< Psaumes 20 >

1 Au chef des chantres. Psaume de David. Que l’Éternel t’exauce au jour de la détresse, Que le nom du Dieu de Jacob te protège!
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ubangiji ya amsa maka sa’ad da ka yi kira cikin wahala; bari sunan Allah na Yaƙub yă kiyaye ka.
2 Que du sanctuaire il t’envoie du secours, Que de Sion il te soutienne!
Bari yă aiko maka da taimako daga wuri mai tsarki yă kuma ba ka gudummawa daga Sihiyona.
3 Qu’il se souvienne de toutes tes offrandes, Et qu’il agrée tes holocaustes! (Pause)
Bari yă tuna da dukan sadakokinka yă kuma karɓi hadayunka na ƙonawa. (Sela)
4 Qu’il te donne ce que ton cœur désire, Et qu’il accomplisse tous tes desseins!
Bari yă biya maka bukatan ranka yă kuma sa dukan shirye-shiryenka su yi nasara.
5 Nous nous réjouirons de ton salut, Nous lèverons l’étendard au nom de notre Dieu; L’Éternel exaucera tous tes vœux.
Za mu yi sowa ta farin ciki sa’ad da ka yi nasara mu kuma ɗaga tutotinmu a cikin sunan Allahnmu. Bari Ubangiji yă biya maka dukan bukatunka.
6 Je sais déjà que l’Éternel sauve son oint; Il l’exaucera des cieux, de sa sainte demeure, Par le secours puissant de sa droite.
Yanzu na san cewa, Ubangiji yakan cece shafaffensa. Yakan amsa masa daga samansa mai tsarki da ikon ceto na hannun damansa.
7 Ceux-ci s’appuient sur leurs chars, ceux-là sur leurs chevaux; Nous, nous invoquons le nom de l’Éternel, notre Dieu.
Waɗansu sun dogara a kekunan yaƙi waɗansu kuma a dawakai, amma mu, mun dogara a cikin sunan Ubangiji Allahnmu.
8 Eux, ils plient, et ils tombent; Nous, nous tenons ferme, et restons debout.
Za a durƙusar da su, su kuma fāɗi, amma mu za mu tashi mu tsaya daram.
9 Éternel, sauve le roi! Qu’il nous exauce, quand nous l’invoquons!
Ya Ubangiji, ka ba da nasara ga sarki! Ka amsa mana sa’ad da muka yi kira!

< Psaumes 20 >