< Jérémie 13 >

1 Voici ce que dit le Seigneur: Pars et achète-toi une ceinture de lin, et mets-la autour de tes reins, et elle ne passera pas l'eau.
Ga abin da Ubangiji ya faɗa mini, “Tafi ka sayo abin ɗamara na lilin ka sha ɗamara da shi, amma kada ka bari yă taɓa ruwa.”
2 Et j'achetai la ceinture, selon la parole du Seigneur, et je la mis autour de mes reins.
Saboda haka na sayo abin ɗamara, yadda Ubangiji ya umarce ni, na kuwa sha ɗamara da shi.
3 Et la parole du Seigneur vint à moi, disant:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini sau na biyu cewa,
4 Prends la ceinture qui entoure tes reins, et lève-toi; puis va sur l'Euphrate, et en ce lieu cache-la dans une crevasse de rocher,
“Ka ɗauki abin ɗamara da ka sayo, wanda ka ɗaura, ka tafi yanzu zuwa Fera ka ɓoye shi a cikin kogon dutse.”
5 Et je partis, et je cachai la ceinture près de l'Euphrate, somme me l'avait commandé le Seigneur.
Saboda haka na tafi na ɓoye shi a Fera, yadda Ubangiji ya ce mini.
6 Et ceci arriva bien des jours après, le Seigneur me dit: Lève-toi, et va sur l'Euphrate, et retire de ce lieu la ceinture que je t'ai ordonné d'y cacher.
Bayan’yan kwanaki sai Ubangiji ya ce mini, “Tafi yanzu zuwa Fera ka ɗauko abin ɗamara da na ce maka ka ɓoye a can.”
7 Et j'allai sur l'Euphrate, et je creusai, et je retirai la ceinture du lieu où je l'avais enfouie, et voilà qu'elle était si consumée, qu'elle n'était plus bonne à rien.
Sai na tafi Fera da haka na ɗauko abin ɗamara daga wurin da na ɓoye shi, amma abin ɗamara yanzu ya lalace ya zama ba shi da amfani sam.
8 Et la parole du Seigneur vint à moi, disant:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
9 Voici ce que dit le Seigneur: Ainsi je consumerai l'orgueil de Juda et l'orgueil de Jérusalem,
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, ‘Haka zan lalatar da alfarmar Yahuda da yawan alfarmar Urushalima.
10 Et ce grand orgueil des hommes qui ne veulent point écouter ma parole, et qui ont marché à la nuit des dieux étrangers, pour les adorer et les servir. Et ils seront comme une ceinture qui n'est plus bonne à rien.
Waɗannan mugayen mutane, waɗanda suka ƙi saurari maganata, waɗanda suka biye wa taurin zuciyarsu suka bi waɗansu alloli don su bauta su kuma yi musu sujada, za su zama kamar wannan abin ɗamara gaba ɗaya marasa amfani!
11 Car de même qu'on attache une ceinture aux reins de l'homme, de même je m'étais attaché la maison d'Israël et toute la maison de Juda, pour qu'elles fussent mon peuple renommé, ma fierté et ma gloire; et ils ne m'ont point écouté.
Gama kamar yadda abin ɗamara kan kame gindin mutum tam, haka zan daure dukan gidan Isra’ila da dukan gidan Yahuda gare ni,’ in ji Ubangiji, ‘domin su zama jama’a, da suna, da yabo, da daraja a gare ni, amma sun ƙi ji.’
12 Et tu diras à ce peuple: Chaque outre sera remplie de vin; et s'ils te disent: Ne savons-nous pas que chaque outre sera remplie de vin?
“Faɗa musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi.’ In kuwa suka ce maka, ‘Ba mu san cewa ya kamata a cika kowace salkar ruwan inabi da ruwan inabi ba?’
13 Tu leur diras: Ainsi dit le Seigneur: Voilà que je vais remplir de boisson enivrante ceux qui habitent cette terre, et leurs rois, fils de David assis sur le trône, et leurs prêtres, et tous les hommes de Juda et de Jérusalem;
Sai ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, zan cika dukan waɗanda suke zama a ƙasar da buguwa, har ma da sarakunan da suke zama a kursiyin Dawuda, firistoci, annabawa da dukan waɗanda suke zaune a Urushalima.
14 Et je les disperserai tous: je séparerai le frère du frère, et le père de ses fils. Je n'en aurai point de regrets, dit le Seigneur, et je n'épargnerai personne, et je serai sans pitié en les détruisant.
Zan fyaɗe su a kan juna, iyaye da’ya’yansu maza, in ji Ubangiji. Tausayi ko jinƙai, ko juyayi ba zai hana ni hallaka su ba.’”
15 Écoutez, prêtez l'oreille, et ne vous élevez pas; car le Seigneur a parlé.
Ku ji ku kuma saurara, kada ku yi girman kai, gama Ubangiji ya yi magana.
16 Rendez gloire au Seigneur votre Dieu, avant la nuit, avant que vos pieds se heurtent à des montagnes de ténèbres. Et vous attendez la lumière; et ce sera l'ombre de la mort, et les hommes resteront dans l'obscurité.
Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnku kafin ya kawo duhu, kafin ƙafafunku su yi tuntuɓe a kan tuddai masu duhu. Za ku sa zuciya ganin haske amma zai mai da shi duhu mai kauri ya kuma canja shi zuwa duhu baƙi ƙirin.
17 Si vous ne m'écoutez point, votre âme pleurera secrètement sur son orgueil, et vos yeux verseront des larmes, parce que le troupeau du Seigneur aura été meurtri.
Amma in ba ku saurara ba, zan yi kuka a ɓoye saboda girmankanku; idanuna za su yi kuka mai zafi, suna zub da hawaye ƙwarai, domin zan kwashe garken Ubangiji zuwa zaman bauta.
18 Dites au roi et aux princes: Humiliez-vous, prosternez-vous; car votre couronne de gloire a été enlevée de votre tête.
Ka faɗa wa sarki da kuma mahaifiyar sarauniya cewa, “Ku sauko daga kursiyinku, gama rawaninku na ɗaukaka za su fāɗi daga kawunanku.”
19 Les villes du midi ont été fermées, et il n'est resté personne pour les ouvrir. Juda a été transporté tout entier; ils ont tous été émigrants et captifs.
Za a kulle biranen da suke a Negeb, kuma babu wanda zai buɗe su. Za a kwashe dukan Yahuda zuwa zaman bauta, za a kwashe su tas.
20 Lève les yeux, Jérusalem, et vois ceux qui viennent de l'aquilon. Où est le troupeau qui t'a été donné? où sont les brebis qui faisaient ta gloire?
Ku tā da idanunku ku ga waɗanda suke zuwa daga arewa. Ina garken da aka ba ku tumakin da kuke taƙama a kai?
21 Que diras-tu, quand ils te visiteront? C'est toi qui les as instruits contre toi, et tes leçons datent de loin. Ne seras-tu pas saisie de douleurs, comme la femme qui enfante?
Me za ku ce sa’ad da Ubangiji ya naɗa muku waɗanda ku kanku kuka koya musu a matsayi abokai na musamman? Ashe, azaba ba za tă auko muku kamar na mace mai naƙuda ba?
22 Et si tu dis en ton cœur: Pourquoi ces choses m'arrivent-elles? A cause de la multitude de tes iniquités; ta robe a été soulevée par derrière, pour que tes jambes reçoivent un châtiment infâme.
In kuma kuka tambaye kanku “Me ya sa wannan ya faru da mu?” Wannan kuwa saboda yawan zunubanku ne ya sa fatarinku ya yage aka kuma wahalshe jikinku.
23 Quand un Éthiopien changera la couleur de sa peau, et la panthère sa bigarrure, vous pourrez faire le bien, vous qui n'avez appris que le mal.
Mutumin Habasha zai iya canja launin fatar jikinsa ko damisa ta canja dabbare dabbarenta? Ba za ku iya yin alheri ku da kuka saba da yin mugunta ba.
24 Et je les ai dispersés comme des broussailles qu'emporte le vent du désert.
“Zan watsar da ku kamar yayin da iskar hamada take hurawa.
25 Tel sera ton sort, tel sera ton partage pour m'avoir désobéi, dit le Seigneur. Comme tu m'as oublié pour mettre ton espérance en des mensonges,
Rabonku ne wannan, sashen da na auka muku,” in ji Ubangiji “domin kun manta da ni kuka kuma dogara ga allolin ƙarya.
26 De même je relèverai ta robe sur ta face, et ton ignominie apparaîtra,
Zan kware fatarinku sama ya rufe fuskarku don a iya ga tsiraicinku
27 Et tes adultères, et tes hennissements, et ta prostitution à des étrangers; j'ai vu tes abominations sur les collines et dans les champs. Malheur à toi, Jérusalem; car tu n'as pas été purifiée, pour marcher à ma suite. Et jusques à quand en sera-t-il ainsi?
zinace zinacenku da haniniya kamar dawakai, karuwancinku na bankunya! Na ga ayyukanku na banƙyama a kan tuddai da kuma a filaye. Kaitonki, ya Urushalima! Har yaushe za ki ci gaba da rashin tsarki?”

< Jérémie 13 >