< Esdras 1 >

1 La première année de la domination de Cyrus, roi des Perses, la parole du Seigneur qu'avait proférée la bouche de Jérémie le prophète, devait s'accomplir; le Seigneur excita l'esprit de Cyrus, roi des Perses, et il envoya en tout son royaume une proclamation par écrit, disant:
A shekara ta farko ta mulkin sarkin Farisa, wato, sarki Sairus, domin a cika maganar Ubangiji da aka yi ta bakin Irmiya, sai Ubangiji ya taɓa zuciyar Sairus sarkin Farisa ya yi shela a duk fāɗin ƙasarsa, ya kuma rubuta cewa,
2 Voici ce qu'a dit Cyrus, roi des Perses: Le Seigneur Dieu du ciel m'a donné tous les royaumes de la terre, et lui-même a jeté les yeux sur moi pour que je lui bâtisse un temple à Jérusalem en Judée.
“Ga abin da Sairus sarkin Farisa yake shela, “‘Ubangiji Allah na sama ya ba ni iko in yi mulkin duniya duka, ya kuma zaɓe ni in gina masa haikali a Urushalima cikin Yahuda.
3 Qui donc, parmi vous tous, est de son peuple? Son Dieu sera avec lui, et il partira pour Jérusalem en Judée; qu'il y bâtisse le temple du Dieu d'Israël; le seul Dieu est celui qui réside à Jérusalem.
Duk wanda yake nasa a cikinku bari Allahnsa yă kasance tare da shi, bari yă tafi Urushalima cikin Yahuda yă gina haikalin Ubangiji, Allah na Isra’ila, Allah wanda yake a Urushalima.
4 Tous ceux de ce peuple qui vivent encore, en quelque lieu qu'ils habitent, les hommes de ce lieu les aideront de dons en argent, en or, en meubles, ou en bestiaux, outre ce qu'ils offriront volontairement pour le temple de Dieu à Jérusalem.
Duk inda akwai mutumin Yahuda da ya rage, sai mutanen da suke zama kusa da shi, su taimake shi da azurfa, da zinariya, da kaya, da kuma dabbobi, tare da kyautai na yardar rai saboda Gidan Allah wanda yake a Urushalima.’”
5 Alors, se levèrent les chefs de famille de Juda et de Benjamin, et les prêtres et les lévites, tous ceux que l'Esprit de Dieu excita à partir et à relever le temple du Seigneur à Jérusalem.
Sai shugabannin zuriyar Yahuda da na Benyamin, da firistoci da Lawiyawa, duk wanda Allah ya taɓa zuciyarsa, suka shirya don su je su gina haikalin Ubangiji a Urushalima.
6 Et tous ceux qui les entouraient leur fortifièrent les mains avec des vases d'argent, de l'or, des meubles, des bestiaux et des présents, outre les dons volontaires pour le temple.
Dukan maƙwabtansu kuwa suka taimake su da gudummawa na kayan azurfa da na zinariya, da kaya, da dabbobi, da kuma kyautai masu daraja bisa bayarwar yardar rai da suka yi.
7 Et le roi Cyrus offrit les vases du temple du Seigneur que Nabuchodonosor avait enlevés de Jérusalem, et qu'il avait dédiés au temple de son Dieu.
Sai sarki Sairus ya fitar da kayan da suke na haikalin Ubangiji waɗanda Nebukadnezzar ya kwashe daga Urushalima ya sa a haikalin allahnsa.
8 Cyrus, roi des Perses, les donna par la main de Mithradate le trésorier, et celui-ci les compta avec Sasabasar, chef de Juda.
Sairus sarkin Farisa ya sa Mitredat ma’aji ya ƙirga su a gaban Sheshbazzar ɗan sarkin Yahuda.
9 En voici le nombre: trente coupes d'or, mille d'argent, vingt-neuf de divers genres, trente coupes d'or,
Ga lissafin kayan. Manyan kwanonin zinariya guda 30 Manyan kwanonin azurfa guda 1,000 Wuƙaƙe guda 29
10 Quatre cent dix doubles coupes d'argent, et mille autres vases.
Waɗansu kwanonin zinariya guda 30 Waɗansu kwanonin azurfa guda 410 da waɗansu kayayyaki guda 1,000
11 Il y avait en tout cinq mille quatre cents vases d'or et d'argent qui furent emportés par Sasabasar, du lieu d'exil de Babylone, à Jérusalem.
Dukan kayayyakin zinariya da na azurfa sun kai 5,400. Sheshbazzar ya kawo kayayyakin nan duka tare da shi lokacin da kamammun suka hauro daga Babilon zuwa Urushalima.

< Esdras 1 >