< Jérémie 23 >

1 Maudits soient les pasteurs qui perdent et dispersent les brebis de leur pâturage!
“Kaiton makiyayan da suka hallakar suka kuma warwatsar da tumakin makiyayanta!” In ji Ubangiji.
2 A cause de cela, voici ce que dit le Seigneur sur les pasteurs de mon peuple: Vous avez dispersé et repoussé mes brebis, et vous ne les avez pas visitées. Et moi je vous punirai de vos méchantes œuvres.
Saboda haka ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila yana ce wa makiyayan da suke lura da mutanena, “Domin kun watsar da garkena kuka kuma kore su ba ku kuma lura da su ba, zan kawo hukunci a kanku saboda muguntar da kuka yi,” in ji Ubangiji.
3 Moi-même je recueillerai les restes de mon peuple sur toute terre où je les ai bannis, et je les rétablirai en leurs pâturages, et ils croîtront et ils se multiplieront.
“Ni kaina zan tattara raguwar garkena daga ƙasashen da na kore su zuwa zan kuma dawo da su ga makiyayansu, inda za su yi ta haihuwa su riɓaɓɓanya.
4 Et je susciterai pour eux des pasteurs qui les mèneront paître, et ils n'auront plus peur, et ils ne trembleront plus, dit le Seigneur.
Zan sa makiyaya a kansu waɗanda za su lura da su, ba za su ƙara jin tsoro ko razana ba, ba kuwa waninsu da zai ɓace,” in ji Ubangiji.
5 Voilà que les jours arrivent, dit le Seigneur, où je susciterai pour David un soleil de justice, et un roi règnera, et il comprendra, et il rendra justice selon le jugement à toute la terre.
“Kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan tā da wa Dawuda Reshen adalci, Sarki wanda zai yi mulki da hikima ya kuma yi abin da yake gaskiya da kuma daidai a ƙasar.
6 De son temps, Juda sera sauvé, et Israël s'abritera dans ses demeures en toute assurance. Et le nom que lui donnera le Seigneur sera Josédec, parmi les prophètes.
A cikin zamaninsa za a ceci Yahuda Isra’ila kuma zai zauna lafiya. Sunan da za a kira shi ke nan, Ubangiji Adalcinmu.
7 A cause de cela, voilà que les jours approchent, dit le Seigneur, où ils ne diront plus: Vive le Seigneur, qui a tiré la maison d'Israël de la terre d'Égypte!
“Saboda haka fa, kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da mutanen ba za su ƙara cewa, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da Isra’ila daga Masar ba,’
8 Mais: Vive le Seigneur, qui a rassemblé toute la race d'Israël, et l'a ramenée de la terre du nord et de toutes les contrées où il les avait bannis, et qui les a rétablis dans leur héritage!
amma za su ce, ‘Muddin Ubangiji yana raye, wanda ya fito da zuriyar Isra’ila daga ƙasar arewa da kuma daga dukan ƙasashen da ya yashe su.’ Sa’an nan za su zauna a ƙasarsu.”
9 Parmi les prophètes, je suis celui au cœur brisé; tous mes os ont été ébranlés; je suis devenu comme un homme meurtri ou comme un homme pris de vin, à la vue du Seigneur et de la magnificence de sa gloire.
Game da annabawa kuwa, Zuciyata ta karai; dukan ƙasusuwana suna kaɗuwa. Na zama kamar wanda ya bugu, kamar mutumin da ruwan inabi ya sha kansa, saboda Ubangiji da kuma maganarsa mai tsarki.
10 Devant sa face, la terre est en deuil, et les pâturages du désert sont desséchés; et la course de ces hommes est devenue mauvaise, et leur force pareillement.
Ƙasar ta cika da mazinata; saboda la’ana ƙasar ta zama kango makiyaya a hamada ta bushe. Annabawa suna bin mugayen muradu suna kuma amfani da ƙarfinsu a hanyar marar kyau.
11 Le prêtre et le prophète se sont souillés; jusque dans mon temple j'ai vu leur corruption.
“Annabi da firist dukansu biyu marasa sanin Allah ne; har ma a cikin haikalina na tarar da muguntarsu,” in ji Ubangiji.
12 A cause de cela, que leur voie soit glissante et sombre, et ils y trébucheront, et ils y tomberont; car j'amènerai sur eux des maux en l'année où je les visiterai.
“Saboda haka hanyarsu za tă yi santsi; za a jefar da su cikin duhu a can kuwa za su fāɗi. Zan kawo musu masifa a shekarar da za a hukunta su,” in ji Ubangiji.
13 Et les prophètes de Samarie, j'ai vu en eux des iniquités; ils ont prophétisé par Baal, et ils ont égaré mon peuple d'Israël.
“A cikin annabawan Samariya na ga wannan abin banƙyama. Suna annabci ta wurin Ba’al suna ɓad da mutanena Isra’ila.
14 Et les prophètes de Jérusalem, j'ai vu en eux des choses horribles; adultères, cheminant dans le mensonge, prenant de toutes mains pour ne point détourner les méchants de leurs voies, ils ont tous été pour moi comme Sodome, et les habitants de Jérusalem comme Gomorrhe.
A cikin annabawan Urushalima kuma na ga wani abin bantsoro. Suna zina suna kuma rayuwar ƙarya. Sun ƙarfafa hannuwa masu aikata mugunta, domin kada wani ya juya daga muguntarsa. Dukansu sun yi kama da Sodom a gare ni; mutanen Urushalima sun yi kama da Gomorra.”
15 A cause de cela, ainsi dit le Seigneur: Voilà que je vais les nourrir de douleurs, et je les abreuverai d'eau saumâtre, parce que des prophètes de Jérusalem est sortie la souillure de toute la terre.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da annabawa, “Zan sa su ci abinci mai ɗaci su kuma sha ruwa mai dafi, domin daga annabawan Urushalima rashin sani Allah ya bazu ko’ina a ƙasar.”
16 Voici ce que dit le Seigneur tout-puissant: N'écoutez point les discours des prophètes, parce qu'ils ont des visions vaines; ils parlent selon leur cœur, et non selon la bouche de Dieu.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Kada ku saurari abin da annabawan suke muku annabci; suna cika ku da sa zuciyar ƙarya. Suna maganar wahayi daga tunaninsu, ba daga bakin Ubangiji ba.
17 Ils disent à ceux qui rejettent la parole du Seigneur: La paix sera avec vous; et à ceux qui courent après leurs désirs et après les égarements de leurs cœurs: Il ne vous arrivera rien de mal.
Suna cin gaba da ce wa waɗanda suka rena ni, ‘Ubangiji ya ce za ku zauna lafiya.’ Ga duka waɗanda suke bin taurin zukatansu kuwa sukan ce, ‘Babu lahanin da zai same ku.’
18 Car qui a assisté au conseil du Seigneur? qui a vu sa parole? qui l'a entendue de ses oreilles?
Amma wane ne a cikinsu ya taɓa tsaya a majalisar Ubangiji yă ga ko ya ji maganarsa? Wa ya saurari ya kuma ji maganarsa?
19 Voilà un tremblement de terre venu du Seigneur, et sa colère produit ce tremblement; elle viendra frapper les impies.
Ga shi, hadarin Ubangiji zai taso cikin hasala guguwa tana kaɗawa a kan kawunan mugaye.
20 Et la colère du Seigneur ne se détournera plus qu'elle n'ait accompli toutes les résolutions de son cœur; et à la fin des jours ils comprendront.
Fushin Ubangiji ba zai kau ba sai ya aikata nufin zuciyarsa. A kwanakin masu zuwa za ku gane sarai.
21 Je n'ai point envoyé ces prophètes, et ils ont couru d'eux-mêmes; je ne leur ai rien dit, et d'eux-mêmes ils ont prophétisé.
Ban aiki waɗannan annabawa ba, duk da haka sun tafi da saƙonsu; ban yi musu magana ba, duk da haka sun yi annabci.
22 Et s'ils avaient assisté à mon conseil, s'ils avaient entendu mes paroles, je les aurais corrigés, et corrigé mon peuple de ses mauvaises inclinations.
Amma da a ce sun tsaya a majalisata, da sun yi shelar maganata ga mutanena sun kuma juyar da su daga mugayen hanyoyinsu da kuma daga mugayen ayyukansu.
23 Je suis Dieu de près, dit le Seigneur; ne suis-je pas aussi Dieu de loin?
“Ni ɗin Allah na kusa ne kawai,” in ji Ubangiji, “ba Allah na nesa ba?
24 Qui se cachera dans le secret, sans que je le découvre? Est-ce que je ne remplis pas le ciel et la terre? dit le Seigneur.
Akwai wanda zai iya ɓuya a lungu har da ba zan iya ganinsa ba?” In ji Ubangiji “Ban cika sama da ƙasa ba?” In ji Ubangiji.
25 J'ai entendu ce que disent les prophètes, ce qu'ils prophétisent en mon nom; ils mentent quand ils disent: J'ai eu un songe.
“Na ji abin da annabawa suna cewa su da suke annabcin ƙarya a sunana. Suna cewa, ‘Na yi mafarki! Na yi mafarki!’
26 Jusques à quand en sera-t-il ainsi du cœur de ces prophètes, qui prophétisent le mensonge, en prophétisant les séductions de leur cœur?
Har yaushe wannan zai ci gaba a cikin zukata annabawa masu ƙarya, waɗanda suke annabcin ruɗun tunaninsu?
27 Ils s'imaginent faire oublier ma loi par des songes que chacun se raconte, comme d'autres ont fait oublier mon nom à leurs pères à cause de Baal?
Suna tsammanin mafarkan da suke faɗa wa juna za su sa mutane su manta da sunana, kamar yadda kakanninsu suka manta da sunana ta wurin yin wa Ba’al sujada.
28 Que le prophète qui a eu un songe le raconte; que celui à qui est venue ma parole annonce selon la vérité. Qu'est-ce que la paille auprès du grain? Ainsi en est-il de mes paroles, dit le Seigneur.
Bari annabin da ya yi mafarki ya faɗa mafarkinsa, amma bari wanda yake da maganata ya yi ta da aminci. Gama me ya haɗa ciyawa da alkama?” In ji Ubangiji.
29 Mes paroles ne sont-elles pas comme le feu, dit le Seigneur, ou comme la hache qui fend un rocher?
“Maganata ba wuta ba ce,” in ji Ubangiji, “kuma kamar gudumar da kan ragargaza dutse?
30 Voilà pourquoi je suis contre les prophètes, dit le Seigneur Dieu, qui dérobent mes paroles à leurs frères.
“Saboda haka,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke satar maganganuna daga juna.
31 Voilà pourquoi je suis contre les prophètes qui prophétisent de la langue et disent les rêves de leur sommeil.
I,” in ji Ubangiji, “Ina gāba da annabawan da suke kaɗa harsunansu sa’an nan su ce, ‘Ubangiji ne ya furta.’
32 Voilà pourquoi je suis contre les prophètes qui prophétisent d'après des songes trompeurs et les racontent, et qui ont égaré mon peuple par leurs mensonges et leurs erreurs; et je ne les avais pas envoyés, et je ne leur avais rien prescrit, et ils ne seront d'aucun secours à ce peuple.
Tabbatacce, ina gāba da waɗannan da suke annabci mafarkan karya,” in ji Ubangiji. “Suna faɗarsu suna ɓad da mutanena da ƙarairayinsu na rashin hankali, duk da haka ban aike su ba, ban kuwa umarce su ba. Ba su amfani wannan mutane ba ko kaɗan,” in ji Ubangiji.
33 Et si ce peuple, ou le prêtre, ou le prophète demandent quel est le fardeau du Seigneur, dis-leur: Vous êtes ce fardeau, et je vous briserai, dit le Seigneur.
“Sa’ad da waɗannan mutane, ko annabi ko firist, ya tambaye ka, ‘Mece ce maganarUbangiji?’ Ka ce musu, ‘Wace magana? Zan yashe ku, in ji Ubangiji.’
34 Si le prophète ou quelqu'un des prêtres ou du peuple se sert de ce mot: Le fardeau du Seigneur, je punirai cet homme et sa maison.
In annabi ko firist ko da wani dabam ya ce, ‘Wannan ne abin da Ubangiji yake cewa,’ zan hukunta wannan mutum da kuma gidansa.
35 Voici ce que vous direz chacun à votre ami, chacun à votre frère: Qu'a dit le Seigneur? quelle est la parole du Seigneur?
Ga abin da kowannenku yana cin gaba da ce wa abokinsa ko danginsa, ‘Mece ce amsar Ubangiji?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
36 Mais ne prononcez plus ce mot: Le fardeau du Seigneur; car c'est votre parole qui sera un fardeau pour lui.
Amma kada ku ƙara ambatar ‘maganar Ubangiji’ domin kowace maganar mutum kan zama maganarsa. Ta haka kukan lalace maganar Allah mai rai, Ubangiji Maɗaukaki, Allahnmu.
37 C'est pourquoi il faut dire: Le Seigneur Dieu nous a-t-il parlé?
Ga abin da za ku ci gaba da faɗa wa annabi, ‘Mece ce amsar Ubangiji gare ka?’ Ko kuwa ‘mene ne Ubangiji ya faɗa?’
38 Voici donc ce que dit le Seigneur notre Dieu: En punition de ce que vous avez prononcé ce mot: Fardeau du Seigneur, après que j'eus envoyé vers vous, et que je vous eus fait dire: Ne dites plus: Le fardeau du Seigneur;
Ko da yake kuna cewa, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ga abin da Ubangiji yana cewa kuna amfani da kalmomi, ‘Wannan ce maganar Ubangiji,’ ko da yake na ce muku kada ku ce, ‘Wannan ce maganar Ubangiji.’
39 A cause de cela, voilà que moi je vous prends et vous brise, vous et cette ville, que j'ai donnée à vous et à vos pères.
Saboda haka, tabbatacce zan manta da ku in kuma jefar da ku daga gabana tare da birnin da na ba ku da kuma kakanninku.
40 Et je vous marquerai d'un éternel opprobre, d'une honte éternelle qui ne sera jamais oubliée.
Zan kawo muku madawwamiyar kunya, kunya ta har abada wadda ba za a taɓa manta ba.”

< Jérémie 23 >