< 1 Samuel 23 >

1 Or on avait fait ce rapport à David, en disant: Voilà, les Philistins font la guerre à Kéhila, et pillent les aires.
Sa’ad da aka ce wa Dawuda, “Duba ga Filistiyawa suna yaƙi da mutanen Keyila, suna kwashe musu hatsi a masussukai.”
2 Et David consulta l'Eternel en disant: Irai-je, et frapperai-je ces Philistins-là? et l'Eternel répondit à David: Va, et tu frapperas les Philistins, et tu délivreras Kéhila.
Sai Dawuda ya nemi nufin Ubangiji, ya ce, “In tafi in fāɗa wa Filistiyawa da yaƙi?” Ubangiji kuwa ya ce masa, “Jeka ka yi yaƙi da Filistiyawa, ka ceci Keyila.”
3 Et les gens de David lui dirent: Voici, nous étant ici en Juda avons peur; que sera-ce donc quand nous serons allés à Kéhila contre les troupes rangées des Philistins?
Amma mutanen Dawuda suka ce masa, “Ga shi, a nan ma a Yahuda muna jin tsoro, balle mu tafi Keyila mu yi yaƙi da sojojin Filistiyawa!”
4 C'est pourquoi David consulta encore l'Eternel, et l'Eternel lui répondit, et dit: Lève-toi, descends à Kéhila, car je m'en vais livrer les Philistins entre tes mains.
Dawuda ya sāke nemi nufin Ubangiji, sai Ubangiji ya ce masa, “Tashi ka gangara zuwa Keyila, gama zan ba da Filistiyawa a hannunka.”
5 Alors David s'en alla avec ses gens à Kéhila, et combattit contre les Philistins, et emmena leur bétail, et fit un grand carnage [des Philistins]; ainsi David délivra les habitants de Kéhila.
Sa’an nan Dawuda da mutanensa suka tafi Keyila, suka yi yaƙi da Filistiyawa, suka kwashe musu shanunsu, suka jijji wa Filistiyawa ƙwarai, suka cece mutanen Keyila daga hannunsu.
6 Or il était arrivé que quand Abiathar fils d'Ahimélec s'était enfui vers David à Kéhila, l'Ephod lui était tombé entre les mains.
(Abiyatar ɗan Ahimelek ya zo da efod sa’ad da ya gudo zuwa wurin Dawuda a Keyila.)
7 Et on rapporta à Saül que David était venu à Kéhila; et Saül dit: Dieu l'a livré entre mes mains; car il s'est enfermé en entrant dans une ville qui a des portes et des barres.
Shawulu ya sami labari cewa Dawuda ya tafi Keyila, sai ya ce, “Allah ya bashe shi a hannuna, domin Dawuda ya kulle kansa ke nan da ya shiga birnin da yake da ƙofofin da ake kulle da ƙarafa.”
8 Et Saül assembla à cri public tout le peuple pour [aller à la] guerre, [et] descendre à Kéhila, afin d'assiéger David et ses gens.
Shawulu ya kira dukan sojojinsa don yaƙi, su gangaro zuwa Keyila su mamaye Dawuda da mutanensa.
9 Mais David ayant su que Saül lui machinait ce mal, dit au Sacrificateur Abiathar: Mets l'Ephod.
Da Dawuda ya ji labari Shawulu yana shirya hanyar da zai kashe shi, sai ya ce wa Abiyatar firist, “Kawo mini efod a nan.”
10 Puis David dit: Ô Eternel! Dieu d'Israël! ton serviteur a appris comme une chose certaine, que Saül cherche d'entrer dans Kéhila, pour détruire la ville à cause de moi.
Dawuda ya ce, “Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, bawanka ya sami labari cewa tabbatacce Shawulu yana shirin zuwa Keyila yă hallaka garin saboda ni.
11 Les Seigneurs de Kéhila me livreront-ils entre ses mains? Saül descendra-t-il, comme ton serviteur l'a ouï dire? Ô Eternel! Dieu d'Israël! je te prie, enseigne-le à ton serviteur. Et l'Eternel répondit: Il descendra.
Mutanen Keyila za su bashe ni a gare shi? Shawulu zai gangaro nan kamar yadda bawanka ya sami labari? Ya Ubangiji, Allah na Isra’ila, ka gaya wa bawanka.” Ubangiji ya ce, “Zai zo.”
12 David dit encore: Les Seigneurs de Kéhila me livreront-ils, moi et mes gens, entre les mains de Saül? Et l'Eternel répondit: Ils t'y livreront.
Dawuda ya sāke cewa, “Mutanen Keyila za su bashe ni da mutanena ga Shawulu?” Ubangiji ya ce, “Za su yi.”
13 Alors David se leva, et environ six cents hommes avec lui, et ils sortirent de Kéhila, et s'en allèrent où ils purent; et on rapporta à Saül que David s'était sauvé de Kéhila: c'est pourquoi il cessa de marcher.
Saboda haka Dawuda da mutanensa wajen mutum ɗari shida suka bar Keyila, suka yi ta tafiya daga wannan wuri zuwa wancan. Sa’ad da aka gaya wa Shawulu cewa Dawuda ya tsere daga Keyila, sai ya fasa tafiya can.
14 Et David demeura au désert dans des lieux forts, et il se tint en une montagne au désert de Ziph. Et Saül le cherchait tous les jours, mais Dieu ne le livra point entre ses mains.
Dawuda ya zauna a jeji cikin kogunan duwatsu da kuma tuddan jejin Zif. Kowace rana Shawulu ya yi ta neman Dawuda amma Allah bai bashe Dawuda a hannunsa ba.
15 David donc ayant vu que Saül était sorti pour chercher sa vie, se tint au désert de Ziph en la forêt.
A lokacin da Dawuda yana zaune a Horesh cikin jejin Zif, ya sami labari cewa Shawulu ya fito don yă kashe shi.
16 Alors Jonathan fils de Saül se leva, et s'en alla en la forêt vers David, et fortifia ses mains en Dieu.
Yonatan ɗan Shawulu kuwa ya tafi wurin Dawuda a Horesh, ya ƙarfafa shi yă dogara ga Allah.
17 Et lui dit: Ne crains point; car Saül mon père ne t'attrapera point, mais tu régneras sur Israël, et moi je serai le second après toi; et même Saül mon père le sait bien.
Ya ce, “Kada ka ji tsoro, mahaifina Shawulu ba zai taɓa sa hannu a kanka ba. Za ka zama sarki a Isra’ila, ni kuma in zama na biyu gare ka. Kai, ko mahaifina Shawulu ma ya san da haka.”
18 Ils traitèrent donc eux deux alliance devant l'Eternel; et David demeura dans la forêt, mais Jonathan retourna en sa maison.
Su biyunsu kuwa suka ɗaura yarjejjeniya a gaban Ubangiji. Sai Yonatan ya koma gida amma Dawuda ya zauna Horesh.
19 Or les Ziphiens montèrent vers Saül à Guibha, et lui dirent: David ne se tient-il pas caché parmi nous, dans des lieux forts, dans la forêt, au coteau de Hakila, qui est à main droite de Jésimon?
Zifawa suka tafi wurin Shawulu a Gibeya suka ce masa, “Ashe, ba Dawuda ne yake ɓuya a cikinmu a kogwannin duwatsu a Horesh a bisan tudun Hakila, kudu da Yeshimon ba?
20 Maintenant donc, ô Roi! si tu souhaites de descendre, descends, et ce sera à nous à le livrer entre les mains du Roi.
Yanzu, ya sarki, ka gangaro, ka zo a duk lokacin da ka ga ya yi maka, ka zo mu kuma hakkinmu ne mu bashe shi a hannun sarki.”
21 Et Saül dit: Bénis soyez-vous de par l'Eternel, de ce que vous avez eu pitié de moi.
Shawulu ya ce, “Ubangiji ya yi muku albarka, gama kun damu da ni.
22 Allez donc, je vous prie, et préparez toutes choses, et sachez, et reconnaissez le lieu, où il fait sa retraite, [et] qui l'aura vu là; car on m'a dit, qu'il est fort rusé.
Ku tafi ku ƙara shiri. Ku san inda yakan tafi, wane ne kuma ya gan shi a can. An gaya mini cewa shi mai wayo ne sosai.
23 Reconnaissez donc et sachez dans laquelle de toutes ces retraites il se tient caché, puis retournez vers moi quand vous en serez assurés, et j'irai avec vous; et s'il est au pays, je le chercherai soigneusement parmi tous les milliers de Juda.
Ku binciko duk wuraren da yakan ɓuya, sai ku dawo ku gaya mini tabbataccen labari. Sa’an nan zan tafi tare da ku in yana can. Zan nemi shi ko’ina cikin dukan kabilar Yahuda.”
24 Ils se levèrent donc et s'en allèrent à Ziph devant Saül; mais David et ses gens étaient au désert de Mahon, en la campagne, à main droite de Jésimon.
Sai suka tashi suka koma Zif, suka sha gaban Shawulu. Dawuda da mutanensa kuwa suna jejin Mawon cikin Araba, kudu da Yeshimon.
25 Ainsi Saül et ses gens s'en allèrent le chercher; et on le rapporta à David: et il descendit dans la roche, et demeura au désert de Mahon: ce que Saül ayant appris, il poursuivit David au désert de Mahon.
Shawulu da mutanensa suka tafi neman Dawuda. Da Dawuda ya ji labari, sai ya gangara cikin duwatsu ya zauna a cikin jejin Mawon. Sa’ad da Shawulu ya ji haka, sai ya tafi jejin Mawon yana fafaran Dawuda.
26 Et Saül allait de deçà le côté de la montagne, et David et ses gens allaient de delà, à l'autre côté de la montagne; et David se hâtait autant qu'il pouvait de s'en aller de devant Saül, mais Saül et ses gens environnèrent David et ses gens pour les prendre.
Shawulu yana tafiya a gefe ɗaya na dutsen, Dawuda da mutanensa kuma suna a wancan gefe, suna hanzari su ɓace wa Shawulu. Sa’ad da Shawulu da sojojinsa suka kusa cimma Dawuda da mutanensa don su kama su,
27 Sur cela un messager vint à Saül, en disant: Hâte-toi, et viens, car les Philistins se sont jetés sur le pays.
sai wani manzo ya zo wurin Shawulu yana cewa, “Ka koma da sauri, Filistiyawa sun kawo wa ƙasar hari.”
28 Ainsi Saül s'en retourna de la poursuite de David, et s'en alla au devant des Philistins: c'est pourquoi on a appelé ce lieu-là Sélah-hammahlekoth.
Shawulu kuwa ya janye daga fafaran Dawuda, ya tafi yă ƙara da Filistiyawa. Dalilin ke nan da ake kiran wannan wuri Sela Hammalekot, wato, dutsen tserewa.
29 Puis David monta de là, et demeura dans les lieux forts de Hen-guédi.
Dawuda kuwa ya haura daga can ya zauna a kogwannin duwatsun En Gedi.

< 1 Samuel 23 >