< Isaïe 52 >

1 Réveille-toi, réveille-toi, Sion; revêts-toi de ta force; Jérusalem, ville sainte, revêts-toi de ta gloire; l'impur, l'incirconcis ne continueront plus à te traverser.
Ki farka, ki farka, ya Sihiyona, ki sanya wa kanki ƙarfi. Ki sa rigarki na daraja, Ya Urushalima, birni mai tsarki. Marasa kaciya da maƙazanta ba za su shi cikinki ba.
2 Secoue ta poussière et lève-toi; assieds-toi, Jérusalem; ôte les chaînes de ton cou, Sion, ma fille captive.
Ki kakkaɓe ƙurarki; ki tashi, ki zauna a kursiyinki, ya Urushalima. Ki’yantar da kanki daga sarƙoƙi a wuyanki, Ke kamammiyar Diyar Sihiyona.
3 Car voici ce que dit le Seigneur: Vous avez été vendus pour rien, et vous serez rachetés sans argent.
Gama ga abin Ubangiji yana cewa, “An sayar da ke ba da kuɗi ba, kuma ba da kuɗi za a fanshe ki ba.”
4 Ainsi dit le Seigneur: Mon peuple est descendu jadis en Égypte pour y demeurer, et il a été traîné de force chez les Assyriens.
Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Da farko mutanena suka gangara zuwa Masar don su zauna; a baya-bayan nan, Assuriya sun zalunce su.
5 Et maintenant pourquoi y êtes-vous encore? Ainsi dit le Seigneur: Parce que mon peuple a été pris gratuitement, soyez dans la stupeur, et poussez des hurlements; car voici ce que dit le Seigneur: A cause de vous, mon nom est sans cesse blasphémé chez les Gentils.
“Yanzu kuma me nake da shi a nan?” In ji Ubangiji. “Gama an kwashe mutanena ba a bakin kome ba kuma waɗanda suka mallake su sun yi musu ba’a, Kullum ana cin gaba da yin wa sunana saɓo.
6 Aussi mon peuple en ce jour-là connaîtra-t-il mon nom; car c'est moi qui parle, et me voici.
Saboda haka mutanena za su san sunana; saboda haka a wannan rana za su san cewa ni ne wanda ya faɗa wannan. I, ni ne.”
7 Me voici, comme le printemps sur les montagnes, comme les pieds de celui qui annonce la bonne nouvelle de la paix, comme celui qui annonce les biens; car je publierai ton salut, disant: Sion, ton Dieu va régner!
Me ya fi wannan kyau a kan duwatsu a ga ƙafafu na masu kawo labari mai daɗi waɗanda suke shelar salama, waɗanda suke kawo labari mai daɗi, waɗanda suke shelar ceto, waɗanda suke ce wa Sihiyona, “Allahnki yana mulki!”
8 Tes gardiens ont élevé la voix, et ils se réjouiront tous à grands cris; car ils verront de leurs yeux, quand le Seigneur aura fait miséricorde à Sion.
Ki kasa kunne! Masu tsaronki sun tā da muryoyinsu; tare sun yi sowa ta farin ciki. Sa’ad da Ubangiji ya komo Sihiyona, za su gan shi da idanunsu.
9 Que la joie éclate dans les solitudes de Jérusalem; car le Seigneur lui a fait miséricorde, et il a sauvé Jérusalem.
Ku ɓarke cikin waƙoƙin farin ciki gaba ɗaya, kangonki na Urushalima, gama Ubangiji ya ta’azantar da mutanensa, ya fanshi Urushalima.
10 Et le Seigneur montrera son bras saint à tous les Gentils; et de toutes les extrémités de la terre on verra le salut qui vient de notre Dieu.
Ubangiji zai nuna hannunsa mai tsarki a fili a idanun dukan al’ummai, da kuma dukan iyakokin duniya za su gani ceton Allahnmu.
11 Éloignez-vous, éloignez-vous, sortez de là; ne touchez à rien d'impur. Sortez du milieu de cette ville, tenez-vous à part, vous qui portez les vases du Seigneur.
Ku fita, ku fita daga can! Kada ku taɓa wani abu marar tsarki! Ku fita daga cikinta ku zama da tsarki, ku da kuke ɗaukan kayan aikin Ubangiji.
12 Car vous ne sortirez pas en tumulte; vous ne marcherez pas comme des fuyards. Le Seigneur marchera le premier devant vous; car c'est lui qui vous aura réunis; c'est le Dieu d'Israël.
Amma ba za ku fita a gaggauce ba ko ku tafi da gudu; gama Ubangiji zai ja gabanku, Allah na Isra’ila zai kasance mai tsaron bayanku.
13 Voilà que mon serviteur comprendra; et il sera élevé, et il montera au comble de la gloire.
Duba, bawana zai aikata abubuwa da hikima; za a tā da shi a kuma ɗaga shi da ɗaukaka ƙwarai.
14 Mais de même qu'à cause de toi beaucoup auront été dans la stupeur, de même ta forme sera sans honneur aux yeux des hommes, et ta gloire méprisée des fils des hommes.
Kamar dai yadda aka kasance da mutane masu yawa waɗanda suka giggice sa’ad da suka gan shi, kamanninsa ya lalace ƙwarai fiye da na kowane mutum siffarsa kuma ta yi muni fiye da yadda ta mutum take,
15 Et comme maintes nations s'étonneront de ses œuvres, les rois aussi se tiendront en silence; parce que ceux à qui rien de lui n'aura été annoncé verront, et ceux qui n'auront rien appris comprendront.
haka zai ba al’ummai masu yawa mamaki, sarakuna kuma za su riƙe bakunansu don mamaki. Gama abin da ba a faɗa musu ba, shi za su gani, kuma abin da ba su ji ba, shi za su fahimta.

< Isaïe 52 >