< Psaumes 106 >

1 Alléluiah! Rendez grâces au Seigneur, parce qu'il est bon, parce que sa miséricorde est éternelle.
Yabi Ubangiji. Yi godiya ga Ubangiji, gama nagari ne shi; ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.
2 Qui dira la puissance du Seigneur, qui fera entendre toutes ses louanges?
Wane ne zai furta manyan ayyukan Ubangiji ko yă furta cikakken yabonsa?
3 Heureux ceux qui gardent ses jugements et qui font justice en tout temps!
Masu albarka ne waɗanda suke yin adalci, waɗanda kullum suke yin abin da yake daidai.
4 Souviens-toi de nous, Seigneur, avec ta bonté pour ton peuple; visite- nous avec ton salut;
Ka tuna da ni, ya Ubangiji, sa’ad da ka nuna alheri ga mutanenka, ka zo ka taimake ni sa’ad da ka cece su,
5 Afin que nous puissions avoir part aux biens de tes élus, nous réjouir de la joie de ton peuple, te glorifier avec ceux de ton héritage.
don in ji daɗin nasarar zaɓaɓɓunka, don in sami rabo cikin farin cikin al’ummarka in kuma shiga gādonka cikin yin yabo.
6 Nous avons péché avec nos pères, nous avons violé ta loi, nous avons commis l'iniquité.
Mun yi zunubi, kamar yadda kakanninmu suka yi; mun yi ba daidai ba muka kuma aikata mugunta.
7 Nos pères en Egypte ne comprirent point tes prodiges, et ils ne se souvinrent pas de l'abondance de ta miséricorde; et ils te provoquèrent, en arrivant à la mer Rouge.
Sa’ad da kakanninmu suke a Masar, ba su damu da mu’ujizanka ba; ba su tuna yawan alheranka ba, suka kuma yi tayarwa a teku, Jan Teku.
8 Et il les sauva pour la gloire de son nom, et pour manifester sa puissance.
Duk da haka ya cece su saboda sunansa, don yă sanar da ikonsa mai girma.
9 Et il menaça la mer Rouge, et elle fut desséchée; et il les ramena dans l'abîme, comme dans le désert.
Ya tsawata wa Jan Teku, ya kuwa bushe; ya bi da su ta cikin zurfafa sai ka ce a hamada.
10 Et il les sauva des mains de ceux qui les haïssaient, et il les racheta de la main de l'ennemi.
Ya cece su daga hannun maƙiyi; daga hannun abokin gāba ya fanshe su.
11 L'eau couvrit ceux qui les opprimaient, et pas un d'eux n'échappa.
Ruwaye suka rufe abokan gābansu; babu ko ɗaya da ya tsira.
12 Et ils eurent foi en ses paroles, et ils chantèrent ses louanges.
Sa’an nan suka gaskata alkawarinsa suka kuma rera yabonsa.
13 Mais ils oublièrent bien vite ses œuvres; ils n'attendirent point son conseil.
Amma nan da nan suka manta abin da ya yi ba su kuwa jira shawararsa ba.
14 Et ils furent pris de concupiscence dans la solitude, et ils tentèrent Dieu dans le désert sans eau.
A cikin hamada suka bar sha’awarsu ta mamaye su a ƙasar da babu kome suka gwada Allah.
15 Et il leur accorda ce qu'ils demandaient, et il envoya la satiété dans leur âme.
Sai ya ba su abin da suka roƙa, amma ya aika musu da muguwar cuta.
16 Et ils irritèrent Moïse dans le camp, et Aaron le saint du Seigneur.
A sansani suka ji kishin Musa da kuma Haruna, wanda Ubangiji ya keɓe.
17 La terre s'ouvrit, et elle engloutit Dathan, et engouffra le rassemblement d'Abiron.
Ƙasa ta buɗe ta haɗiye Datan ta binne iyalin Abiram.
18 Et la flamme dévora leur synagogue, et le feu consuma les pécheurs.
Wuta ta ƙuno a cikin mabiyansu; harshen wuta ya cinye mugaye.
19 Et ils se firent un veau en Choreb, et ils adorèrent une image sculptée.
A Horeb suka yi ɗan maraƙi suka yi wa gunkin zubi daga ƙarfe sujada.
20 Et ils échangèrent leur gloire contre la statue d'un veau qui se repaît de fourrage.
Suka sauke Ɗaukakarsu saboda siffar bijimi, wanda yake cin ciyawa.
21 Ils oublièrent le Dieu qui les avait sauvés, qui avait fait de grandes choses en Egypte,
Suka manta da Allahn da ya cece su, wanda ya aikata manyan abubuwa a Masar,
22 Des prodiges en la terre de Cham, et des actions terribles sur la mer Rouge.
mu’ujizai a ƙasar Ham ayyukan banrazana a Jan Teku.
23 Et il dit qu'il les exterminerait, si Moïse, son élu, ne s'était placé devant lui, et n'eût brisé l'idole, pour détourner sa fureur et l'empêcher de les détruire.
Don haka ya ce zai hallaka su, amma Musa, zaɓaɓɓensa, ya yi godo a gabansa don yă kau da hasalarsa daga hallaka su.
24 Et ils méprisèrent comme rien la terre désirable, et n'eurent point foi en la parole de Dieu.
Sai suka rena ƙasa mai ni’ima; ba su gaskata alkawarinsa ba.
25 Et ils murmurèrent sous leurs tentes, et n'écoutèrent point la voix du Seigneur!
Suka yi gunaguni a tentunansu ba su kuwa yi biyayya da Ubangiji ba.
26 Et il leva la main sur eux pour les abattre dans le désert,
Saboda haka ya rantse musu ya kuma ɗaga hannu cewa zai sa su mutu a cikin hamada,
27 Et pour rejeter leur race parmi les nations, et les disperser en diverses régions.
ya sa zuriyarsu su mutu a cikin al’ummai ya kuma watsar da su cikin dukan ƙasashe.
28 Et ils se prostituèrent à Belphégor, et ils mangèrent des victimes sacrifiées aux morts.
Suka haɗa kai da Ba’al-Feyor suka kuma ci hadayun da aka miƙa wa allolin da ba su da rai;
29 Et ils irritèrent Dieu par leurs désordres, et la ruine se multiplia chez eux.
suka tsokane Ubangiji ya yi fushi ta wurin mugayen ayyukansu, sai annoba ta ɓarke a cikinsu.
30 Et Phinéès se leva, et il apaisa le Seigneur, et la plaie cessa.
Amma Finehas ya miƙe tsaye ya ɗauki mataki, sai annobar ta daina.
31 Et cela lui fut imputé à justice, de génération en génération, dans tous les siècles.
An ayana masa wannan a matsayin adalci har zamanai marar matuƙa masu zuwa.
32 Et ils irritèrent Dieu vers les eaux de contradiction, et Moïse eut à souffrir de leur part;
A ruwan Meriba suka ba Ubangiji fushi, sai wahala ta zo wa Musa saboda su;
33 Parce qu'ils avaient rempli son esprit d'une amertume qui s'échappa de ses lèvres.
saboda sun yi tayarwa a kan Ruhun Allah, har mugayen kalmomi suka fito daga leɓunan Musa.
34 Ils n'exterminèrent point les nations, comme le Seigneur le leur avait dit;
Ba su hallakar da mutanen yadda Ubangiji ya umarce su ba,
35 Et ils se mêlèrent aux Gentils, et ils apprirent leurs œuvres,
amma suka yi cuɗanya da al’ummai suka ɗauki al’adunsu.
36 Et ils servirent leurs idoles, et ce fut pour eux un sujet de chute.
Suka yi wa gumakansu sujada, waɗanda suka zama tarko gare su.
37 Et ils sacrifièrent aux démons leurs fils et leurs filles.
Suka miƙa’ya’yansu maza hadaya’yan matansu kuma ga aljanu.
38 Et ils versèrent le sang innocent, le sang de leurs fils et de leurs filles, qu'ils immolèrent aux sculptures de Chanaan. Et la terre fut pleine de carnage et de sang.
Suka zub da jini marar laifi, jinin’ya’yansu maza da mata, waɗanda suka miƙa hadaya ga gumakan Kan’ana, ƙasar kuwa ta ƙazantu ta wurin jininsu.
39 Et elle fut souillée par leurs œuvres; et ils se prostituèrent en leurs passions.
Suka ƙazantar da kansu ta wurin abin da suka yi; ta wurin ayyukansu suka yi karuwanci.
40 Et le Seigneur s'enflamma de colère contre son peuple, et il eut en abomination son héritage.
Saboda haka Ubangiji ya yi fushi da mutanensa ya ji ƙyamar gādonsa.
41 Et il les livra aux mains de leurs ennemis, et ceux qui les haïssaient devinrent leurs maîtres.
Ya miƙa su ga al’ummai, maƙiyansu kuma suka yi mulki a kansu.
42 Et leurs ennemis les opprimèrent, et ils furent humiliés sous leurs mains.
Abokan gābansu suka danne su suka sa su a ƙarƙashin ikonsu.
43 Souvent Dieu les sauva; mais ils l'irritèrent encore en leurs conseils, et ils furent humiliés dans leurs iniquités.
Sau da yawa ya cece su, amma sun nace su yi tawaye suka kuma lalace cikin zunubinsu.
44 Et le Seigneur les vit en leurs tribulations, et il écouta leur prière.
Amma ya lura da wahalarsu sa’ad da ya ji kukansu;
45 Et il se souvint de son alliance, et il se repentit en la plénitude de sa miséricorde.
saboda su ya tuna da alkawarinsa kuma daga yawan ƙaunarsa ya ji tausayi.
46 Et il leur accorda ses miséricordes, en face de ceux qui les retenaient captifs.
Ya sa aka ji tausayinsu a wurin dukan waɗanda suka kame su.
47 Sauve-nous, Seigneur notre Dieu, et rassemble-nous du milieu des Gentils, pour que nous proclamions ton saint nom et que nous mettions notre gloire à te louer.
Ka cece mu, Ubangiji Allahnmu, ka kuma tattara mu daga al’ummai, don mu yi wa sunanka mai tsarki godiya mu kuma ɗaukaka cikin yabonka.
48 Béni soit le Seigneur, Dieu d'Israël, dans tous les siècles des siècles, et tout le peuple dira: Ainsi soit-il! Ainsi soit-il!
Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Bari dukan mutane su ce, “Amin!” Yabo ga Ubangiji.

< Psaumes 106 >