< Psaumes 7 >

1 Complainte de David. Chantée à l’Éternel, au sujet de Cusch, Benjamite. Éternel, mon Dieu! Je cherche en toi mon refuge; Sauve-moi de tous mes persécuteurs, et délivre-moi,
Wani shiggayiyon ta Dawuda, wanda Ya Rera wa Ubangiji game da Kush mutumin Benyamin. Ya Ubangiji Allahna, na zo neman mafaka a wurinka; ka cece ni ka kuɓutar da ni daga dukan waɗanda suke bi na,
2 Afin qu’ils ne me déchirent pas, comme un lion Qui dévore sans que personne vienne au secours.
in ba haka ba za su yayyage ni kamar zaki su ɓarke ni kucu-kucu ba tare da wani da zai cece ni ba.
3 Éternel, mon Dieu! Si j’ai fait cela, S’il y a de l’iniquité dans mes mains,
Ya Ubangiji Allahna, in na yi kuskure aka kuwa sami laifi a hannuwana,
4 Si j’ai rendu le mal à celui qui était paisible envers moi, Si j’ai dépouillé celui qui m’opprimait sans cause,
in na yi mugunta ga wanda yake zaman lafiya da ni ko kuwa ba da wani dalilin cuci abokin gābana,
5 Que l’ennemi me poursuive et m’atteigne, Qu’il foule à terre ma vie, Et qu’il couche ma gloire dans la poussière! (Pause)
to, bari abokin gābana yă bi yă kuma cim mini; bari yă tattake raina a ƙasa ya sa in kwana a ƙura. (Sela)
6 Lève-toi, ô Éternel! Dans ta colère, Lève-toi contre la fureur de mes adversaires, Réveille-toi pour me secourir, ordonne un jugement!
Ka tashi, ya Ubangiji, cikin fushinka; ka tashi gāba da fushin abokan gābana. Ka farka, Allahna, ka umarta adalci.
7 Que l’assemblée des peuples t’environne! Monte au-dessus d’elle vers les lieux élevés!
Bari taron mutane su taru kewaye da kai. Ka yi mulki a bisansu daga bisa;
8 L’Éternel juge les peuples: Rends-moi justice, ô Éternel! Selon mon droit et selon mon innocence!
bari Ubangiji mai shari’ar mutane. Ka shari’anta ni Ya Ubangiji, bisa ga adalcina, bisa ga mutuncina, ya Mafi Ɗaukaka.
9 Mets un terme à la malice des méchants, Et affermis le juste, Toi qui sondes les cœurs et les reins, Dieu juste!
Ya Allah mai adalci, wanda yake binciken tunani da zukata, ka kawo ƙarshen rikicin mugaye ka kuma sa adalai su zauna lafiya.
10 Mon bouclier est en Dieu, Qui sauve ceux dont le cœur est droit.
Garkuwata shi ne Allah Mafi Ɗaukaka, wanda yake ceton masu tsabtar zuciya.
11 Dieu est un juste juge, Dieu s’irrite en tout temps.
Allah alƙali ne mai adalci, Allahn da yakan bayyana fushinsa kowace rana.
12 Si le méchant ne se convertit pas, il aiguise son glaive, Il bande son arc, et il vise;
In mutum bai tuba ba, Allah zai wasa takobinsa; zai tanƙware yă kuma ɗaura bakansa.
13 Il dirige sur lui des traits meurtriers, Il rend ses flèches brûlantes.
Ya shirya makamansa masu dafi; ya shirya kibiyoyinsa masu wuta.
14 Voici, le méchant prépare le mal, Il conçoit l’iniquité, et il enfante le néant.
Wanda yake da cikin mugunta ya kuma ɗauki cikin damuwa yakan haifi ƙarya.
15 Il ouvre une fosse, il la creuse, Et il tombe dans la fosse qu’il a faite.
Wanda ya haƙa rami yakan fāɗa cikin ramin da ya haƙa.
16 Son iniquité retombe sur sa tête, Et sa violence redescend sur son front.
Damuwar da ya ja yakan sāke nannaɗe a kansa; fitinarsa takan sauka a kansa.
17 Je louerai l’Éternel à cause de sa justice, Je chanterai le nom de l’Éternel, du Très-Haut.
Zan gode wa Ubangiji saboda adalcinsa zan kuma rera yabo ga sunan Ubangiji Mafi Ɗaukaka.

< Psaumes 7 >