< Psaumes 89 >

1 Cantique d’Éthan, l’Ezrachite. Je chanterai toujours les bontés de l’Éternel; Ma bouche fera connaître à jamais ta fidélité.
Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
2 Car je dis: La bonté a des fondements éternels; Tu établis ta fidélité dans les cieux.
Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
3 J’ai fait alliance avec mon élu; Voici ce que j’ai juré à David, mon serviteur:
Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
4 J’affermirai ta postérité pour toujours, Et j’établirai ton trône à perpétuité. (Pause)
cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
5 Les cieux célèbrent tes merveilles, ô Éternel! Et ta fidélité dans l’assemblée des saints.
Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
6 Car qui, dans le ciel, peut se comparer à l’Éternel? Qui est semblable à toi parmi les fils de Dieu?
Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
7 Dieu est terrible dans la grande assemblée des saints, Il est redoutable pour tous ceux qui l’entourent.
Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
8 Éternel, Dieu des armées! Qui est comme toi puissant, ô Éternel? Ta fidélité t’environne.
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
9 Tu domptes l’orgueil de la mer; Quand ses flots se soulèvent, tu les apaises.
Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
10 Tu écrasas l’Égypte comme un cadavre, Tu dispersas tes ennemis par la puissance de ton bras.
Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
11 C’est à toi qu’appartiennent les cieux et la terre, C’est toi qui as fondé le monde et ce qu’il renferme.
Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
12 Tu as créé le nord et le midi; Le Thabor et l’Hermon se réjouissent à ton nom.
Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
13 Ton bras est puissant, Ta main forte, ta droite élevée.
Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
14 La justice et l’équité sont la base de ton trône. La bonté et la fidélité sont devant ta face.
Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
15 Heureux le peuple qui connaît le son de la trompette; Il marche à la clarté de ta face, ô Éternel!
Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
16 Il se réjouit sans cesse de ton nom, Et il se glorifie de ta justice.
Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
17 Car tu es la gloire de sa puissance; C’est ta faveur qui relève notre force.
Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
18 Car l’Éternel est notre bouclier, Le Saint d’Israël est notre roi.
Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
19 Alors tu parlas dans une vision à ton bien-aimé, Et tu dis: J’ai prêté mon secours à un héros, J’ai élevé du milieu du peuple un jeune homme;
Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
20 J’ai trouvé David, mon serviteur, Je l’ai oint de mon huile sainte.
Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
21 Ma main le soutiendra, Et mon bras le fortifiera.
Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
22 L’ennemi ne le surprendra pas, Et le méchant ne l’opprimera point;
Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
23 J’écraserai devant lui ses adversaires, Et je frapperai ceux qui le haïssent.
Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
24 Ma fidélité et ma bonté seront avec lui, Et sa force s’élèvera par mon nom.
Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
25 Je mettrai sa main sur la mer, Et sa droite sur les fleuves.
Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
26 Lui, il m’invoquera: Tu es mon père, Mon Dieu et le rocher de mon salut!
Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
27 Et moi, je ferai de lui le premier-né, Le plus élevé des rois de la terre.
Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
28 Je lui conserverai toujours ma bonté, Et mon alliance lui sera fidèle;
Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
29 Je rendrai sa postérité éternelle, Et son trône comme les jours des cieux.
Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
30 Si ses fils abandonnent ma loi Et ne marchent pas selon ses ordonnances,
“In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
31 S’ils violent mes préceptes Et n’observent pas mes commandements,
in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
32 Je punirai de la verge leurs transgressions, Et par des coups leurs iniquités;
zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
33 Mais je ne lui retirerai point ma bonté Et je ne trahirai pas ma fidélité,
amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
34 Je ne violerai point mon alliance Et je ne changerai pas ce qui est sorti de mes lèvres.
Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
35 J’ai juré une fois par ma sainteté: Mentirai-je à David?
Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
36 Sa postérité subsistera toujours; Son trône sera devant moi comme le soleil,
cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
37 Comme la lune il aura une éternelle durée. Le témoin qui est dans le ciel est fidèle. (Pause)
zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
38 Et pourtant, tu as rejeté, tu as repoussé! Tu t’es irrité contre ton oint!
Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
39 Tu as dédaigné l’alliance avec ton serviteur; Tu as abattu, profané sa couronne.
Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
40 Tu as détruit toutes ses murailles, Tu as mis en ruines ses forteresses.
Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
41 Tous les passants le dépouillent; Il est un objet d’opprobre pour ses voisins.
Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
42 Tu as élevé la droite de ses adversaires, Tu as réjoui tous ses ennemis;
Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
43 Tu as fait reculer le tranchant de son glaive, Et tu ne l’as pas soutenu dans le combat.
Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
44 Tu as mis un terme à sa splendeur, Et tu as jeté son trône à terre;
Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
45 Tu as abrégé les jours de sa jeunesse, Tu l’as couvert de honte. (Pause)
Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
46 Jusques à quand, Éternel! Te cacheras-tu sans cesse, Et ta fureur s’embrasera-t-elle comme le feu?
Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
47 Rappelle-toi ce qu’est la durée de ma vie, Et pour quel néant tu as créé tous les fils de l’homme.
Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
48 Y a-t-il un homme qui puisse vivre et ne pas voir la mort, Qui puisse sauver son âme du séjour des morts? (Pause) (Sheol h7585)
Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol h7585)
49 Où sont, Seigneur! Tes bontés premières, Que tu juras à David dans ta fidélité?
Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
50 Souviens-toi, Seigneur! De l’opprobre de tes serviteurs, Souviens-toi que je porte en mon sein tous les peuples nombreux;
Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
51 Souviens-toi des outrages de tes ennemis, ô Éternel! De leurs outrages contre les pas de ton oint.
zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
52 Béni soit à jamais l’Éternel! Amen! Amen!
Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!

< Psaumes 89 >