< Nombres 1 >

1 Et le Seigneur parla à Moïse dans le tabernacle du témoignage, au désert de Sina, le premier du second mois de la seconde année, après la sortie d'Egypte, disant:
Ubangiji ya yi magana da Musa a Tentin Sujada a cikin Hamadar Sinai, a rana ta fari na watan biyu a shekara ta biyu, bayan Isra’ilawa suka fito Masar ya ce,
2 Prenez le nombre de toute la synagogue d'Israël, et comptez-les par familles, par maisons paternelles, par têtes et par leurs noms.
“Ka yi ƙidayan dukan al’umman Isra’ilawa bisa ga iyalansu da kabilarsu, ka rubuta kowa da sunansa bi da bi.
3 Tout mâle de vingt ans et au-dessus, tout Israélite pouvant marcher au combat, comptez-le dans l'armée. Tu feras ce dénombrement avec Aaron.
Da kai da Haruna za ku lissafta dukan mazan Isra’ila bisa ga sashensu, waɗanda suka kai shekaru ashirin ko fiye, da za su iya shiga soja.
4 Faites-vous seconder par les princes des diverses tribus et familles paternelles.
Mutum ɗaya daga kowace kabila wanda yake shugaban danginsa, zai taimake ku.
5 Voici les noms des hommes qui vous assisteront; parmi ceux de Ruben, Elisur, fils de Sédiur;
“Ga sunayen da za su taimake ku. “Daga kabilar Ruben, Elizur ɗan Shedeyur;
6 Parmi ceux de Siméon: Salamiel, fils de Surisadaï;
daga kabilar Simeyon, Shelumiyel ɗan Zurishaddai;
7 Parmi ceux de Juda: Nahasson, fils d'Aminadab;
daga kabilar Yahuda, Nashon ɗan Amminadab;
8 Parmi ceux d'Issachar: Nathanaël, fils de Sogar;
daga kabilar Issakar, Netanel ɗan Zuwar;
9 Parmi ceux de Zabulon: Eliab, fils de Chaïlon;
daga kabilar Zebulun, Eliyab ɗan Helon;
10 Parmi ceux de Joseph et d'Ephraïm: Elisama, fils d'Emiud; et parmi ceux de Manassé: Gamaliel, fils de Phadasur;
daga kabilar’ya’yan Yusuf, daga Efraim, Elishama ɗan Ammihud; daga Manasse, Gamaliyel ɗan Fedazur;
11 Parmi ceux de Benjamin: Abidan, fils de Gadéoni;
daga kabilar Benyamin, Abidan ɗan Gideyoni;
12 Parmi ceux de Dan: Achièzer, fils d'Amisadaï;
daga kabilar Dan, Ahiyezer ɗan Ammishaddai;
13 Parmi ceux d'Aser: Phagéel, fils d'Echran;
daga kabilar Asher, Fagiyel ɗan Okran;
14 Parmi ceux de Gad: Eliasaph, fils de Raguel;
daga kabilar Gad, Eliyasaf ɗan Deyuwel;
15 Et parmi ceux de Nephthali: Achire, fils d'Enan.
daga kabilar Naftali, Ahira ɗan Enan.”
16 Ce sont les plus illustres du peuple, les princes de leurs tribus selon leur origine paternelle, commandants de mille hommes en Israël.
Waɗannan su ne mutanen da aka naɗa daga cikin jama’a, shugabannin asalin kabilu. Su ne kuma shugabannin dangogin Isra’ila.
17 Moïse et Aaron prirent donc les hommes nominativement désignés.
Sai Musa da Haruna suka ɗauki sunayen mutanen nan da aka ba su,
18 Puis, ils rassemblèrent tout le peuple, le premier jour du second mois de la seconde année, et ils firent le dénombrement; ils prirent les noms de tous les mâles de vingt ans et au-dessus, selon leur naissance, par familles et par têtes,
suka kira dukan al’umma wuri ɗaya a rana ta fari ga wata na biyu. Aka kuwa rubuta mutanen bisa ga asalin kabilansu da iyalansu. Aka kuma rubuta sunayen maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekaru ashirin ko fiye,
19 Comme le Seigneur l'avait prescrit à Moïse; ils firent ce recensement dans le désert de Sina.
yadda Ubangiji ya umarci Musa. Da haka ya ƙidaya su a Hamadar Sinai.
20 Les fils de Ruben, premier-né d'Israël, de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui pouvaient aller à l'armée, furent comptés nominativement par familles, par branches, par maisons paternelles et par têtes,
Daga zuriyar Ruben ɗan fari na Isra’ila. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
21 Et le recensement de la tribu de Ruben donna quarante-six mille cinq cents hommes.
Jimillar maza daga mutanen Ruben 46,500 ne.
22 Les fils de Siméon, de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui pouvaient aller à l'armée, furent comptés nominativement pat familles, par branches, par maisons paternelles et par têtes,
Daga zuriyar Simeyon. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
23 Et le recensement de la tribu de Siméon donna cinquante-neuf mille trois cents hommes.
Jimillar maza daga mutanen Simeyon 59,300 ne.
24 Les fils de Juda, de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui pouvaient aller à l'armée, furent comptés nominativement par familles, par branches, par maisons paternelles, par têtes,
Daga zuriyar Gad. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
25 Et le recensement de la tribu de Juda donna soixante-quatorze mille six cents hommes.
Jimillar maza daga mutanen Gad 45,650 ne.
26 Les fils d'Issachar de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui pouvaient aller à l'armée, furent compter nominativement par familles, par branches, par maisons paternelles, par têtes,
Daga zuriyar Yahuda. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
27 Et le recensement de la tribu d'Issachar donna cinquante-quatre mille quatre cents hommes.
Jimillar maza daga mutanen Yahuda 74,600 ne.
28 Les fils de Zabulon, tous ceux qui pouvaient aller à l'armée, furent comptes nominativement par familles, par branches, par maisons paternelles, par têtes,
Daga zuriyar Issakar. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
29 Et le recensement de la tribu de Zabulon donna cinquante-sept mille quatre cents hommes.
Jimillar maza daga mutanen Issakar 54,400 ne.
30 Les fils de Joseph, fils d'Ephraïm, de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui pouvaient aller à l'armée, furent compter nominativement par familles, par branches, par maisons paternelles, par têtes,
Daga zuriyar Zebulun. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
31 Et le recensement de la tribu d'Ephraïm donna quarante mille cinq cents hommes.
Jimillar maza daga mutanen Zebulun 57,400 ne.
32 Les fils de Manassé, de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui pouvaient aller à l'armée, furent comptés nominativement par familles, par branches, par maisons paternelles, par têtes,
Daga’ya’yan Yusuf. Daga zuriyar Efraim. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
33 Et le recensement de la tribu de Manassé donna trente-deux mille deux cents hommes.
Jimillar maza daga mutanen Efraim 40,500 ne.
34 Les fils de Benjamin, de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui pouvaient aller à l'armée, furent comptés nominativement par familles, par branches, par maisons paternelles, par têtes,
Daga zuriyar Manasse. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
35 Et le recensement de la tribu de Benjamin donna trente-cinq mille quatre cents hommes.
Jimillar maza daga mutanen Manasse 32,200 ne.
36 Les fils de Gad, de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui pouvaient aller à l'armée, furent comptés nominativement par familles, par branches, par maisons paternelles, par têtes,
Daga zuriyar Benyamin. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
37 Et le recensement de la tribu de Gad donna quarante-cinq mille six cent cinquante hommes.
Jimillar maza daga mutanen Benyamin 35,400 ne.
38 Les fils de Dan, de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui pouvaient aller à l'armée, furent comptés nominativement par familles, par branches, par maisons paternelles, par têtes,
Daga zuriyar Dan. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
39 Et le recensement de la tribu de Dan donna soixante-deux mille sept cents hommes.
Jimillar maza daga mutanen Dan 62,700 ne.
40 Les fils d'Aser, de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui pouvaient aller à l'armée, furent comptés nominativement par familles, par branches, par maisons paternelles, par têtes,
Daga zuriyar Asher. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
41 Et le recensement de la tribu d'Aser donna quarante-un mille cinq cents hommes.
Jimillar maza daga mutanen Asher 41,500 ne.
42 Les fils de Nephthali, de vingt ans et au-dessus, tous ceux qui pouvaient aller à l'armée, furent comptés nominativement par familles, par branches, par maisons paternelles, par têtes,
Daga zuriyar Naftali. Aka rubuta sunayen dukan maza ɗaya-ɗaya da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, bisa ga iyalansu da kabilarsu da take a rubuce.
43 Et le recensement de la tribu de Nephthali donna cinquante-trois mille quatre cents hommes.
Jimillar maza daga mutanen Naftali kuwa 53,400 ne.
44 Tel fut le dénombrement que fit Moïse avec Aaron, et les chefs d'Israël au nombre de douze, un homme par tribu, pris dans la tribu de sa maison paternelle.
Waɗannan su ne mazan da Musa da Haruna, tare da shugabanni goma sha biyun nan na Isra’ila suka ƙidaya, kowa a madadin iyalinsa.
45 Et Le recensement total des fils d'Israël, de vingt ans et au-dessus, en état de porter les armes, donna
Dukan Isra’ilawan da suka kai shekara ashirin ko fiye da suka isa shiga soja, an ƙidaya su bisa ga iyalansu.
46 Six cent trois mille cinq cent cinquante hommes.
Jimillar kuwa ita ce mutum 603,550.
47 Mais les lévites de la tribu paternelle de Lévi ne furent point recensés parmi les fils d'Israël.
Ba a dai ƙidaya zuriyar Lawi tare da saura kabilan ba.
48 Car le Seigneur avait parlé à Moïse, disant:
Ubangiji ya riga ya gaya wa Musa cewa,
49 Tu ne recenseras pas la tribu de Lévi, et tu n'en prendras pas le nombre parmi les fils d'Israël.
“Ka tabbatar ba ka ƙidaya mutanen Lawi ko kuma ka haɗe su tare a ƙidayan sauran Isra’ilawa ba.
50 Tu donneras aux lévites le soin du tabernacle du témoignage, de ses ornements et de tout ce qu'il renferme; et ils transporteront le tabernacle avec tous ses ornements; ils exerceront le sacerdoce dans le tabernacle, et ils camperont autour du tabernacle.
A maimakon haka sai ka naɗa Lawiyawa su lura da tabanakul Shaida, wato, kan dukan kayayyaki da kuma kome da yake na wuri mai tsarki. Za su ɗauko tabanakul da dukan kayayyakinsa; za su lura da shi, su kasance kewaye da shi.
51 Lorsqu'il faudra enlever le tabernacle, les Lévites l'enlèveront, et lorsqu'il faudra dresser le tabernacle, ils, le dresseront; que l'homme d'une autre tribu qui s'en approcherait soit mis à mort.
Duk sa’ad da za a gusar da tabanakul, Lawiyawa ne za su saukar da shi; kuma duk sa’ad da za a kafa shi, Lawiyawa ne za su yi haka. Duk wani dabam da ya je kusa da shi za a kashe shi.
52 Lorsque les fils d'Israël camperont en corps d'armée, chacun au rang à lui assigné, selon la branche a laquelle il appartient,
Sauran Isra’ilawa za su zauna ƙungiya-ƙungiya, kowane mutum a ƙungiyarsa daidai bisa ga ƙa’idarsa.
53 Que les lévites campent en cercle, près du tabernacle du témoignage, et il n'y aura point de péché parmi les fils d'Israël. Les lévites seuls auront la garde du tabernacle du témoignage.
Amma Lawiyawa za su kafa sansaninsu kewaye da tabanakul na Shaida. Don kada fushi yă fāɗo a kan al’ummar Isra’ilawa. Hakkin Lawiyawa ne su kula da tabanakul na Shaida.”
54 Et tout ce que le Seigneur avait prescrit à Moïse et à Aaron, les fils d'Israël le firent.
Isra’ilawa suka yi duk waɗannan kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.

< Nombres 1 >