< Psaumes 147 >

1 Alléluiah. Psaume d'Aggée et de Zacharie. Louez le Seigneur, car le chant d'un psaume lui est agréable; puissent nos louanges être agréables à notre Dieu!
Yabi Ubangiji. Yana da kyau a rera yabai ga Allahnmu, abu mai daɗi ne daidai ne kuma a yabe shi!
2 C'est le Seigneur qui a bâti Jérusalem; il rassemblera les membres dispersés d'Israël.
Ubangiji ya gina Urushalima; ya tattara kamammu na Isra’ilan da aka kai bauta.
3 Il guérit les hommes contrits en leur cœur; il bande leurs plaie.
Ya warkar da masu raunanar zuciya ya ɗaɗɗaura miyakunsu.
4 Il dénombre la multitude des étoiles, et toutes, il les appelle par leur nom.
Ya lissafta yawan taurari ya kuma kira kowannensu da suna.
5 Notre Seigneur est grand; sa force est grande, et son intelligence infinie.
Shugabanmu mai girma ne mai iko duka; ganewarsa ba shi da iyaka.
6 Le Seigneur élève les doux; il humilie jusqu'à terre les pécheurs.
Ubangiji yana kula da masu sauƙinkai yakan yar da mugaye a ƙasa.
7 Entonnez des chants de gloire au Seigneur; chantez des psaumes à notre Dieu sur la cithare.
Rera wa Ubangiji waƙar godiya; ku kada garaya ga Allahnmu.
8 C'est lui qui revêt le ciel de nuages, lui qui prépare de la pluie pour la terre; lui qui fait naître de l'herbe dans les montagnes, et du fourrage pour le service de l'homme.
Ya rufe sararin sama da gizagizai; yana tanada wa duniya ruwan sama yana kuma sa ciyawa tă yi girma a kan tuddai.
9 Il donne la pâture aux bêtes et aux petits des corbeaux qui l'invoquent.
Yakan tanada wa shanu abinci da kuma saboda’ya’yan hankaki sa’ad da suka yi kira.
10 Il ne veut pas qu'on se complaise dans la force du cheval, ni que l'on se confie dans les jarrets de l'homme.
Jin daɗinsa ba ya a ƙarfin doki, balle farin cikinsa yă kasance a ƙafafun mutum;
11 Le Seigneur se complaît en ceux qui le craignent, et en tous ceux qui espèrent en sa miséricorde.
Ubangiji yakan yi farin ciki a waɗanda suke tsoronsa, waɗanda suke sa zuciya a ƙaunarsa marar ƙarewa.
12 Alléluiah. Psaume d'Aggée et de Zacharie. Jérusalem, loue de concert le Seigneur; ô Sion, loue ton Dieu.
Ki ɗaukaka Ubangiji, ya Urushalima; ki yabi Allahnki, ya Sihiyona.
13 Car il a fortifié les verrous de tes portes; il a béni les fils dans ton enceinte.
Gama yana ƙarfafa ƙyamaren ƙofofinki yana kuma albarkace mutanenki a cikinki.
14 C'est lui qui a établi la paix sur tes frontières, et qui te rassasie de fleur de froment;
Yana ba da salama ga iyakokinki yana kuma ƙosar da ke da alkama mafi kyau.
15 Lui qui envoie sa parole à la terre, et sa voix court avec rapidité;
Yana ba da umarninsa ga duniya; maganarsa tana tafiya da sauri.
16 Lui qui couvre la terre de neige comme d'une toison, et verse des brouillards comme de la cendre;
Yana shimfiɗa ƙanƙara kamar ulu yă kuma watsar da hazo kamar toka.
17 Lui qui produit la glace comme des morceaux de pain: qui alors peut supporter la rigueur de la froidure?
Yana zuba ƙanƙara kamar ƙananan duwatsu. Wa zai iya jure wa sanyin da ya aiko?
18 Il enverra sa parole, et la glace fondra; il exhalera son souffle, et les eaux couleront.
Yakan aiki maganarsa ta kuwa narkar da su; yakan tā da iskarsa, ruwaye kuwa su gudu.
19 C'est lui qui annonce sa parole à Jacob, ses ordonnances et ses jugements à Israël.
Ya bayyana maganarsa ga Yaƙub, dokokinsa da ƙa’idodinsa ga Isra’ila.
20 Il n'a point fait de même pour toutes les nations, et il ne leur a pas révélé ses commandements.
Bai yi wannan ga wata al’umma ba; ba su san dokokinsa ba. Yabi Ubangiji.

< Psaumes 147 >