sokewa.”
9 C'est pourquoi le Roi Darius écrivit la lettre et le décret.
Sai Sarki Dariyus ya ba da umarnin a rubuce.
10 Or quand Daniel eut appris que les Lettres en étaient écrites, il entra dans sa maison, et les fenêtres de sa chambre étant ouvertes du côté de Jérusalem, il se mettait trois fois le jour à genoux, et il priait et célébrait son Dieu, comme il avait fait auparavant.
To, da Daniyel ya ji labarin cewa an fitar da doka, sai ya tafi gidansa a ɗakinsa na sama inda tagogin ɗakin suke duban wajen Urushalima. Sau uku yakan durƙusa yă yi addu’a yana yin godiya ga Allahnsa, kamar yadda ya saba yi.
11 Alors ces hommes s'assemblèrent, et trouvèrent Daniel priant, et faisant requête à son Dieu.
Sai waɗannan mutane suka tafi a ƙungiyance suka kuma iske Daniyel yana addu’a yana roƙon Allah yă taimake shi.
12 Ils s'approchèrent et dirent au Roi touchant le décret royal: N'as-tu pas écrit ce décret, que tout homme qui ferait requête à quelque Dieu, ou à quelque homme que ce fût, d'ici à trente jours, sinon à toi, ô Roi! serait jeté dans la fosse des lions? [Et] le Roi répondit, et dit: La chose est constante, selon la Loi des Mèdes et des Perses, laquelle est irrévocable.
Sai suka tafi wurin sarki suka yi masa magana game da dokar mulkinsa, suka ce, “Ashe, ba ka yi doka cewa a cikin kwana talatin nan gaba duk wanda aka tarar yana addu’a ga wani allah ko mutum in ba kai ba, ya sarki, za ka jefa shi a cikin ramin zakoki ba?” Sarki ya amsa ya ce, “Dokar tana nan daram bisa ga dokar Medes da Farisa, waɗanda ba a iya sokewa.”
13 Alors ils répondirent, et dirent au Roi: Daniel, qui est un de ceux qui ont été emmenés captifs de Juda, n'a tenu compte de toi, ô Roi! ni du décret que tu as écrit; mais il prie, faisant requête trois fois le jour.
Sai suka ce wa sarki, “Daniyel ɗin nan, wanda yake ɗaya daga cikin waɗanda aka kwaso daga Yahuda, bai kula da kai ba, ya sarki, balle fa dokar da ka yi. Har yanzu yana addu’a sau uku a rana.”
14 Ce que le Roi ayant entendu, il en eut en lui-même un grand déplaisir, et il prit à cœur Daniel pour le délivrer, et s'appliqua fortement jusqu'au soleil couchant à le délivrer.
Da sarki ya ji haka, sai ya damu sosai, ya ƙudura yă ceci Daniyel, ya yi ta fama har fāɗuwar rana yadda zai yi yă kuɓutar da shi.
15 Mais ces hommes-là s'assemblèrent vers le Roi, et lui dirent: Ô Roi! sache que la Loi des Mèdes et des Perses est, que tout décret et toute ordonnance que le Roi aura établie, ne se doit point changer.
Sai mutanen nan suka je wurin sarki a ƙungiyance suka ce masa, “Ka tuna, ya sarki; cewa bisa ga dokar Medes da Farisa, babu umarni ko dokar da sarki ya yi da za a iya sokewa.”
16 Alors le Roi commanda qu'on amenât Daniel, et qu'on le jetât dans la fosse des lions. Et le Roi prenant la parole dit à Daniel: Ton Dieu, lequel tu sers incessamment, sera celui qui te délivrera.
Saboda haka sai sarki ya ba da umarni suka kuma kawo Daniyel suka jefa shi cikin ramin zakoki. Sarki ya ce wa Daniyel, “Bari Allahn nan wanda kake bauta masa kullum, yă cece ka!”
17 Et on apporta une pierre, qui fut mise sur l'ouverture de la fosse, et le Roi la scella de son anneau, et de l'anneau de ses gentilshommes, afin que rien ne fût changé touchant Daniel.
Aka kawo dutsen aka rufe bakin ramin, sa’an nan sarki ya hatimce shi da zobensa da kuma zoban manyan mutanensa, don kada wani yă canja yanayin Daniyel.
18 Après quoi le Roi s'en alla dans son palais, et passa la nuit sans souper, et on ne lui fit point venir les instruments de musique, il ne put même point dormir.
Sa’an nan sarki ya koma fadarsa ya kwana bai ci ba, kuma babu wata liyafar da aka kawo masa. Ya kuma kāsa barci.
19 Puis le Roi se leva de grand matin, lorsque le jour commençait à luire, et s'en alla en diligence vers la fosse des lions.
Gari yana wayewa, sai sarki ya tashi ya hanzarta zuwa ramin zakoki.
20 Et comme il approchait de la fosse, il cria d'une voix triste: Daniel, [et] le Roi prenant la parole dit à Daniel: Daniel, serviteur du Dieu vivant, ton Dieu, lequel tu sers incessamment, aurait-il bien pu te délivrer des lions?
Da ya yi kusa da ramin zakokin, sai ya kira Daniyel da muryar mai cike da damuwa ya ce, “Daniyel bawan Allah mai rai, ko Allahn nan naka wanda kake bauta wa kullum, ya iya cetonka daga zakoki?”
21 Alors Daniel dit au Roi: Ô Roi, vis éternellement.
Sai Daniyel ya amsa ya ce, “Ran sarki, yă daɗe!
22 Mon Dieu a envoyé son Ange, et a fermé la gueule des lions, tellement qu'ils ne m'ont fait aucun mal, parce que j'ai été trouvé innocent devant lui; et même à ton égard, ô Roi! je n'ai commis aucune faute.
Allahna ya aiko da mala’ikansa, ya kuwa rufe bakunan zakoki. Ba su yi mini rauni ba, gama an same ni marar laifi ne a gabansa. Ban kuwa taɓa yin wani abu marar kyau a gabanka ba, ya sarki.”
23 Alors le Roi eut en lui-même une grande joie, et il commanda qu'on tirât Daniel hors de la fosse. Ainsi Daniel fut tiré hors de la fosse, et on ne trouva en lui aucune blessure, parce qu'il avait cru en son Dieu.
Sai sarki ya cika da murna ƙwarai, ya kuma yi umarni a ciro Daniyel daga ramin zakoki. Kuma da aka fito da Daniyel daga ramin, ba a sami wani rauni a jikinsa ba, domin ya dogara ga Allahnsa.
24 Et par le commandement du Roi, ces hommes qui avaient accusé Daniel, furent amenés, et jetés, eux, leurs enfants, et leurs femmes, dans la fosse des lions, et avant qu'ils fussent parvenus au bas de la fosse, les lions se saisirent d'eux, et leur brisèrent tous les os.
Sai sarki ya umarta, a kawo mutanen nan da suka yi wa Daniyel maƙarƙashiya, a tura su, da’ya’yansu, da matansu cikin ramin zakoki. Kafin ma su kai ƙurewar ramin, sai zakoki suka hallaka su suka yayyage su, suka yi kaca-kaca da su.
25 Alors le Roi Darius écrivit [des Lettres de telle teneur]: A tous peuples, nations et Langues, qui habitent en toute la terre; que votre paix soit multipliée!
Sa’an nan Sarki Dariyus ya rubuta wa dukan mutane, da al’ummai da kuma mutanen dukan harsunan a duk fāɗin ƙasar. “Bari yă yi nasara sosai!
26 De par moi est fait un Edit, que dans toute l'étendue de mon Royaume on ait de la crainte et de la frayeur pour le Dieu de Daniel, car c'est le Dieu vivant, et permanent à toujours; et son Royaume ne sera point dissipé, et sa domination sera jusqu'à la fin.
“Na fitar da doka cewa a cikin dukan iyakar ƙasar mulkina, dole mutane su ji tsoro su kuma girmama Allah na Daniyel.
27 Il sauve et délivre, il fait des prodiges et des merveilles dans les cieux et sur la terre, et il a délivré Daniel de la puissance des lions.
Yakan kuɓutar ya kuma ceci;
28 Ainsi Daniel prospéra au temps du règne de Darius, et au temps du règne de Cyrus de Perse.
Daniyel kuwa ya bunkasa a lokacin mulkin Dariyus da kuma mulkin Sairus na Farisa.

< Daniel 6 >