< Job 26 >

1 Job prit la parole et dit:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Comme tu sais bien venir en aide à la faiblesse! Comme tu prêtes secours au bras sans force!
“Yadda ka taimaki marar ƙarfi! Yadda ka ceci marar ƙarfi!
3 Quels bons conseils tu donnes à celui qui manque d’intelligence! Quelle abondance de sagesse tu fais paraître!
Ka ba marar hikima shawara! Ka nuna kana da ilimi sosai.
4 A qui s’adressent tes paroles? Et qui est-ce qui t’inspire?
Wane ne ya taimake ka ka yi waɗannan maganganu? Kuma ruhun wane ne ya yi magana ta bakinka?
5 Devant Dieu les ombres tremblent Au-dessous des eaux et de leurs habitants;
“Matattu suna cikin azaba, waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukan mazauna cikin ruwaye.
6 Devant lui le séjour des morts est nu, L’abîme n’a point de voile. (Sheol h7585)
Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe. (Sheol h7585)
7 Il étend le septentrion sur le vide, Il suspend la terre sur le néant.
Ya shimfiɗa arewancin sararin sama a sarari; ya rataye duniya ba a jikin wani abu ba.
8 Il renferme les eaux dans ses nuages, Et les nuages n’éclatent pas sous leur poids.
Ya naɗe ruwaye a cikin gizagizansa, duk da haka girgijen bai yage saboda nauyi ba.
9 Il couvre la face de son trône, Il répand sur lui sa nuée.
Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa gizagizai a kan shi,
10 Il a tracé un cercle à la surface des eaux, Comme limite entre la lumière et les ténèbres.
ya zāna iyakar fuskar ruwa a kan iyakar da take tsakanin duhu da haske.
11 Les colonnes du ciel s’ébranlent, Et s’étonnent à sa menace.
Madogaran sama sun girgiza, saboda tsawatawarsa.
12 Par sa force il soulève la mer, Par son intelligence il en brise l’orgueil.
Da ikonsa ya kwantar da teku; da hikimarsa ya hallaka dodon ruwan nan Rahab.
13 Son souffle donne au ciel la sérénité, Sa main transperce le serpent fuyard.
Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi kyau da hannunsa ya soke macijin nan mai gudu.
14 Ce sont là les bords de ses voies, C’est le bruit léger qui nous en parvient; Mais qui entendra le tonnerre de sa puissance?
Waɗannan kaɗan ke nan daga cikin ayyukansa masu yawa. Kaɗan kawai muke ji game da shi! Wane ne kuwa yake iya gane tsawar ikonsa?”

< Job 26 >