< 2 Samuel 2 >

1 Or il arriva après cela que David consulta l'Eternel, en disant: Monterai-je en quelqu'une des villes de Juda? Et l'Eternel lui répondit: Monte. Et David dit: En laquelle monterai-je? Il répondit: A Hébron.
Bayan’yan kwanaki, sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji ya ce, “In haura zuwa ɗaya daga cikin biranen Yahuda?” Ubangiji ya ce, “Haura.” Dawuda ya ce, “Wanne zan tafi?” Ubangiji ya ce, “Je Hebron.”
2 David donc monta là avec ses deux femmes, Ahinoham qui était de Jizréhel, et Abigal, [qui avait été] femme de Nabal, lequel était de Carmel.
Saboda haka sai Dawuda ya tafi can tare da matansa biyu, Ahinowam daga Yezireyel da Abigiyel gwauruwar Nabal mutumin Karmel.
3 David fit remonter aussi les hommes qui étaient avec lui, chacun avec sa famille, et ils demeurèrent dans les villes de Hébron.
Dawuda kuma ya tafi tare da dukan mutanen da suke tare da shi, kowa da iyalinsa, suka zauna a Hebron da garuruwansa.
4 Et ceux de Juda vinrent, et oignirent là David pour Roi sur la maison de Juda. Et on fit rapport à David; en disant: Les hommes de Jabés de Galaad ont enseveli Saül.
Sa’an nan mutanen Yahuda suka zo Hebron, a can kuwa suka naɗa Dawuda sarkin Yahuda. Sa’ad da aka gaya wa Dawuda cewa mutanen Yabesh Gileyad ne suka binne Shawulu,
5 Et David envoya des messagers vers les hommes de Jabés de Galaad, et leur fit dire: Bénis soyez-vous de l'Eternel de ce que vous avez fait cette gratuité à Saül votre Seigneur, que de l'avoir enseveli.
sai ya aiki manzanni zuwa Yabesh Gileyad a ce musu, “Ubangiji yă albarkace ku saboda alherin da kuka nuna wa Shawulu ta wurin binne shi.
6 Que maintenant donc l'Eternel veuille user envers vous de gratuité, et de vérité; de ma part aussi je vous ferai du bien, parce que vous avez fait cela.
Bari Ubangiji yă nuna muku ƙaunarsa da amincinsa, ni kuma zan nuna muku irin wannan alherin saboda kun yi haka.
7 Et que maintenant vos mains se fortifient, et soyez hommes de cœur; car Saül votre Seigneur est mort, et la maison de Juda m'a oint pour être Roi sur eux.
Yanzu fa, sai ku ƙarfafa, ku yi jaruntaka, gama Shawulu sarkinku ya mutu, gidan Yahuda kuwa sun naɗa ni sarki a kansu.”
8 Mais Abner fils de Ner, chef de l'armée de Saül, prit Is-boseth fils de Saül, et le fit passer à Mahanajim;
Ana cikin haka, Abner ɗan Ner, komandan sojojin Shawulu, ya ɗauki Ish-Boshet ɗan Shawulu ya kawo shi Mahanayim.
9 Et l'établit Roi sur Galaad, et sur les Asuriens, et sur Jizréhel, et sur Ephraïm, et sur Benjamin; même sur tout Israël.
Ya naɗa shi sarkin Gileyad, da na Ashuri, da na Yezireyel, da a kan Efraim, da Benyamin, da kuma na dukan Isra’ila.
10 Is-boseth fils de Saül était âgé de quarante ans quand il commença à régner sur Israël, et il régna deux ans. Il n'y avait que la maison de Juda qui suivît David.
Ish-Boshet ɗan Shawulu yana da shekaru arba’in sa’ad da ya zama sarkin Isra’ila, ya kuma yi sarauta shekara biyu. Amma fa, gidan Yahuda, suka bi Dawuda.
11 Et le nombre des jours que David régna à Hébron sur la maison de Juda, fut de sept ans et six mois.
Tsawon lokacin da Dawuda ya yi mulki a Hebron a kan gidan Yahuda, shekara bakwai ne da wata shida.
12 Or Abner fils de Ner, et les gens d'Is-boseth fils de Saül, sortirent de Mahanajim, vers Gabaon.
Abner ɗan Ner, tare da mutanen Ish-Boshet ɗan Shawulu, suka bar Mahanayim suka tafi Gibeyon.
13 Joab aussi fils de Tséruja, et les gens de David sortirent, et ils se rencontrèrent les uns les autres près de l'étang de Gabaon; et les uns se tenaient auprès de l'étang du côté de deçà, et les autres auprès de l'étang du côté de delà.
Yowab wanda ake ce mamarsa Zeruhiya tare da waɗansu mutanen Dawuda suka fito suka haɗu da su tafkin Gibeyon, Suka zauna, waɗannan a wannan gefe, waɗancan a wancan gefe.
14 Alors Abner dit à Joab: Que quelques-uns de ces jeunes gens se lèvent maintenant, et qu'ils escarmouchent devant nous. Et Joab dit: Qu'ils se lèvent.
Sa’an nan Abner ya ce wa Yowab, “Bari mu bar waɗansu samari su tashi su yi faɗa hannu da hannu a gabanmu.” Yowab ya ce, “To, su tashi.”
15 Ils se levèrent donc, et on en compta douze de Benjamin pour le parti d'Is-boseth fils de Saül; et douze des gens de David.
Saboda haka samarin suka tashi aka ƙidaya su, mutum sha biyu wajen Benyamin da Ish-Boshet ɗan Shawulu, sha biyu kuma wajen Dawuda.
16 Alors chacun d'eux empoignant son homme lui passa son épée dans les flancs, et ils tombèrent tous ensemble; et ce lieu-là fut appelé Helkath-hatsurim, qui est en Gabaon.
Sa’an nan kowannensu ya kama abokin gābansa a kā ya soki da wuƙa a jiki, sai duka suka fāɗi a ƙasa. Saboda haka ne ake kiran wannan wuri Helkat Hazzurim a Gibeyon.
17 Et il y eut en ce jour-là un très-rude combat, dans lequel Abner fut battu avec ceux d'Israël par les gens de David.
Faɗan ya yi zafi a ranar ƙwarai, mutanen Dawuda suka ci mutanen Abner da na Isra’ila.
18 Les trois fils de Tséruja, Joab, Abisaï, et Hasaël étaient là. Et Hasaël était léger du pied comme un chevreuil [qui est] par les champs.
’Ya’yan Zeruhiya, maza uku sun kasance a can. Su ne, Yowab, Abishai da Asahel. To, Asahel mai gudu ne kamar barewa.
19 Et Hasaël poursuivit Abner, sans se détourner à droite ni à gauche d'après Abner.
Ya fafari Abner, bai juya dama ko hagu ba, yayinda yake fafararsa.
20 Abner donc regardant derrière soi, dit: Es-tu Hasaël? et [Hasaël] répondit: Je le suis.
Abner ya waiga, sai ya ce, “Kai ne, Asahel?” Ya ce, “Ni ne.”
21 Et Abner lui dit: Détourne-toi à droite ou à gauche, et saisis-toi de l'un de ces jeunes gens, et prends sa dépouille pour toi. Mais Hasaël ne voulut point se détourner de lui.
Sai Abner ya ce masa, “Yi dama ko hagu ka runtumi ɗaya daga cikin samarin, ka ƙwace makamansa.” Amma Asahel bai bar fafararsa ba.
22 Et Abner continuait à dire à Hasaël: Détourne-toi de moi; pourquoi te jetterais-je mort par terre? et comment oserais-je paraître devant Joab ton frère?
Abner ya sāke gargaɗe shi ya ce, “Ka bar fafarata! Yaya zan kashe ka? Yaya zan yin ido biyu da ɗan’uwanka Yowab?”
23 Mais il ne voulut jamais se détourner; et Abner le frappa de sa hallebarde à la cinquième côte du bout de derrière, tellement que sa hallebarde lui sortait par derrière, et il tomba là roide mort sur la place; et tous ceux qui venaient à l'endroit où Hasaël était tombé mort, s'arrêtaient.
Amma Asahel ya ƙi yă bar fafararsa; saboda haka Abner ya soki Asahel da māshinsa a ciki; har māshin ya fita ta bayansa. Nan take ya fāɗi, ya mutu. Kowa da ya zo wurin da Asahel ya fāɗi, ya mutu, sai yă tsaya.
24 Joab donc et Abisaï poursuivirent Abner, et le soleil se coucha quand ils arrivèrent au coteau d'Amma, qui est vis-à-vis de Gujah, au chemin du désert de Gabaon.
Amma Yowab da Abishai suka fafari Abner, kuma da rana tana fāɗuwa sai suka iso tudun Amma, kusa da Giya, a hanyar zuwa jejin Gibeyon.
25 Et les enfants de Benjamin s'assemblèrent auprès d'Abner, se rangèrent en un bataillon, et se tinrent sur le sommet d'un coteau.
Sa’an nan mutanen Benyamin suka haɗa kansu suka koyi bayan Abner. Suka zama ƙungiya guda, suka tsaya daram a kan tudu.
26 Alors Abner cria à Joab, et dit: L'épée dévorera-t-elle sans cesse? ne sais-tu pas bien que l'amertume est à la fin; et jusqu'à quand différeras-tu de dire au peuple, qu'il cesse de poursuivre ses frères?
Sai Abner ya kira Yowab ya ce, har abada ne māshi zai yi ta hallakarwa? Ba ka sani cewa ƙarshen zai zama da ɗaci ba. Sai yaushe za ka umarci mutanenka su daina fafaran’yan’uwansu?
27 Et Joab dit: Dieu est vivant, que si tu avais parlé ainsi, le peuple se serait retiré dès le matin chacun arrière de son frère.
Yowab ya ce, “Muddin Allah yana a raye, da ba a ce ka yi magana ba, da mutanen za su ci gaba da fafaran’yan’uwansu har gari yă waye.”
28 Joab donc sonna de la trompette et tout le peuple s'arrêta, ils ne poursuivirent plus Israël, et ils ne continuèrent plus à se battre.
Sai Yowab ya busa ƙaho, dukan mutane kuwa suka tsaya; suka daina fafaran Isra’ila. Nan take faɗan ya tsaya.
29 Ainsi Abner et ses gens marchèrent toute cette nuit-là par la campagne, traversèrent le Jourdain, passèrent par tout Bithron, et arrivèrent à Mahanajim.
Abner da mutanensa suka ratsa kwarin Urdun dukan dare. Sa’an nan suka haye kogin, suka kuwa ci gaba dukan safe har suka zo Mahanayim.
30 Joab aussi revint de la poursuite d'Abner; et quand il eut assemblé tout le peuple, on trouva qu'il en manquait dix-neuf des gens de David, et Hasaël.
Da Yowab ya dawo daga fafaran Abner, sai ya tattara dukan mutanensa. Ban da Asahel, sai ya gane an rasa mutum goma sha tara na Dawuda.
31 Mais les gens de David frappèrent de ceux de Benjamin, [savoir] des gens d'Abner, trois cent soixante hommes qui moururent.
Amma mutanen Dawuda sun kashe mutum ɗari uku da sittin daga kabilar Benyamin da suke tare da Abner.
32 Et ils enlevèrent Hasaël, et l'ensevelirent au sépulcre de son père, à Bethléhem; et toute cette nuit-là Joab et ses gens marchèrent et arrivèrent à Hébron sur le point du jour.
Suka ɗauki gawar Asahel suka binne a kabarin mahaifinsa a Betlehem. Sa’an nan Yowab da mutanensa suka bi dare har suka iso Hebron da safe.

< 2 Samuel 2 >