< Ézéchiel 11 >

1 L’esprit m’enleva, et me transporta à la porte orientale de la maison de l’Éternel, à celle qui regarde l’orient. Et voici, à l’entrée de la porte, il y avait vingt-cinq hommes; et je vis au milieu d’eux Jaazania, fils d’Azzur, et Pelathia, fils de Benaja, chefs du peuple.
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni ƙofar gidan Ubangiji wadda take fuskantar gabas. Can a mashigi zuwa ƙofar akwai mutum ashirin da biyar, na kuma ga a cikinsu akwai Ya’azaniya ɗan Azzur da Felatiya ɗan Benahiya, shugabannin jama’a.
2 Et l’Éternel me dit: Fils de l’homme, ce sont les hommes qui méditent l’iniquité, et qui donnent de mauvais conseils dans cette ville.
Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan su ne mutanen da suke ƙulla mugunta suna kuma ba da muguwa shawara a cikin wannan birni.
3 Ils disent: Ce n’est pas le moment! Bâtissons des maisons! La ville est la chaudière, et nous sommes la viande.
Suna cewa, ‘Lokaci bai yi kusa da za a gina gidaje ba? Wannan birni yana tukunyar dahuwa, mu ne kuwa naman.’
4 C’est pourquoi prophétise contre eux, prophétise, fils de l’homme!
Saboda haka yi annabci a kansu; yi annabci, ɗan mutum.”
5 Alors l’esprit de l’Éternel tomba sur moi. Et il me dit: Dis: Ainsi parle l’Éternel: Vous parlez de la sorte, maison d’Israël! Et ce qui vous monte à la pensée, je le sais.
Sai Ruhun Ubangiji ya sauko a kaina, ya kuma faɗa mini in ce, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, haka kuke cewa, ya gidan Isra’ila, amma na san abin da yake a zuciyarku.
6 Vous avez multiplié les meurtres dans cette ville, Vous avez rempli les rues de cadavres.
Kun kashe mutane da yawa a wannan birni kuka kuma cika titunanta da gawawwaki.
7 C’est pourquoi ainsi parle le Seigneur, l’Éternel: Vos morts que vous avez étendus au milieu d’elle, C’est la viande, et elle, c’est la chaudière; Mais vous, on vous en fera sortir.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa gawawwakin da kuka zubar a can su ne naman, wannan birni kuwa ita ce tukunya, amma zan kore ku daga cikinta.
8 Vous avez peur de l’épée, Et je ferai venir sur vous l’épée, Dit le Seigneur, l’Éternel.
Kuna jin tsoron takobi, kuma takobi ne zan kawo muku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Je vous ferai sortir du milieu d’elle, Je vous livrerai entre les mains des étrangers, Et j’exercerai contre vous mes jugements.
Zan kore ku daga birnin in miƙa ku a hannuwan baƙi in kuma azabtar da ku.
10 Vous tomberez par l’épée, Je vous jugerai sur la frontière d’Israël, Et vous saurez que je suis l’Éternel.
Za ku mutu ta wurin takobi, zan kuma hukunta ku a iyakokin Isra’ila. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
11 La ville ne sera pas pour vous une chaudière, Et vous ne serez pas la viande au milieu d’elle: C’est sur la frontière d’Israël que je vous jugerai.
Wannan birni ba za tă zama muku tukunya ba, ba kuwa za ku zama nama a cikinta ba; zan hukunta ku a iyakokin Isra’ila.
12 Et vous saurez que je suis l’Éternel, Dont vous n’avez pas suivi les ordonnances Et pratiqué les lois; Mais vous avez agi selon les lois des nations qui vous entourent.
Za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji, gama ba ku bi ƙa’idodina ba balle ku kiyaye dokokina, amma kuka bi hanyoyin al’ummai kewaye da ku.”
13 Comme je prophétisais, Pelathia, fils de Benaja, mourut. Je tombai sur ma face, et je m’écriai à haute voix: Ah! Seigneur Éternel, anéantiras-tu ce qui reste d’Israël?
Yanzu yayinda nake yin annabci, sai Felatiya ɗan Benahiya ya mutu. Sai na fāɗi rubda ciki na kuma yi kuka da babbar murya na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Za ka hallaka raguwar Isra’ila ƙaƙaf ne?”
14 Et la parole de l’Éternel me fut adressée, en ces mots:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
15 Fils de l’homme, ce sont tes frères, tes frères, Ceux de ta parenté, et la maison d’Israël tout entière, A qui les habitants de Jérusalem disent: Restez loin de l’Éternel, Le pays nous a été donné en propriété.
“Ɗan mutum,’yan’uwanka,’yan’uwanka waɗanda suke danginka na cikinka da kuma dukan gidan Isra’ila su ne waɗanda mutanen Urushalima suka ce, ‘Su ne da nisa daga Ubangiji; an ba mu wannan ƙasa ta zama mallakarmu.’
16 C’est pourquoi tu diras: Ainsi parle le Seigneur, l’Éternel: Si je les tiens éloignés parmi les nations, Si je les ai dispersés en divers pays, Je serai pour eux quelque temps un asile Dans les pays où ils sont venus.
“Saboda haka ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ko da yake na kore su zuwa cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe, duk da haka na zama wuri mai tsarki a gare su a ƙasashen da suka tafi.’
17 C’est pourquoi tu diras: Ainsi parle le Seigneur, l’Éternel: Je vous rassemblerai du milieu des peuples, Je vous recueillerai des pays où vous êtes dispersés, Et je vous donnerai la terre d’Israël.
“Saboda haka, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan tattaro ku daga al’ummai in kuma dawo da ku daga ƙasashen da aka warwatsa ku, zan kuwa sāke mayar muku da ƙasar Isra’ila.’
18 C’est là qu’ils iront, Et ils en ôteront toutes les idoles et toutes les abominations.
“Za su dawo gare ta su kawar da dukan mugayen siffofi da gumaka masu banƙyama.
19 Je leur donnerai un même cœur, Et je mettrai en vous un esprit nouveau; J’ôterai de leur corps le cœur de pierre, Et je leur donnerai un cœur de chair,
Zan ba su zuciya ɗaya in kuma sa sabon ruhu a cikinsu; zan fid da zuciyar dutse daga gare su in kuma ba su zuciya ta nama.
20 Afin qu’ils suivent mes ordonnances, Et qu’ils observent et pratiquent mes lois; Et ils seront mon peuple, et je serai leur Dieu.
Sa’an nan za su bi ƙa’idodina su kuma yi hankali ga kiyaye dokokina. Za su zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnsu.
21 Mais pour ceux dont le cœur se plaît à leurs idoles et à leurs abominations, Je ferai retomber leurs œuvres sur leur tête, Dit le Seigneur, l’Éternel.
Amma game da waɗanda zukatansu suka karkata ga bin mugayen siffofi da gumakan banƙyama, zan sāka musu gwargwadon ayyukansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
22 Les chérubins déployèrent leurs ailes, accompagnés des roues; et la gloire du Dieu d’Israël était sur eux, en haut.
Sa’an nan kerubobi, tare da da’irori kusa da su, suka buɗe fikafikansu, ɗaukakar Allah kuwa tana a bisansu.
23 La gloire de l’Éternel s’éleva du milieu de la ville, et elle se plaça sur la montagne qui est à l’orient de la ville.
Ɗaukakar Ubangiji ta haura daga cikin birnin ta sauka a bisa dutse gabas da shi.
24 L’esprit m’enleva, et me transporta en Chaldée auprès des captifs, en vision par l’esprit de Dieu; et la vision que j’avais eue disparut au-dessus de moi.
Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma kawo ni ga masu zaman bauta a ƙasar Babilon cikin wahayin da Ruhun Allah ya bayar. Sa’an nan wahayin da na gani ya rabu da ni,
25 Je dis aux captifs toutes les paroles de l’Éternel, qu’il m’avait révélées.
na kuwa faɗa wa masu zaman bautan dukan abin da Ubangiji ya nuna mini.

< Ézéchiel 11 >