< Job 36 >

1 Élihu continua et dit:
Elihu ya ci gaba,
2 Attends un peu, et je vais poursuivre, Car j’ai des paroles encore pour la cause de Dieu.
“Ka ɗan ƙara haƙuri da ni kaɗan, zan kuma nuna maka cewa akwai sauran abubuwan da zan faɗa a madadin Allah.
3 Je prendrai mes raisons de haut, Et je prouverai la justice de mon créateur.
Daga nesa na sami sanina; zan nuna cewa Mahaliccina shi mai gaskiya ne.
4 Sois-en sûr, mes discours ne sont pas des mensonges, Mes sentiments devant toi sont sincères.
Abin da zan gaya maka ba ƙarya ba ne; mai cikakken sani yana tare da kai.
5 Dieu est puissant, mais il ne rejette personne; Il est puissant par la force de son intelligence.
“Allah mai iko ne, amma ba ya rena mutane; shi mai girma ne cikin manufarsa.
6 Il ne laisse pas vivre le méchant, Et il fait droit aux malheureux.
Ba ya barin mugaye da rai sai dai yana ba waɗanda ake tsanantawa hakkinsu.
7 Il ne détourne pas les yeux de dessus les justes, Il les place sur le trône avec les rois, Il les y fait asseoir pour toujours, afin qu’ils soient élevés.
Ba ya fasa duban masu adalci; yana sa su tare da sarakuna yana ɗaukaka su har abada.
8 Viennent-ils à tomber dans les chaînes, Sont-ils pris dans les liens de l’adversité,
Amma in mutane suna daure da sarƙoƙi, ƙunci kuma ya daure su,
9 Il leur dénonce leurs œuvres, Leurs transgressions, leur orgueil;
yana gaya musu abin da suka yi, cewa sun yi zunubi da girman kai.
10 Il les avertit pour leur instruction, Il les exhorte à se détourner de l’iniquité.
Yana sa su saurari gyara yă kuma umarce su su tuba daga muguntarsu.
11 S’ils écoutent et se soumettent, Ils achèvent leurs jours dans le bonheur, Leurs années dans la joie.
In sun yi biyayya suka bauta masa, za su yi rayuwa dukan kwanakinsu cikin wadata shekarunsu kuma cikin kwanciyar zuciya.
12 S’ils n’écoutent pas, ils périssent par le glaive, Ils expirent dans leur aveuglement.
Amma in ba su saurara ba, za su hallaka da takobi kuma za su mutu ba ilimi.
13 Les impies se livrent à la colère, Ils ne crient pas à Dieu quand il les enchaîne;
“Waɗanda ba su da Allah a zuciyarsu su ne suke riƙe fushi; ko sa’ad da ya ba su horo, ba su neman taimakonsa.
14 Ils perdent la vie dans leur jeunesse, Ils meurent comme les débauchés.
Suna mutuwa tun suna matasa, cikin ƙazamar rayuwar karuwanci.
15 Mais Dieu sauve le malheureux dans sa misère, Et c’est par la souffrance qu’il l’avertit.
Amma yana kuɓutar da masu wahala; yana magana da su cikin wahalarsu.
16 Il te retirera aussi de la détresse, Pour te mettre au large, en pleine liberté, Et ta table sera chargée de mets succulents.
“Yana so yă rinjaye ka daga haƙoran ƙunci, zuwa wuri mai sauƙi inda ba matsi zuwa teburinka cike da abincin da kake so.
17 Mais si tu défends ta cause comme un impie, Le châtiment est inséparable de ta cause.
Amma yanzu an cika ka da hukuncin da ya kamata a yi wa mugaye; shari’a da kuma gaskiya sun kama ka.
18 Que l’irritation ne t’entraîne pas à la moquerie, Et que la grandeur de la rançon ne te fasse pas dévier!
Ka yi hankali kada wani yă ruɗe ka da arziki; kada ka bar toshiya ta sa ka juya.
19 Tes cris suffiraient-ils pour te sortir d’angoisse, Et même toutes les forces que tu pourrais déployer?
Dukiyarka ko dukan yawan ƙoƙarinka sun isa su riƙe ka su hana ka shan ƙunci?
20 Ne soupire pas après la nuit, Qui enlève les peuples de leur place.
Kada ka yi marmari dare yă yi, don a fitar da mutane daga gidajensu.
21 Garde-toi de te livrer au mal, Car la souffrance t’y dispose.
Ka kula kada ka juya ga mugunta, abin da ka fi so fiye da wahala.
22 Dieu est grand par sa puissance; Qui saurait enseigner comme lui?
“An ɗaukaka Allah cikin ikonsa. Wane ne malami kamar sa?
23 Qui lui prescrit ses voies? Qui ose dire: Tu fais mal?
Wane ne ya nuna masa hanyar da zai bi, ko kuma wane ne ya ce masa, ‘Ba ka yi daidai ba?’
24 Souviens-toi d’exalter ses œuvres, Que célèbrent tous les hommes.
Ka tuna ka ɗaukaka aikinsa, waɗanda mutane suka yaba a cikin waƙa.
25 Tout homme les contemple, Chacun les voit de loin.
Dukan’yan adam sun gani; mutane sun hanga daga nesa.
26 Dieu est grand, mais sa grandeur nous échappe, Le nombre de ses années est impénétrable.
Allah mai girma ne, ya wuce ganewarmu! Yawan shekarunsa ba su bincikuwa.
27 Il attire à lui les gouttes d’eau, Il les réduit en vapeur et forme la pluie;
“Yana sa ruwa yă zama tururi yă zubo daga sama.
28 Les nuages la laissent couler, Ils la répandent sur la foule des hommes.
Gizagizai suna zubo da raɓarsu kuma ruwan sama yana zubowa’yan adam a wadace.
29 Et qui comprendra le déchirement de la nuée, Le fracas de sa tente?
Wane ne zai iya gane yadda ya shimfiɗa gizagizai yadda yake tsawa daga wurin zamansa?
30 Voici, il étend autour de lui sa lumière, Et il se cache jusque dans les profondeurs de la mer.
Dubi yadda ya baza walƙiyarsa kewaye da shi, tana haskaka zurfin teku.
31 Par ces moyens il juge les peuples, Et il donne la nourriture avec abondance.
Haka yake mulkin al’ummai yana kuma tanada abinci a wadace.
32 Il prend la lumière dans sa main, Il la dirige sur ses adversaires.
Yana cika hannuwansa da walƙiya kuma yana ba ta umarni tă fāɗi a inda ya yi nufi.
33 Il s’annonce par un grondement; Les troupeaux pressentent son approche.
Tsawarsa tana nuna cewa babbar iska da ruwa suna zuwa; ko shanu sun san da zuwansa.

< Job 36 >