< Néhémie 11 >

1 Les chefs du peuple s’établirent à Jérusalem. Le reste du peuple tira au sort, pour qu’un sur dix vînt habiter Jérusalem, la ville sainte, et que les autres demeurassent dans les villes.
To, fa, shugabannin mutane suka zauna a Urushalima, sauran mutanen kuma suka jefa ƙuri’a don su kawo mutum ɗaya daga kowane mutum goma don su zauna a Urushalima, birni mai tsarki, yayinda sauran tara suka zauna a garuruwansu.
2 Le peuple bénit tous ceux qui consentirent volontairement à résider à Jérusalem.
Sai mutane suka yaba wa dukan mutanen da suka ba da kansu da yardar rai su zauna a Urushalima.
3 Voici les chefs de la province qui s’établirent à Jérusalem. Dans les villes de Juda, chacun s’établit dans sa propriété, dans sa ville, Israël, les sacrificateurs et les Lévites, les Néthiniens, et les fils des serviteurs de Salomon.
Waɗannan su ne shugabannin yankuna waɗanda suka zauna a Urushalima (ko da yake waɗansu Isra’ilawa, da firistoci, da Lawiyawa, da ma’aikatan haikali, da zuriyar bayin Solomon, suka yi zama a cikin garuruwan Yahuda, kowanne a mallakarsa cikin garuruwa dabam-dabam,
4 A Jérusalem s’établirent des fils de Juda et des fils de Benjamin. Des fils de Juda: Athaja, fils d’Ozias, fils de Zacharie, fils d’Amaria, fils de Schephathia, fils de Mahalaleel, des fils de Pérets,
yayinda sauran mutane daga Yahuda da Benyamin suka zauna a Urushalima). Daga zuriyar Yahuda akwai, Atahiya ɗan Uzziya, ɗan Zakariya, ɗan Amariya, ɗan Shefatiya, ɗan Mahalalel, wani zuriyar Ferez;
5 et Maaséja, fils de Baruc, fils de Col-Hozé, fils de Hazaja, fils d’Adaja, fils de Jojarib, fils de Zacharie, fils de Schiloni.
da Ma’asehiya ɗan Baruk, ɗan Kol-Hoze, ɗan Hazahiya, ɗan Adahiya, ɗan Yohiyarib, ɗan Zakariya, zuriyar Shela.
6 Total des fils de Pérets qui s’établirent à Jérusalem: quatre cent soixante-huit hommes vaillants.
Zuriyar Ferez waɗanda suka zauna a Urushalima sun kai ɗari huɗu da sittin da takwas, dukansu kuwa muhimman mutane ne.
7 Voici les fils de Benjamin: Sallu, fils de Meschullam, fils de Joëd, fils de Pedaja, fils de Kolaja, fils de Maaséja, fils d’Ithiel, fils d’Ésaïe,
Daga zuriyar Benyamin akwai, Sallu ɗan Meshullam, ɗan Yowed, ɗan Fedahiya, ɗan Kolahiya, ɗan Ma’asehiya, ɗan Itiyel, ɗan Yeshahiya,
8 et, après lui, Gabbaï et Sallaï, neuf cent vingt-huit.
da mabiyansa, Gabbai da Sallai, mutum 928.
9 Joël, fils de Zicri, était leur chef; et Juda, fils de Senua, était le second chef de la ville.
Yowel ɗan Zikri ne babban shugabansu, Yahuda kuma ɗan Hassenuwa, ya shugabanci Yanki na Biyu na birni.
10 Des sacrificateurs: Jedaeja, fils de Jojarib, Jakin,
Daga firistoci akwai, Yedahiya ɗan Yohiyarib, da Yakin,
11 Seraja, fils de Hilkija, fils de Meschullam, fils de Tsadok, fils de Merajoth, fils d’Achithub, prince de la maison de Dieu,
da Serahiya ɗan Hilkiya, ɗan Meshullam, ɗan Zadok, ɗan Merahiyot, ɗan Ahitub, mai lura da abubuwa a cikin gidan Allah,
12 et leurs frères occupés au service de la maison, huit cent vingt-deux; Adaja, fils de Jerocham, fils de Pelalia, fils d’Amtsi, fils de Zacharie, fils de Paschhur, fils de Malkija,
tare da’yan’uwansu waɗanda suke aiki domin haikali, su 822 ne. Akwai kuma Adahiya ɗan Yeroham, ɗan Felaliya, ɗan Amzi, ɗan Zakariya, ɗan Fashhur, ɗan Malkiya,
13 et ses frères, chefs des maisons paternelles, deux cent quarante-deux; et Amaschsaï, fils d’Azareel, fils d’Achzaï, fils de Meschillémoth, fils d’Immer,
da’yan’uwansa waɗanda suke shugabannin iyalai, su 242. Sai kuma Amashsai ɗan Azarel, ɗan Ahzai, ɗan Meshillemot, ɗan Immer,
14 et leurs frères, vaillants hommes, cent vingt-huit. Zabdiel, fils de Guedolim, était leur chef.
da’yan’uwansa, su 128 ne muhimman mutane. Babban shugabansu shi ne Zabdiyel ɗan Haggedolim.
15 Des Lévites: Schemaeja, fils de Haschub, fils d’Azrikam, fils de Haschabia, fils de Bunni,
Daga Lawiyawa kuwa akwai, Shemahiya ɗan Hasshub, ɗan Azrikam, ɗan Hashabiya, ɗan Bunni,
16 Schabbethaï et Jozabad, chargés des affaires extérieures de la maison de Dieu, et faisant partie des chefs des Lévites;
da Shabbetai, da kuma Yozabad, biyu cikin shugabanni Lawiyawa waɗanda suke da nawayar aiki waje da gidan Allah.
17 Matthania, fils de Michée, fils de Zabdi, fils d’Asaph, le chef qui entonnait la louange à la prière, et Bakbukia, le second parmi ses frères, et Abda, fils de Schammua, fils de Galal, fils de Jeduthun.
Sai kuma Mattaniya ɗan Mika, ɗan Zabdi, ɗan Asaf, shugaban da yake bi da hidimar godiya da kuma addu’a. Sai Bakbukiya, na biyu a cikin’yan’uwansa; da Abda ɗan Shammuwa, ɗan Galal, ɗan Yedutun.
18 Total des Lévites dans la ville sainte: deux cent quatre-vingt-quatre.
Lawiyawan da suke cikin birni mai tsarki sun kai 284.
19 Et les portiers: Akkub, Thalmon, et leurs frères, gardiens des portes, cent soixante-douze.
Matsaran ƙofofi kuwa su ne, Akkub, da Talmon, da’yan’uwansu waɗanda suke tsaron ƙofofi, su 172 ne.
20 Le reste d’Israël, les sacrificateurs, les Lévites, s’établirent dans toutes les villes de Juda, chacun dans sa propriété.
Sauran Isra’ilawa tare da firistoci, da Lawiyawa sun kasance a dukan garuruwan Yahuda, kowanne a mallakar kakansa.
21 Les Néthiniens s’établirent sur la colline, et ils avaient pour chefs Tsicha et Guischpa.
Ma’aikatan haikali sun zauna a kan tudun Ofel. Ziha, da Gishfa ne suke lura da su.
22 Le chef des Lévites à Jérusalem était Uzzi, fils de Bani, fils de Haschabia, fils de Matthania, fils de Michée, d’entre les fils d’Asaph, les chantres chargés des offices de la maison de Dieu;
Babban shugaban Lawiyawa a Urushalima shi ne Uzzi ɗan Bani, ɗan Hashabiya, ɗan Mattaniya, ɗan Mika. Uzzi yana ɗaya daga zuriyar Asaf, waɗanda suke mawaƙan da suke da nawayar hidima a gidan Allah.
23 car il y avait un ordre du roi concernant les chantres, et un salaire fixe leur était accordé pour chaque jour.
Mawaƙa sun bi umarnan sarki, a kan abin da za su yi kowace rana.
24 Pethachja, fils de Meschézabeel, des fils de Zérach, fils de Juda, était commissaire du roi pour toutes les affaires du peuple.
Fetahahiya ɗan Meshezabel, ɗaya daga zuriyar Zera ɗan Yahuda ne, wakilin sarki cikin dukan al’amuran da suka shafi mutane.
25 Dans les villages et leurs territoires, des fils de Juda s’établirent à Kirjath-Arba et dans les lieux de son ressort, à Dibon et dans les lieux de son ressort, à Jekabtseel et dans les villages de son ressort,
Game da ƙauyukan da filayensu, waɗansu mutanen Yahuda suka zauna a Kiriyat Arba da ƙauyukanta, da Dibon da ƙauyukanta, da Yekabzeyel da ƙauyukanta.
26 à Jéschua, à Molada, à Beth-Paleth,
Akwai su kuma a Yeshuwa, da Molada, da Bet-Felet,
27 à Hatsar-Schual, à Beer-Schéba, et dans les lieux de son ressort,
da Hazar Shuwal, da Beyersheba da ƙauyukanta.
28 à Tsiklag, à Mecona et dans les lieux de son ressort,
Akwai su a Ziklag, da Mekona da ƙauyukanta.
29 à En-Rimmon, à Tsorea, à Jarmuth,
Suna nan kuma a En Rimmon, da Zora, da Yarmut,
30 à Zanoach, à Adullam, et dans les villages de leur ressort, à Lakis et dans son territoire, à Azéka et dans les lieux de son ressort. Ils s’établirent depuis Beer-Schéba jusqu’à la vallée de Hinnom.
da Zanowa, da Adullam da ƙauyukansu, da Lakish da gonakinta, da kuma Azeka da ƙauyukanta. Saboda haka sun yi zama tun daga Beyersheba har zuwa Kwarin Hinnom.
31 Les fils de Benjamin s’établirent, depuis Guéba, à Micmasch, à Ajja, à Béthel et dans les lieux de son ressort,
Zuriyar mutanen Benyamin daga Geba sun zauna a Mikmash, da Aiya, da Betel da ƙauyukanta,
32 à Anathoth, à Nob, à Hanania,
da Anatot, da Nob, da Ananiya,
33 à Hatsor, à Rama, à Guitthaïm,
da Hazor, da Rama, da Gittayim,
34 à Hadid, à Tseboïm, à Neballath,
da Hadid, da Zeboyim, da Neballat,
35 à Lod et à Ono, la vallée des ouvriers.
da Lod, da Ono, da kuma a Kwarin Masu sana’a.
36 Il y eut des Lévites qui se joignirent à Benjamin, quoique appartenant aux divisions de Juda.
Waɗansu gundumomin Lawiyawan Yahuda sun zauna a Benyamin.

< Néhémie 11 >