< Proverbes 29 >

1 L'homme qui reprend vaut mieux que l'indocile; car celui-ci tombera soudain dans des maux cuisants et sans remède.
Mutumin da ya ci gaba da taurinkai bayan an kwaɓe shi ba da daɗewa ba zai hallaka ba makawa.
2 Quand les justes sont loués, les peuples sont dans la joie; mais quand les impies gouvernent, les hommes gémissent.
Sa’ad da masu adalci suke cin nasara, mutane kan yi farin ciki sa’ad da mugaye suke mulki, mutane kan yi nishi.
3 Un homme qui aime la sagesse fait la joie de son père; celui qui nourrit des prostituées dissipe ses richesses.
Duk mai ƙaunar hikima kan kawo wa mahaifinsa farin ciki, amma wanda yake ma’amala da karuwai kan lalatar da dukiyarsa.
4 Le roi juste fait prospérer ses États; le méchant les ruine.
Ta wurin yin adalci sarki kan sa ƙasa tă yi ƙarƙo amma duk mai haɗama don cin hanci kan rushe ƙasar.
5 Celui qui tend un filet à la face de son ami, s'y prendra lui-même les pieds.
Duk wanda yake wa maƙwabcinsa daɗin baki yana sa wa ƙafafunsa tarko ne.
6 Le pécheur marche environné de pièges; le juste vit plein de paix et de joie.
Mugun mutum tarko ne ta wurin zunubinsa, amma mai adalci zai iya rera ya kuma yi murna.
7 Le juste sait rendre justice aux pauvres; mais l'impie n'entend pas cette science, et le nécessiteux n'a pas l'esprit assez intelligent.
Masu adalci sun damu game da adalci don talakawa, amma mugaye ba su da wannan damuwa.
8 Les hommes déréglés mettent en feu une ville; le sage apaise les colères.
Masu ba’a kan kuta faɗa a birni, amma masu hikima sukan kwantar da fushi.
9 Un homme sage juge les nations; mais un homme méprisable, s'il se met en colère, fait rire et n'effraie personne.
In mai hikima ya je wurin shari’a da wawa, wawa kan yi ta fushi yana ta dariya, ba kuwa za a sami salama ba.
10 Les hommes de sang haïssent un saint; les hommes droits recherchent son âme.
Masu kisankai sukan ƙi mutum mai mutunci su kuma nema su kashe mai aikata gaskiya.
11 L'insensé donne cours à toute sa colère; le sage la contient et la mesure.
Wawa yakan nuna fushinsa a fili, amma mai hikima kan kanne fushinsa.
12 Quand un roi prête l'oreille à l'injustice, tous ses sujets transgressent la loi.
In mai mulki yana sauraran ƙarairayi, dukan ma’aikatansa za su zama mugaye.
13 L'usurier et l'emprunteur marchent ensemble; le Seigneur les surveille l'un et l'autre.
Matalauci da azzalumi suna da wannan abu ɗaya. Ubangiji ne yake ba dukansu gani.
14 Si un roi juge les pauvres selon la vérité, son trône sera affermi pour servir de témoignage.
In sarki yana hukunta talakawa da adalci kursiyinsa kullum zai kasance lafiya.
15 Les réprimandes et les corrections donnent la sagesse; l'enfant qui s'en écarte est la honte de ses parents.
Sandar gyara kan ba da hikima, amma yaron da aka bari ba horo kan jawo kunya ga mahaifiyarsa.
16 Plus il y a d'impies, plus il y a de péchés; les justes, avertis par leurs chutes, deviennent craintifs.
Sa’ad da mugaye suke cin nasara, haka zunubi zai yi ta ƙaruwa, amma masu adalci za su ga fāɗuwar waɗannan mutane.
17 Corrige ton fils, et il donnera à toi le repos, à ton âme la gloire.
Ka hori ɗanka, zai kuwa ba ka salama; zai ba ka farin cikin da kake so.
18 Il n'est point de prophète pour une nation perverse; mais bienheureux est celui qui garde la loi.
Inda ba wahayi, mutane kan kangare; amma masu albarka ne waɗanda suke kiyaye doka.
19 La parole ne suffit pas pour corriger un mauvais serviteur; car même quand il la comprend, il lui est indocile.
Ba a yi wa bawa gyara ta wurin magana kawai; ko da ya fahimta ma, ba zai kula ba.
20 Si tu vois un homme prompt à parler, sache que l'insensé même a plus d'espoir que lui.
Ka ga mutum mai yin magana da garaje? To, gara a sa zuciya ga wawa da a sa zuciya gare shi.
21 Celui qui, dès l'enfance, a vécu dans les délices, un jour sera au service d'autrui et pleurera sur lui-même.
In mutum ya yi wa bawansa shagwaɓa tun yana yaro, zai jawo baƙin ciki a ƙarshe.
22 L'homme enclin à la colère excite des discordes; l'homme irascible se creuse un abîme de péchés.
Mutum mai cika fushi yakan tā da faɗa, mai zafin rai kuma kan yi zunubai masu yawa.
23 L'orgueil abaisse l'homme; le Seigneur est l'appui des humbles, et les élève en gloire.
Fariyar mutum kan jawo masa ƙasƙanci amma mai sauƙinkai kan sami girmamawa.
24 Celui qui prend sa part d'un larcin hait son âme; ceux qui ayant ouï un serment, n'en ont rien dit,
Duk wanda yake abokin ɓarawo abokin gāban kansa ne; yana jin sa yana ta rantsuwa, amma bai isa ya ce kome ba.
25 par crainte ou par égard pour les hommes, ont failli. Celui qui met sa confiance dans le Seigneur sera dans la joie; l'impiété cause la chute de l'homme; celui qui a mis sa confiance dans le Maître, sera sauvé.
Jin tsoron mutum tarko ne, amma duk wanda ya dogara ga Ubangiji zai zauna lafiya.
26 Beaucoup se prosternent devant la face du prince; mais c'est le Seigneur qui est le juge des hommes.
Mutane sukan nemi samun farin jini daga wurin sarki, amma daga wurin Ubangiji ne mutum kan sami adalci.
27 Le juste est en abomination à l'injuste; et celui qui suit la droite voie est en abomination au pervers.
Masu adalci suna ƙyamar masu rashin gaskiya; mugaye sukan yi ƙyamar masu aikata gaskiya.

< Proverbes 29 >