< Isaïe 58 >

1 Crie de toute ta force, et ne cesse point; élève ta voix comme le son d'une trompette, et fais connaître ses péchés à mon peuple, et à la maison de Jacob ses iniquités.
“Ku yi ihu da ƙarfi, ba ƙaƙƙautawa. Ku tā da muryarku kamar busar ƙaho. Ku furta wa mutanena tawayensu da kuma ga gidan Yaƙub zunubansu.
2 Ils me cherchent de jour en jour; ils désirent connaître mes voies comme un peuple qui a pratiqué la justice, et n'a point abandonné le jugement de son Dieu. Ils me demandent maintenant un jugement équitable, et ils désirent s'approcher de Dieu.
Gama kowace rana suna nemana; suna marmarin sanin hanyoyina, sai ka ce al’ummar da take yin abin da yake daidai ba ta kuma yashe umarnan Allahnta ba. Sun nemi shawarwaran da suke daidai daga gare ni suna kuma marmari Allah ya zo kusa da su.
3 Pourquoi, disent-ils, avons-nous jeûné sans que vous l'ayez vu? Pourquoi avons-nous humilié nos âmes sans que vous en ayez rien su? C'est qu'en vos jours de jeûne vous avez trouvé votre plaisir, et vous affligez tous tous ceux qui vous sont soumis.
Suna cewa, ‘Don me muka yi azumi, ba ka kuma gani ba? Me ya sa muka ƙasƙantar da kanmu, ba ka kuma lura da wannan ba?’ “Duk da haka a ranar azuminku, kuna yi yadda kuka ga dama kuna kuma zaluntar dukan ma’aikata.
4 Si vous jeûnez pour vous livrer à vos procès et à vos querelles, si vous frappez du poing le pauvre, à quel propos jeûnez-vous pour moi, comme aujourd'hui, criant et élevant la voix afin d'être entendus?
Azuminku yakan ƙare a faɗa da kuma hargitsi, kuna ta naushin juna da mugayen naushe-naushe. Ba za ku iya azumi kamar yadda kuke yi a yau ku zaci za a ji muryarku can sama.
5 Je n'ai point choisi ce jeûne ni ce jour pour qu'un homme humilie son âme; cesse donc de courber ton cou comme un cerceau, de t'étendre sur la cendre et les cilices, et après cela d'appeler ce jeûne agréable à Dieu.
Irin azumin da na zaɓa ke nan, rana guda kawai don mutum ya ƙasƙantar da kansa? Sunkuyar da kanku kamar iwa kawai kuna kuma kwance a tsummoki da toka? Abin da kuke kira azumi ke nan rana yardajje ga Ubangiji?
6 Ce n'est pas un tel jeûne que j'ai choisi, dit le Seigneur; mais romps tous tes liens avec l'iniquité; dénoue les nœuds des contrats violents; renvoie quittes ceux que tu as lésés; déchire toute obligation inique.
“Irin azumin da na zaɓa shi ne, a kunce sarƙoƙin rashin adalci a kuma kunce igiyoyin karkiya, a’yantar da waɗanda ake zalunta a kuma kakkarye kowace karkiya?
7 Romps ton pain avec l'affamé; recueille dans ta maison le pauvre sans abri. Si tu vois un homme nu, donne-lui des vêtements, et garde-toi de mépriser ceux de ta propre chair.
Ba shi ne ku rarraba abincinku da mayunwata ku kuma tanada wa matalauta masu yawo mahalli, sa’ad da kuka ga wanda yake tsirara, ku yi masa sutura, kada kuma ku ba wa namanku da jininku baya?
8 Alors ta lumière éclatera comme le matin; ta guérison sera prompte, ta justice te devancera, et la gloire de Dieu t'environnera.
Sa’an nan haskenku zai keto kamar ketowar alfijir, warkarwarku kuma zai bayyana nan da nan; sa’an nan adalcinku zai tafi a gabanku, ɗaukakar Ubangiji kuma zai tsare ku daga baya.
9 Tu crieras alors, et Dieu t'exaucera; tu n'auras pas fini de parler qu'il te dira: Me voici. Si tu éloignes de toi les pièges et les votes injustes, et les paroles de murmure;
Sa’an nan za ku yi kira, Ubangiji kuma zai amsa; za ku yi kuka don neman taimako, zai kuwa ce ga ni nan. “In kuka kawar da karkiyar zalunci, kuka daina nuna wa juna yatsa da kuma faɗar mugayen maganganu,
10 Si tu donnes de bon cœur du pain à l'affamé; si tu rassasies l'âme du pauvre, alors ta lumière brillera dans les ténèbres, et tes ténèbres seront comme le midi.
in kuma kuka ɗauki lokaci kuka ƙosar da mayunwata kuka kuma biya bukatun waɗanda suke shan tsanani, sa’an nan ne haskenku zai haskaka cikin duhu darenku kuma zai zama kamar tsakar rana.
11 Et Dieu sera toujours avec toi; et tu seras rassasié selon les désirs de ton âme; et tes os seront pleins de moelle; ils seront comme un verger arrosé, comme une fontaine où l'eau ne tarit jamais.
Ubangiji zai bishe ku kullum; zai biya muku bukatunku a ƙasa mai zafin rana ya kuma ƙarfafa ƙasusuwanku. Za ku zama kamar lambun da aka yi masa banruwa, kamar rafin da ruwansa ba ya ƙafewa.
12 Et tes places, autrefois désertes, seront rebâties; et tes fondations dureront dans tous les siècles pour les générations des générations; et tu seras appelé le réparateur des haies détruites, et tu feras régner la paix en tes sentiers.
Mutanenku za su sāke gina kufai na da su kuma daga tsofaffin harsashai; za a ce da ku Masu Gyaran Katangar da ta Rushe, Masu Farfaɗo da Tituna da kuma Wuraren zama.
13 Si tu défends à tes pieds de transgresser les sabbats pour ne point faire à ta volonté en un jour saint; si tu trouves des délices aux sabbats consacrés à Dieu; si tu t'abstiens de tes travaux; si aucun mot de colère ne sort de ta bouche;
“In kun kiyaye ƙafafunku daga take Asabbaci da kuma daga aikata abin da kuka gan dama a ranata mai tsarki, in kuka kira Asabbaci ranar murna rana mai tsarki ta Ubangiji kuma mai bangirma, in kuka girmama ta ta wurin ƙin yin abin da kuka gan dama da kuma yin al’amuranku ko yin mugayen maganganu,
14 Si tu mets ta confiance dans le Seigneur, il t'élèvera au-dessus des félicités de la terre; il te donnera pour te nourrir l'héritage de ton père Jacob; car ainsi a parlé la bouche du Seigneur.
sa’an nan za ku yi farin ciki a cikin Ubangiji, zan kuma sa ku a kan maɗaukaka ƙasashe ku kuma yi biki a gādon mahaifinku Yaƙub.” Ni Ubangiji ne na faɗa.

< Isaïe 58 >