< 2 Rois 3 >

1 Or la dix-huitième année de Josaphat Roi de Juda, Joram fils d'Achab avait commencé à régner sur Israël en Samarie, et il régna douze ans.
Yoram, ɗan Ahab ya zama sarki Isra’ila, a Samariya, a shekara ta goma sha takwas ta mulkin Yehoshafat, sarkin Yahuda, ya kuma yi mulki shekara goma sha biyu.
2 Et fit ce qui déplaît à l'Eternel, non pas toutefois comme [avaient fait] son père et sa mère, car il ôta la statue de Bahal que son père avait faite.
Yoram ya aikata mugunta a gaban Ubangiji, amma ba kamar yadda mahaifinsa da mahaifiyarsa suka yi ba. Ya kawar da dutsen tsarkin Ba’al wanda mahaifinsa ya yi.
3 Mais il adhéra aux péchés de Jéroboam fils de Nébat, par lesquels il avait fait pécher Israël, [et] ne se détourna point d'aucun d'eux.
Duk da haka ya manne wa zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata, bai rabu da su ba.
4 Or Mésah, Roi de Moab, se mêlait de bétail, et payait au Roi d'Israël cent mille agneaux, et cent mille moutons [portant] laine.
Mesha, sarkin Mowab yana kiwon tumaki, ya kuma zama tilas yă biya haraji ga sarkin Isra’ila. Saboda haka yakan ba da’yan tumaki dubu ɗari, da kuma gashin raguna dubu ɗari.
5 Mais aussitôt qu'Achab fut mort, il arriva que le Roi de Moab se rebella contre le Roi d'Israël.
Amma bayan mutuwar Ahab, sai sarkin Mowab ya yi wa sarkin Isra’ila tawaye.
6 C'est pourquoi le Roi Joram sortit ce jour-là de Samarie, et dénombra tout Israël.
To, a lokacin, Sarki Yoram ya tashi daga Samariya, ya tattara sojoji daga dukan Isra’ila.
7 Puis il alla, et envoya vers Josaphat Roi de Juda, pour lui dire: Le Roi de Moab s'est rebellé contre moi, ne viendras-tu pas avec moi à la guerre contre Moab? et il répondit: J'y monterai; fais ton compte de moi comme de toi, de mon peuple comme de ton peuple, et de mes chevaux comme de tes chevaux.
Ya kuma aika da wannan saƙo ga Yehoshafat sarkin Yahuda cewa, “Sarkin Mowab ya yi mini tawaye. Za ka tafi tare da ni mu yaƙi Mowab?” Sai sarkin Yahuda ya ce, “I, ina shirye mu tafi. Ai, sojojina sojojinka ne, dawakaina kuma dawakanka ne.”
8 Ensuite il dit: Par quel chemin monterons-nous? Et il répondit: Par le chemin du désert d'Edom.
Ya ƙara da cewa, “Wace hanya za mu bi?” Sai Yoram ya amsa ya ce, “Ta hanyar jejin Edom.”
9 Ainsi le Roi d'Israël, et le Roi de Juda, et le Roi d'Edom partirent, et tournoyèrent par le chemin durant sept jours, jusqu'à ce qu'ils n'eurent plus d'eau pour le camp, ni pour les bêtes qu'ils menaient.
Saboda haka sarkin Isra’ila ya fita tare da sarkin Yahuda, da kuma sarkin Edom. Da suka yi kwana bakwai suna ta zagawa, sai sojoji da dabbobi suka rasa ruwan sha.
10 Et le Roi d'Israël dit: Ha! Ha! certainement l'Eternel a appelé ces trois Rois pour les livrer entre les mains de Moab.
Sai sarkin Isra’ila ya ce, “Mene! Ubangiji ya kira mu sarakunan nan uku don kawai yă ba da mu ga Mowab ne?”
11 Et Josaphat dit: N'y a-t-il point ici quelque Prophète de l'Eternel, afin que par son moyen nous consultions l'Eternel? Et un des serviteurs du Roi d'Israël répondit, et dit: Il y a ici Elisée fils de Saphat, qui versait de l'eau sur les mains d'Elie.
Amma Yehoshafat ya yi tambaya ya ce, “Babu wani annabin Ubangiji a nan da za mu nemi nufin Ubangiji ta wurinsa?” Wani hafsan sarkin Isra’ila ya amsa ya ce, “Ai, akwai Elisha ɗan Shafat, wanda dā ya yi wa Iliya hidima.”
12 Alors Josaphat dit: La parole de l'Eternel est avec lui; et le Roi d'Israël, et Josaphat, et le Roi d'Edom descendirent vers lui.
Yehoshafat ya ce, “Maganar Ubangiji tana tare da shi.” Saboda haka sarkin Isra’ila da Yehoshafat da kuma sarkin Edom suka tafi wurin Elisha.
13 Mais Elisée dit au Roi d'Israël: Qu'y a-t-il entre moi et toi? va-t'en vers les prophètes de ton père, et vers les prophètes de ta mère. Et le Roi d'Israël lui répondit: Non; car l'Eternel a appelé ces trois Rois pour les livrer entre les mains de Moab.
Elisha ya ce wa sarkin Isra’ila, “Ina ruwana da kai? Tafi wurin annabawan mahaifinka da annabawa mahaifiyarka.” Sai sarkin Isra’ila ya ce, “A’a, ai Ubangiji ne ya kira mu, mu sarakunan nan uku don yă bashe mu ga Mowab.”
14 Et Elisée dit: L'Eternel des armées, devant lequel je me tiens, est vivant, que si je n'avais de la considération pour Josaphat le Roi de Juda, je n'aurais aucun égard pour toi, et ne t'aurais même pas vu.
Sai Elisha ya ce, “Muddin Ubangiji Maɗaukaki yana a raye, wanda nake bauta, da ba don ina ganin girman Yehoshafat Sarkin Yahuda ba, da ko kallonka ba zan yi ba.
15 Mais maintenant amenez-moi un joueur d'instruments. Et comme le joueur jouait des instruments, la main de l'Eternel fut sur Elisée;
Amma yanzu, a kawo mini makaɗin garaya.” Yayinda makaɗin garayan yake kiɗa, ikon Ubangiji ya sauko a kan Elisha
16 Et il dit: Ainsi a dit l'Eternel: Qu'on coupe par des fossés toute cette vallée.
ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce, zan cika kwarin nan da tafkunan ruwa.
17 Car ainsi a dit l'Eternel: Vous ne verrez ni vent, ni pluie, et néanmoins cette vallée sera remplie d'eaux, et vous boirez, vous et vos bêtes.
Gama ga abin da Ubangiji ya ce, ko da yake babu iska, ko ruwan sama, duk da haka kwarin nan zai cika da ruwa, har ku da dabbobinku da kuma sauran dabbobi ku sha.
18 Encore cela est peu de chose pour l'Eternel; car il livrera Moab entre vos mains;
Wannan abu mai sauƙi ne a wurin Ubangiji; zai kuma ba da Mowab a gare ku.
19 Et vous détruirez toutes les villes fortes, et toutes les villes principales, et vous abattrez tous les bons arbres, et vous boucherez toutes les fontaines d'eaux, et vous gâterez avec des pierres tous les meilleurs champs.
Za ku ci kowane birni mai katanga, da kowane babban gari. Za ku sare kowane itace mai kyau, ku kuma tattoshe maɓuɓɓugan ruwa. Za ku kuma yi amfani da duwatsu ku lalatar da kowace gona mai kyau.”
20 Il arriva donc au matin, environ l'heure qu'on offre l'oblation, qu'on vit venir des eaux du chemin d'Edom, en sorte que ce lieu-là fut rempli d'eaux.
Kashegari, daidai lokacin hadaya, sai ga ruwa yana gangarowa daga gefen Edom! Ƙasar kuwa ta cika da ruwa.
21 Or tous les Moabites ayant appris que ces Rois-là étaient montés pour leur faire la guerre, s'étaient assemblés à cri public, depuis tous ceux qui étaient en âge de porter les armes, et au-dessus, et ils se tinrent sur la frontière.
To, dukan Mowabawa suka ji cewa sarakuna suna tafe don su yaƙe su; saboda haka aka kira kowane namiji, babba da yaro, wanda ya isa ɗaukan makami, aka jera su a bakin iyaka.
22 Et le lendemain ils se levèrent de bon matin, et comme le soleil fut levé sur les eaux, les Moabites virent vis-à-vis d'eux les eaux rouges comme du sang.
Da suka tashi da sassafe, rana tana haska ruwa. Sai ruwan ya yi ja kamar jini a idanun Mowabawan da suke a ƙetare.
23 Et ils dirent: C'est du sang; certainement ces Rois-là se sont entre-tués, et chacun a frappé son compagnon; maintenant donc, Moabites, au butin.
Sai suka ce, “Jini ne! Ba shakka sarakunan nan sun yaƙe juna, suka karkashe juna. Ya Mowabawa, mu tafi mu kwashi ganima!”
24 Ainsi ils vinrent au camp d'Israël, et les Israëlites se levèrent, et frappèrent les Moabites, lesquels s'enfuirent devant eux; puis ils entrèrent au pays, et frappèrent Moab.
Amma da Mowabawa suka isa sansanin Isra’ila, sai Isra’ilawa suka taso suka auka musu har sai da suka gudu. Isra’ilawa kuwa suka kai musu hari, suka karkashe Mowabawa.
25 Ils détruisirent les villes; et chacun jetait des pierres dans les meilleurs champs, de sorte qu'ils les en remplirent; ils bouchèrent toutes les fontaines d'eaux, et abattirent tous les bons arbres, jusqu'à ne laisser que les pierres à Kir-haréseth, laquelle les tireurs de fronde environnèrent, et battirent.
Suka ragargaza garuruwa, kowane mutum kuwa ya jefa dutse a kowane gona mai kyau har sai da aka rufe gonakin gaba ɗaya. Suka tattoshe duk maɓulɓulan ruwa, suka kuma sare duk itace mai kyau. Kir Hareset ne kaɗai aka bari tare da duwatsunsa yadda suke, amma mutanen da suke da majajjawa suka yi wa birnin zobe, suka kai masa hari shi ma.
26 Et le Roi de Moab voyant qu'il n'était pas le plus fort, prit avec lui sept cents hommes dégainant l'épée, pour enfoncer jusqu'au Roi d'Edom; mais ils ne purent.
Da sarkin Mowab ya ga yaƙi ya rinjaye shi, sai ya ɗauki mutane masu takobi ɗari bakwai, ya ratsa zuwa wajen sarkin Edom, amma ba su yi nasara ba.
27 Alors il prit son fils premier-né, qui devait régner en sa place, et l'offrit en holocauste sur la muraille, et il y eut une grande indignation en Israël; ainsi ils se retirèrent de lui, et s'en retournèrent en leur pays.
Sa’an nan ya ɗauki ɗansa na fari, wanda zai gāje shi, ya yi hadaya da shi a bisa katangan birnin. Isra’ilawa suka firgita ƙwarai; sai suka janye suka koma ƙasarsu.

< 2 Rois 3 >