< 1 Rois 19 >

1 Or Achab rapporta à Izebel tout ce qu'Elie avait fait, et comment il avait entièrement tué avec l'épée tous les Prophètes.
Ahab fa ya faɗa wa Yezebel kome da Iliya ya yi, da yadda ya karkashe dukan annabawan da takobi.
2 Et Izebel envoya un messager vers Elie, pour lui dire: Ainsi fassent les dieux, et ainsi ils y ajoutent, si demain, à cette heure-ci, je ne te mets au même état que l'un d'eux.
Saboda haka Yezebel ta aika da ɗan aika wa Iliya yă faɗa masa, “Bari alloli su hukunta ni da tsanani, in war haka gobe ban mai da ranka kamar na ɗaya daga cikin annabawan Ba’al ba.”
3 Et [Elie] voyant cela se leva, et s'en alla comme son cœur lui disait. Il s'en vint à Beersebah, qui appartient à Juda; et il laissa là son serviteur.
Iliya ya ji tsoro, ya gudu don yă ceci ransa. Sa’ad da ya kai Beyersheba a Yahuda, sai ya bar bawansa a can.
4 Mais lui s'en alla au désert, le chemin d'un jour, et y étant venu il s'assit sous un genêt, et demanda que Dieu retirât son âme, et dit: C'est assez, ô Eternel! prends maintenant mon âme; car je ne suis pas meilleur que mes pères.
Shi kuma ya yi tafiya yini guda zuwa cikin hamada. Ya zo wurin wani itacen tsintsiya, ya zauna a ƙarƙashinsa, ya roƙa yă mutu. Ya ce, “Ya ishe ni haka, Ubangiji, ka ɗauki raina; ban fi kakannina ba.”
5 Puis il se coucha, et s'endormit sous un genêt; et voici un Ange le toucha, et lui dit: Lève-toi, mange.
Sa’an nan ya kwanta a ƙarƙashin itacen ya yi barci. Farat ɗaya sai wani mala’ika ya taɓa shi, ya ce, “Tashi ka ci abinci.”
6 Et il regarda, et voici à son chevet un gâteau cuit aux charbons, et une fiole d'eau. Il mangea donc et but, et se recoucha.
Ya duba kewaye, sai ga wainar burodi kusa da kansa a bisa garwashin wuta mai zafi, da kuma tulun ruwa. Ya ci, ya sha, sa’an nan ya sāke kwanta.
7 Et l'Ange de l'Eternel retourna pour la seconde fois, et le toucha, et lui dit: Lève-toi, mange; car le chemin est trop long pour toi.
Mala’ikan Ubangiji ya sāke dawowa sau na biyu ya taɓa shi, ya ce, “Tashi ka ci abinci, gama tafiyar za tă yi maka yawa.”
8 Il se leva donc, et mangea et but; puis avec la force que lui donna ce repas il marcha quarante jours et quarante nuits, jusqu'à Horeb, la montagne de Dieu.
Saboda haka ya tashi ya ci, ya kuma sha. Ta wurin ƙarfin da ya samu saboda wannan abinci, ya yi tafiya yini arba’in da dare arba’in, sai da ya kai Horeb, dutsen Allah.
9 Et là il entra dans une caverne, et y passa la nuit. Ensuite voilà, la parole de l'Eternel lui [fut adressée], et [l'Eternel] lui dit: Quelle affaire as-tu ici, Elie?
A can ya shiga kogo ya kwana. Sai maganar Ubangiji ta zo masa, ta ce, “Me kake yi a nan, Iliya?”
10 Et il répondit: J'ai été extrêmement ému à jalousie pour l'Eternel le Dieu des armées, parce que les enfants d'Israël ont abandonné ton alliance; ils ont démoli tes autels, ils ont tué tes Prophètes avec l'épée, je suis resté moi seul, et ils cherchent ma vie pour me l'ôter.
Ya amsa, ya ce, “Ina kishi dominka Ubangiji, Allah Maɗaukaki. Isra’ilawa sun ƙi alkawarinka, suka rurrushe bagadanka, suka kuma kashe annabawanka da takobi. Ni ne kaɗai na rage, yanzu, ni ma suna ƙoƙari su kashe ni.”
11 Mais il lui dit: Sors, et tiens-toi sur la montagne devant l'Eternel. Et voici, l'Eternel passait, et un grand vent impétueux, qui fendait les montagnes, et brisait les rochers, allait devant l'Eternel; mais l'Eternel n'était point dans ce vent. Après le vent [se fit] un tremblement; mais l'Eternel n'était point dans ce tremblement.
Sai Ubangiji ya ce, “Fita ka tsaya a kan dutse a gaban Ubangiji, gama Ubangiji yana shirin wucewa.” Sai ga babbar iska mai ƙarfi ta tsage duwatsu, ta kuma ragargaza duwatsu a gaban Ubangiji, amma Ubangiji ba ya cikin iskar. Bayan iskar sai aka yi girgizar ƙasa, amma Ubangiji ba ya cikin girgizar ƙasa.
12 Après le tremblement venait un feu; mais l'Eternel n'était point dans ce feu. Après le feu venait un son doux et subtil.
Bayan girgizar ƙasa, sai ga wuta, amma Ubangiji ba ya cikin wuta. Bayan wutar kuma sai ga wata’yar murya.
13 Et il arriva que dès qu'Elie l'eut entendu, il enveloppa son visage de son manteau, et sortit, et se tint à l'entrée de la caverne, et voici, une voix lui [fut adressée], et lui dit: Quelle affaire as-tu ici, Elie?
Sa’ad da Iliya ya ji ta, ya ja mayafinsa ya rufe fuskarsa, ya fita ya tsaya a bakin kogon. Sai ya ji murya ta ce masa, “Me kake yi a nan, Iliya?”
14 Et il répondit: J'ai été extrêmement ému à jalousie pour l'Eternel le Dieu des armées, parce que les enfants d'Israël ont abandonné ton alliance; ils ont démoli tes autels, ils ont tué tes prophètes avec l'épée; je suis resté moi seul; et ils cherchent ma vie pour me l'ôter.
Ya amsa, ya ce, “Ina kishi dominka Ubangiji, Allah Maɗaukaki. Isra’ilawa sun ƙi alkawarinka, suka rurrushe bagadanka, suka kuma kashe annabawanka da takobi. Ni ne kaɗai na rage, yanzu, ni ma suna ƙoƙari su kashe ni.”
15 Mais l'Eternel lui dit: Va, retourne-t'en par ton chemin vers le désert de Damas, et quand tu seras arrivé tu oindras Hazaël pour Roi sur la Syrie.
Sai Ubangiji ya ce masa, “Ka koma ta hanyar da ka zo, ka tafi Hamadan Damaskus. Sa’ad da ka kai can, ka shafe Hazayel yă zama sarki bisa Aram.
16 Tu oindras aussi Jéhu fils de Nimsi pour Roi sur Israël; et tu oindras Elisée fils de Saphat, qui est d'Abel-méhola pour Prophète en ta place.
Ka kuma shafe Yehu ɗan Nimshi yă zama sarkin Isra’ila, ka shafe Elisha ɗan Shafat daga Abel-Mehola yă gāje ka a matsayin annabi.
17 Et il arrivera que quiconque échappera de l'épée de Hazaël, Jéhu le fera mourir; et quiconque échappera de l'épée de Jéhu, Elisée le fera mourir.
Yehu zai kashe duk wani wanda ya tsere wa takobin Hazayel, Elisha kuwa zai kashe duk wani wanda ya tsere wa takobin Yehu.
18 Mais je me suis réservé sept mille hommes de reste en Israël, [savoir], tous ceux qui n'ont point fléchi leurs genoux devant Bahal, et dont la bouche ne l'a point baisé.
Duk da haka zan bar mutane dubu bakwai na Isra’ila waɗanda ba su rusuna da gwiwansu wa Ba’al ba, ba su kuma sumbace shi da bakinsu ba.”
19 Elie donc partit de là, et trouva Elisée fils de Saphat, qui labourait ayant douze paires [de bœufs] devant soi, et il était avec la douzième. Quand Elie eut passé vers lui, il jeta son manteau sur lui.
Sai Iliya ya tafi daga can ya sami Elisha ɗan Shafat, yana noma da shanu goma sha biyu masu garman noma, shi kansa yana jan na goma sha biyun. Iliya ya tafi wurinsa ya jefa mayafinsa a kan Elisha.
20 Et [Elisée] laissa ses bœufs, et courut après Elie, et dit: Je te prie, que je baise mon père, et ma mère, et puis je te suivrai. Et il lui dit: Va, [et] retourne; car que t'ai-je fait?
Sai Elisha ya bar shanun, ya ruga ya bi Iliya. Ya ce, “Bari in sumbace mahaifina da mahaifiyata, in yi musu bankwana, sa’an nan in zo in bi ka.” Iliya ya ce, “Koma! Me na yi maka?”
21 Il s'en retourna donc d'avec lui et prit une paire de bœufs, et les sacrifia; et de l'attelage des bœufs il en bouillit la chair, et la donna au peuple, et ils mangèrent; puis il se leva, et suivit Elie, et il le servait.
Sai Elisha ya bar shi, ya koma, ya ɗauki shanunsa ya yayyanka. Ya ƙone kayan garman noman don yă dafa naman, ya kuma ba wa mutane naman, suka kuwa ci. Sa’an nan ya tashi, ya bi Iliya, ya kuma zama mai hidimarsa.

< 1 Rois 19 >