< Psaumes 104 >

1 Mon âme, bénis l’Éternel! Éternel, mon Dieu, tu es infiniment grand! Tu es revêtu d’éclat et de magnificence!
Yabi Ubangiji, ya raina. Ya Ubangiji Allahna, kana da girma ƙwarai; kana saye da daraja da ɗaukaka.
2 Il s’enveloppe de lumière comme d’un manteau; Il étend les cieux comme un pavillon.
Ubangiji ya naɗe kansa da haske kamar riga ya shimfiɗa sammai kamar tenti
3 Il forme avec les eaux le faîte de sa demeure; Il prend les nuées pour son char, Il s’avance sur les ailes du vent.
ya kafa ginshiƙan ɗakin samansa a kan ruwaye. Ya maido da gizagizai suka zama keken yaƙinsa yana hawa a kan fikafikan iska.
4 Il fait des vents ses messagers, Des flammes de feu ses serviteurs.
Ya mai da iska suka zama’yan saƙonsa harsunan wuta kuma bayinsa.
5 Il a établi la terre sur ses fondements, Elle ne sera jamais ébranlée.
Ya kafa duniya a kan tussanta; ba za a iya matsar da ita ba.
6 Tu l’avais couverte de l’abîme comme d’un vêtement, Les eaux s’arrêtaient sur les montagnes;
Ka rufe ta da zurfi kamar da riga ruwaye sun tsaya a bisa duwatsu.
7 Elles ont fui devant ta menace, Elles se sont précipitées à la voix de ton tonnerre.
Amma a tsawatawarka ruwaye suka gudu da jin ƙarar tsawanka suka ruga da gudu;
8 Des montagnes se sont élevées, des vallées se sont abaissées, Au lieu que tu leur avais fixé.
suka gudu a bisa duwatsu, suka gangara zuwa cikin kwaruruka, zuwa wurin da ka shirya musu.
9 Tu as posé une limite que les eaux ne doivent point franchir, Afin qu’elles ne reviennent plus couvrir la terre.
Ka kafa iyakar da ba a iya tsallakawa; ba za su ƙara rufe duniya ba.
10 Il conduit les sources dans des torrents Qui coulent entre les montagnes.
Ya sa maɓulɓulai suka zuba ruwa cikin kwaruruka; yana gudu tsakanin duwatsu.
11 Elles abreuvent tous les animaux des champs; Les ânes sauvages y étanchent leur soif.
Suna ba da ruwa ga dukan namun jeji; jakunan jeji suna kashe ƙishirwansu.
12 Les oiseaux du ciel habitent sur leurs bords, Et font résonner leur voix parmi les rameaux.
Tsuntsaye sarari suna sheƙunansu kusa da ruwan; suna rera cikin rassa.
13 De sa haute demeure, il arrose les montagnes; La terre est rassasiée du fruit de tes œuvres.
Yana wa duwatsu banruwa daga ɗakinsa na sama; ƙasa tana ƙoshiya da amfanin aikinsa.
14 Il fait germer l’herbe pour le bétail, Et les plantes pour les besoins de l’homme, Afin que la terre produise de la nourriture,
Yana sa ciyawa tă yi girma saboda shanu, tsire-tsire domin mutum ya nome, suna fid da abinci daga ƙasa,
15 Le vin qui réjouit le cœur de l’homme, Et fait plus que l’huile resplendir son visage, Et le pain qui soutient le cœur de l’homme.
ruwan inabi yakan sa zuciyar mutum tă yi murna, mai kuwa yakan sa fuska tă yi haske, abinci kuma da yake riƙe zuciyarsa.
16 Les arbres de l’Éternel se rassasient, Les cèdres du Liban, qu’il a plantés.
Ana yi wa itatuwan Ubangiji banruwa sosai, al’ul na Lebanon da ya shuka.
17 C’est là que les oiseaux font leurs nids; La cigogne a sa demeure dans les cyprès,
A can tsuntsaye suke sheƙunnansu; shamuwa tana da gidanta a itatuwan fir.
18 Les montagnes élevées sont pour les boucs sauvages, Les rochers servent de retraite aux damans.
Manyan duwatsu na awakin jeji ne; tsagaggun duwatsun mafaka ne ga rema.
19 Il a fait la lune pour marquer les temps; Le soleil sait quand il doit se coucher.
Wata ne ke ƙididdigar lokuta, rana kuma ta san sa’ad da za tă fāɗi.
20 Tu amènes les ténèbres, et il est nuit: Alors tous les animaux des forêts sont en mouvement;
Ka yi duhu, sai ya zama dare, sai dukan namun jeji a kurmi suka fito a maƙe.
21 Les lionceaux rugissent après la proie, Et demandent à Dieu leur nourriture.
Zakoki sun yi ruri sa’ad da suke farauta suna kuma neman abincinsu daga Allah.
22 Le soleil se lève: ils se retirent, Et se couchent dans leurs tanières.
Rana ta fito, sai suka koma shiru; suka koma suka kwanta a kogwanninsu.
23 L’homme sort pour se rendre à son ouvrage, Et à son travail, jusqu’au soir.
Mutum yakan tafi aikinsa, zuwa wurin aikinsa har yamma.
24 Que tes œuvres sont en grand nombre, ô Éternel! Tu les as toutes faites avec sagesse. La terre est remplie de tes biens.
Ina misalin yawan aikinka, ya Ubangiji! Cikin hikima ka yi su duka; duniya ta cika da halittunka.
25 Voici la grande et vaste mer: Là se meuvent sans nombre Des animaux petits et grands;
Akwai teku, babba da kuma fāɗi, cike da halittun da suka wuce ƙirga, abubuwa masu rai babba da ƙarami.
26 Là se promènent les navires, Et ce léviathan que tu as formé pour se jouer dans les flots.
A can jiragen ruwa suna kai komo, kuma dodon ruwan da ka yi, yă yi wasa a can.
27 Tous ces animaux espèrent en toi, Pour que tu leur donnes la nourriture en son temps.
Waɗannan duka suna dogara gare ka don ka ba su abincinsu a daidai lokaci.
28 Tu la leur donnes, et ils la recueillent; Tu ouvres ta main, et ils se rassasient de biens.
Sa’ad da ba su da shi, sai su tattara shi; sa’ad da ka buɗe hannunka, sukan ƙoshi da abubuwa masu kyau.
29 Tu caches ta face: ils sont tremblants; Tu leur retires le souffle: ils expirent, Et retournent dans leur poussière.
Sa’ad da ka ɓoye fuskarka, sai su razana; sa’ad da ka ɗauke numfashinsu, sai su mutu su kuma koma ga ƙura.
30 Tu envoies ton souffle: ils sont créés, Et tu renouvelles la face de la terre.
Sa’ad da ka aika da Ruhunka, sai su halittu, su kuma sabunta fuskar duniya.
31 Que la gloire de l’Éternel subsiste à jamais! Que l’Éternel se réjouisse de ses œuvres!
Bari ɗaukakar Ubangiji ta dawwama har abada; bari Ubangiji yă yi farin ciki cikin aikinsa,
32 Il regarde la terre, et elle tremble; Il touche les montagnes, et elles sont fumantes.
shi wanda ya dubi duniya, sai ta razana, wanda ya taɓa duwatsu, sai suka yi hayaƙi.
33 Je chanterai l’Éternel tant que je vivrai, Je célébrerai mon Dieu tant que j’existerai.
Zan rera ga Ubangiji dukan raina; zan rera yabo ga Allahna muddin ina raye.
34 Que mes paroles lui soient agréables! Je veux me réjouir en l’Éternel.
Bari tunanina yă gamshe shi, yayinda nake farin ciki a cikin Ubangiji.
35 Que les pécheurs disparaissent de la terre, Et que les méchants ne soient plus! Mon âme, bénis l’Éternel! Louez l’Éternel!
Amma bari masu zunubi su ɓace daga duniya mugaye kuma kada a ƙara ganinsu. Yabi Ubangiji, ya raina. Yabi Ubangiji.

< Psaumes 104 >