< 2 Chroniques 25 >

1 Amatsia commença à régner étant âgé de vingt-cinq ans, et il régna vingt-neuf ans à Jérusalem. Sa mère avait nom Jéhohaddam, [et] elle était de Jérusalem.
Amaziya yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara ashirin da tara. Sunan mahaifiyarsa Yehoyaddin ce; ita daga Urushalima ne.
2 Il fit ce qui est droit devant l'Eternel; mais non pas d'un cœur parfait.
Ya yi abin da yake daidai a gaban Ubangiji, amma ba da dukan zuciyarsa ba.
3 Or il arriva qu'après qu'il fut affermi dans son Royaume, il fit mourir ses serviteurs qui avaient tué le Roi son père.
Bayan sarauta ta kahu a ƙarƙashinsa, sai ya kashe hafsoshin da suka kashe mahaifinsa sarki.
4 Mais il ne fit point mourir leurs enfants, selon ce qui est écrit dans la Loi, au Livre de Moïse, dans lequel l'Eternel a commandé, en disant: Les pères ne mourront point pour les enfants, et les enfants ne mourront point pour les pères; mais chacun mourra pour son péché.
Duk da haka bai kashe’ya’yansu maza ba amma ya yi bisa ga abin da yake a rubuce a cikin Doka, a cikin Littafin Musa, inda Ubangiji ya umarta, “Ba za a kashe iyaye saboda’ya’yansu ba; ba kuwa za a kashe’ya’ya saboda iyayensu ba; kowa zai mutu saboda zunubansa ne.”
5 Puis Amatsia assembla ceux de Juda; et les établit selon les familles des pères, selon les capitaines de milliers et de centaines, par tout Juda et Benjamin; et il en fit le dénombrement depuis l'âge de vingt ans, et au dessus; et il s'en trouva trois cent mille d'élite, marchant en bataille, et portant la javeline et le bouclier.
Amaziya ya tattara mutanen Yahuda ya kuma ba su aiki bisa ga iyalansu, ya ba da aiki ga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, a dukan Yahuda da Benyamin. Ya kuma tattara waɗanda suke’yan shekara ashirin da haihuwa ko fiye ya sami mutane dubu ɗari uku da suke a shirye don aikin soja, da suka isa riƙe māshi da garkuwa.
6 Il prit aussi à sa solde cent mille hommes forts et vaillants de ceux d'Israël, pour cent talents d'argent.
Ya kuma ɗauko sojan haya jarumawa dubu ɗari ɗaya daga Isra’ila a kan talenti ɗari na azurfa.
7 Mais un homme de Dieu vint à lui, et lui dit: Ô Roi! que l'armée d'Israël ne marche point avec toi, car l'Eternel n'est point avec Israël; ils sont tous enfants d'Ephraïm.
Amma mutumin Allah ya zo wurinsa ya ce, “Ya sarki, waɗannan runduna daga Isra’ila ba za su tafi tare da kai ba, gama Ubangiji ba ya tare da Isra’ila, ba ya nan da wani cikin mutanen Efraim.
8 Sinon, va, fais, fortifie-toi pour la bataille; [mais] Dieu te fera tomber devant l'ennemi; car Dieu a la puissance d'aider et de faire tomber.
Ko da ma ya tafi ya yi faɗa da ƙwazo a cikin yaƙi, Allah zai tumɓuke shi a gaban abokan gāba, gama Allah yana da iko yă taimaka ko yă tumɓuke.”
9 Et Amatsia répondit à l'homme de Dieu: Mais que deviendront les cent talents que j'ai donnés aux troupes d'Israël? et l'homme de Dieu dit: L'Eternel en a pour t'en donner beaucoup plus.
Amaziya ya tambayi mutumin Allah ya ce, “Amma game da talenti ɗarin da na biya saboda waɗannan rundunonin Isra’ila fa?” Mutumin Allah ya amsa, “Ubangiji zai ba ka fiye da wannan.”
10 Ainsi Amatsia sépara les troupes qui lui étaient venues d'Ephraïm, afin qu'elles retournassent en leur lieu; et leur colère s'enflamma fort contre Juda, et ils s'en retournèrent en leur lieu avec une grande ardeur de colère.
Saboda haka Amaziya ya sallame rundunonin da suka zo daga Efraim, ya kuma mayar da su gida. Suka husata da Yahuda suka koma gida da fushi sosai.
11 Alors Amatsia ayant pris courage conduisit son peuple, et s'en alla en la vallée du sel; où il battit dix mille hommes des enfants de Séhir.
Sa’an nan Amaziya ya yi ƙarfin hali ya jagoranci mayaƙansa zuwa Kwarin Gishiri, inda ya kashe mutanen Seyir dubu goma.
12 Et les enfants de Juda prirent dix mille hommes vifs, et les ayant amenés sur le sommet d'une roche, ils les jetèrent du haut de la roche, de sorte qu'ils moururent tous.
Mayaƙan Yahuda suka kuma kama mutane dubu goma da rai, suka ɗauke su zuwa ƙwanƙolin dutsen, suka yi ta tunkuɗa su ƙasa suka yi kaca-kaca.
13 Mais les troupes qu'Amatsia avait renvoyées, afin qu'elles ne vinssent point avec lui à la guerre, se jetèrent sur les villes de Juda, depuis Samarie jusqu'à Béthoron, et tuèrent trois mille hommes, et emportèrent un gros butin.
Ana cikin haka, sai rundunar da Amaziya ya mai da su gida, waɗanda ba a bari suka tafi yaƙin ba, suka kai wa garuruwan Yahuda daga Samariya zuwa Bet-Horon hari. Suka kashe mutane dubu uku suka kwashe ganima mai yawan gaske.
14 Or il arriva qu'Amatsia étant revenu de la défaite des Iduméens, et ayant apporté les dieux des enfants de Séhir, il se les établit pour dieux; il se prosterna devant eux, et leur fit des encensements.
Da Amaziya ya dawo daga kisan mutanen Edom, sai ya dawo da allolin mutanen Seyir. Ya kafa su a matsayin allolinsa, ya rusuna musu, ya kuma miƙa musu hadayun ƙonawa.
15 Et la colère de l'Eternel s'enflamma contre Amatsia, et il envoya vers lui un Prophète qui lui dit: Pourquoi as-tu recherché les dieux d'un peuple qui n'ont point délivré leur peuple de ta main?
Fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan Amaziya, sai ya aiki wani annabi wurinsa wanda ya ce, “Me ya sa ka nemi shawarar allolin mutanen nan, waɗanda ba za su cece mutanensu daga hannunka ba?”
16 Et comme il parlait au Roi, le Roi lui dit: T'a-t-on établi conseiller du Roi? arrête-toi; pourquoi te ferais-tu tuer? et le Prophète s'arrêta, et lui dit: Je sais très-bien que Dieu a délibéré de te détruire, parce que tu as fait cela, et que tu n'as point obéi à mon conseil.
Tun yana cikin magana, sai sarki ya ce masa, “Yaushe muka naɗa ka mai ba sarki shawara? Rufe mana baki! Me zai hana a kashe ka?” Sai annabin ya yi shiru, amma ya ce, “Na dai sani Allah ya riga ya shirya zai hallaka ka, saboda ka aikata wannan, ba ka kuma saurari shawarata ba.”
17 Et Amatsia Roi de Juda, ayant tenu conseil, envoya vers Joas fils de Jéhoachaz, fils de Jéhu, Roi d'Israël, pour [lui] dire: Viens, [et] que nous nous voyions l'un l'autre.
Bayan Amaziya sarkin Yahuda ya nemi shawara mashawartansa, sai ya kalubalanci Yowash ɗan Yehoyahaz, ɗan Yehu, sarkin Isra’ila, “Zo mu gamu fuska da fuska.”
18 Et Joas Roi d'Israël envoya dire à Amatsia Roi de Juda: L'épine qui est au Liban a envoyé dire au cèdre qui est au Liban: Donne ta fille pour femme à mon fils; mais les bêtes sauvages qui sont au Liban, ont passé, et ont foulé l'épine.
Amma Yowash sarkin Isra’ila ya amsa wa Amaziya sarkin Yahuda ya ce, “Wata ƙaya ce a Lebanon, ta aika da saƙo wa itacen al’ul na Lebanon cewa, ‘Ka ba ɗana’yarka aure.’ Sai wani naman jeji na Lebanon ya zo ya tattake ƙayar.
19 Tu as dit: Voici, j'ai battu Edom, et ton cœur s'est élevé pour en tirer vanité. Demeure maintenant dans ta maison; pourquoi t'engagerais-tu dans un mal dans lequel tu tomberais, toi et Juda avec toi?
Ka ce wa kanka cewa ka ci Edom da yaƙi, yanzu kuwa kana fariya da ɗaga kai. Amma tsaya dai a gida! Me ya sa kake neman faɗa kana neman fāɗuwarka da ta Yahuda?”
20 Mais Amatsia ne l'écouta point; car cela venait de Dieu, afin de les livrer entre les mains de [Joas], parce qu'ils avaient recherché les dieux d'Edom.
Amma Amaziya bai saurara ba gama Allah ya yi haka domin yă miƙa su ga Yehowash, domin sun nemi shawarar allolin Edom.
21 Ainsi Joas Roi d'Israël monta, et ils se virent l'un l'autre, lui et Amatsia Roi de Juda, à Beth-sémes, qui est de Juda.
Saboda haka Yowash sarkin Isra’ila ya kai yaƙi. Shi da Amaziya sarkin Yahuda suka fuskanci juna a Bet-Shemesh a Yahuda.
22 Et Juda ayant été défait par Israël, ils s'enfuirent chacun dans leurs tentes.
Isra’ila ta fatattaki Yahuda, sai kowane mutum ya gudu zuwa gidansa.
23 Et Joas Roi d'Israël prit Amatsia Roi de Juda, fils de Joas, fils de Jéhoachaz, à Beth-sémes; et l'amena à Jérusalem, et il fit une brèche de quatre cents coudées à la muraille de Jérusalem, depuis la porte d'Ephraïm, jusqu'à la porte du coin.
Yehowash sarkin Isra’ila ya kama Amaziya sarkin Yahuda, ɗan Yowash, ɗan Ahaziya a Bet-Shemesh. Sa’an nan Yehowash ya kawo shi Urushalima ya farfasa katangar Urushalima daga Ƙofar Efraim har zuwa Ƙofar Kusurwa, wani sashe mai tsawon ƙafa ɗari shida.
24 Et ayant pris tout l'or et l'argent, et tous les vaisseaux qui furent trouvés dans la maison de Dieu sous la direction d'Hobed-Edom, avec les trésors de la Maison Royale, et des gens pour otages, il s'en retourna à Samarie.
Ya kwashe dukan zinariya da azurfa da dukan kayayyakin da aka samu a haikalin Allah waɗanda suke a ƙarƙashin kulawar Obed-Edom, da kaya masu daraja na gidan sarki, da waɗanda aka kamo cikin yaƙi, ya kawo Samariya.
25 Et Amatsia fils de Joas Roi de Juda vécut quinze ans, après que Joas fils de Jéhoachaz Roi d'Israël fut mort.
Amaziya ɗan Yowash sarkin Yahuda ya rayu shekara goma sha biyar bayan mutuwar Yehowash ɗan Yehoyahaz sarkin Isra’ila.
26 Le reste des faits d'Amatsia, tant les premiers que les derniers, voilà; n'est-il pas écrit au Livre des Rois de Juda et d'Israël?
Game da sauran ayyukan mulkin Amaziya, daga farko zuwa ƙarshe, an rubuta su a littafin sarakunan Yahuda da Isra’ila.
27 Or depuis le temps qu'Amatsia se fut détourné de l'Eternel, on fit une conspiration contre lui à Jérusalem, et il s'enfuit à Lakis; mais on envoya après lui à Lakis, et on le tua là.
Sa’ad da Amaziya ya bar bin Ubangiji, aka shirya masa maƙarƙashiya a Urushalima, sai ya gudu zuwa Lakish, amma suka aiki mutane suka bi shi zuwa Lakish, a can suka kashe shi.
28 Et on l'apporta sur des chevaux, et on l'ensevelit avec ses pères dans la ville de Juda.
Aka dawo da shi a kan doki, aka binne shi tare da kakanninsa a Birnin Yahuda.

< 2 Chroniques 25 >