< Deutéronome 9 >

1 Ecoute, Israël: tu vas traverser aujourd'hui le Jourdain, pour prendre le territoire de grandes nations beaucoup plus fortes que toi, et pour prendre de grandes villes, dont les remparts montent jusqu'au ciel,
Ku ji, ya Isra’ila. Kuna gab da haye Urdun, ku shiga, ku kuma kori al’ummai da suka fi ku yawa, suka kuma fi ku ƙarfi, masu manyan biranen da suke da katangar da suka yi tsaye zuwa sama.
2 Pour supplanter un peuple grand et nombreux, et de haute taille, les fils d'Enac, que tu connais; car, tu sais le proverbe: Qui résistera en face aux fils d'Enac?
Mutane ne masu ƙarfi, kuma dogaye, zuriyar Anakawa! Ai, kun ji akan ce, “Wa zai iya tsayayya da Anakawa?”
3 Et tu vas savoir que le Seigneur ton Dieu lui-même marchera à ta tête; ton Dieu est un feu consumant; c'est lui qui les exterminera, c'est lui qui les chassera loin de ta face, et il les détruira promptement, comme te l'a dit le Seigneur.
Amma ku zauna da sani a yau, cewa Ubangiji Allahnku, shi ne wanda ya ƙetare ya sha gabanku kamar wuta mai cinyewa. Zai hallaka su, zai rinjaye su a gabanku. Za ku kore su, ku kuma hallaka su nan da nan, yadda Ubangiji ya yi muku alkawari.
4 Garde-toi de dire en ton cœur, tandis que le Seigneur ton Dieu dissipera ces nations devant toi: C'est à cause de ma justice que le Seigneur m'a conduit, pour me donner en héritage cette terre fortunée. mais c'est à cause de l'iniquité de ces nations que le Seigneur détruira devant toi
Bayan Ubangiji Allahnku ya kore su a gabanku, kada ku faɗa a zuciyarku, “Ubangiji ya kawo mu a nan, mu mallaki wannan ƙasa saboda adalcinmu ne.” A’a, saboda muguntar waɗannan al’umma ne ya sa Ubangiji ya kore su a gabanku.
5 Non, ce n'est pas à cause de ta justice, ce n'est pas à cause de la sainteté de ton cœur que tu vas avoir leur terre pour héritage, mais c'est à cause de l'iniquité de ces nations que le Seigneur détruira devant toi, afin d'établir l'alliance que le Seigneur a jurée avec nos pères: Abraham, Isaac et Jacob.
Ba domin adalci ko mutuncinku ba ne ya sa za ku mallaki ƙasarsu; sai dai saboda muguntar al’umman nan ne ya sa Ubangiji Allahnku yana korinsu a gabanku don yă cika abin da ya rantse wa kakanninku, wato, Ibrahim, Ishaku da Yaƙub.
6 Tu connaîtras aujourd'hui que ce n'est point à cause de ta justice que le Seigneur ton Dieu te donne en héritage cette terre fortunée, à toi, peuple revêche que tu es.
Ku gane wannan, cewa ba domin adalcinku ba ne ya sa Ubangiji Allahnku yana ba ku wannan ƙasa mai kyau, ku mallaki, gama ku mutane masu taurinkai ne.
7 Souviens-toi, n'oublie point combien tu as irrité le Seigneur ton Dieu dans le désert, depuis le jour où vous êtes sortis d'Egypte, jusqu'à votre arrivée au lieu ou nous sommes; vous avez persévéré dans l'insoumission au Seigneur.
Ku tuna da wannan, kada kuma ku manta yadda kuka tsokane Ubangiji Allahnku, har ya yi fushi a hamada. Daga ranar da kuka bar Masar har sai da kuka isa nan, kuna ta tawaye wa Ubangiji.
8 En Horeb, vous avez irrité le Seigneur, et il s'est courroucé contre vous, au point de vouloir vous exterminer,
A Horeb, kun tayar wa Ubangiji har ya yi fushin da ya isa yă hallaka ku.
9 Comme j'étais monté sur la montagne pour prendre les tables de pierre, les tables de l'alliance que le Seigneur a faite avec vous; j'y restai quarante jours et quarante nuits, et je n'y mangeai pas de pain, et je n'y bus pas d'eau.
Sa’ad da na hau kan dutse don in karɓi allunan dutse, allunan alkawarin da Ubangiji ya yi da ku, na zauna a kan dutse yini arba’in da dare arba’in; ban ci abinci ba, ban sha ruwa ba.
10 Et Dieu me donna les deux tables de pierre, écrites du doigt du Seigneur; toutes les paroles que le Seigneur avait dites devant vous sur la montagne, au jour de l'Eglise, y étaient écrites.
Ubangiji ya ba ni alluna biyu wanda shi kansa ya yi rubutu da yatsarsa. A kansu akwai dukan umarnan Ubangiji da an furta muku a kan dutse a tsakiyar wuta, a ranar taron jama’a.
11 Le Seigneur me donna donc les deux tables de pierre, les tables de l'alliance, après quarante jours et quarante nuits.
A ƙarshen yini arba’in da dare arba’in ɗin, Ubangiji ya ba ni alluna biyu na dutse, allunan alkawari.
12 Et le Seigneur me dit: Lève-toi, et descends bien vite d'ici; car ton peuple, que tu as fait sortir d'Egypte, s'est égaré. Ils se sont promptement écartés de la voie que je leur ai marquée et ils se sont fait une image en fonte.
Sa’an nan Ubangiji ya faɗa mini, “Sauka daga nan da sauri, domin mutanenka waɗanda ka fitar da su daga Masar sun lalace. Sun juye da sauri daga abin da na umarce su, suka kuma yi zubin gunki wa kansu.”
13 Et le Seigneur me dit: Je te l'ai répété plus d'une fois: je connais, j'ai vu ce peuple; c'est un peuple revêche.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Na ga mutanen nan, su masu taurinkai ne sosai!
14 Laisse-moi donc les détruire, et j'effacerai leur nom sous le ciel, et je te mettrai à la tête d'une nation grande et forte, plus nombreuse que celle-ci.
Bar ni kawai, in hallaka su, in kuma shafe sunansu daga ƙarƙashin sama. Zan kuwa yi maka wata al’umma mafi ƙarfi da kuma masu yawa fiye da su.”
15 Je partis donc; je descendis de la montagne. Or, la montagne était enflammée, et lançait du feu jusqu'au ciel, et je tenais dans mes deux mains les deux tables du témoignage.
Saboda haka na juya, na sauko daga dutsen yayinda yake cin wuta. Allunan biyu na alkawarin kuma suna a hannuwana.
16 Et, quand je vis que vous aviez péché devant le Seigneur notre Dieu, que vous vous étiez fait une image en fonte, que vous vous étiez écartés de la voie où le Seigneur vous avait prescrit de marcher,
Sa’ad da na duba, sai na ga cewa kun yi zunubi wa Ubangiji Allahnku; kun yi wa kanku gunkin da kuka yi zubi a siffar ɗan maraƙi. Kun kauce da sauri daga hanyar da Ubangiji ya umarce ku.
17 Je saisis les deux tables, je les jetai de mes deux mains, et je les brisai devant vous;
Saboda haka na ɗauko alluna biyun na jefar da su daga hannuwana, na farfashe su a idanunku.
18 Et je priai devant le Seigneur une seconde fois, quarante jours et quarante nuits comme la première, et je ne mangeai pas de pain, et je ne bus point d'eau, et je priai pour tous vos péchés, pour le mal que vous aviez fait devant le Seigneur Dieu en l'irritant ainsi.
Sai nan da nan kuma na fāɗi rubda ciki a gaban Ubangiji, yini arba’in da dare arba’in; ban ci ba, ban sha ba, kamar yadda dā na yi, duka saboda zunubin da kuka aikata a gaban Ubangiji. Ta haka kuka tsokane shi don yă yi fushi.
19 Je suis encore effrayé du courroux, de la fureur que ressentait le Seigneur contre vous, au point de vouloir vous exterminer; or, en ce temps-là, le Seigneur m'exauça.
Na ji tsoron fushi da hasalar Ubangiji, gama ya yi fushin da ku da ya isa yă hallaka ku. Amma na yi roƙo a lokacin, Ubangiji kuwa ya saurare ni.
20 Mais il était courroucé contre Aaron, au point de vouloir l'exterminer; et, en ce temps-là, je priai aussi pour Aaron.
Ubangiji ya yi fushi sosai da Haruna, har ya yi niyya yă hallaka shi, amma a wannan lokaci, na yi addu’a saboda Haruna shi ma.
21 Et votre péché, le veau que tous aviez fabriqué, je le consumai dans le feu, je le pilai, après l'avoir battu et réduit en lames très-minces; je le réduisis en poudre, et je jetai cette poussière dans le torrent qui descend de la montagne.
Sa’an nan na ɗauki kayan zunubin da kuka yi, wato, gunkin ɗan bijimi, na ƙone shi da wuta, na farfashe shi, na niƙa shi liɓis, sai da ya zama kamar ƙura mai laushi, na zubar da ƙurar a cikin ruwan rafin da yake gangarowa daga dutse.
22 Ensuite, au lieu de l'embrasement, au lieu de la tentation, au lieu des sépulcres de la concupiscence, vous irritâtes encore le Seigneur.
Kun kuma sa Ubangiji ya yi fushi a Tabera, a Massa da kuma a Kibrot Hatta’awa.
23 Et lorsque le Seigneur vous fit sortir de Cadès-Barné, disant: Montez et prenez possession de la terre que je vous donne, vous fûtes encore indociles à la parole du Seigneur votre Dieu, vous n'eûtes point foi en lui, et vous n'obéîtes point à sa voix.
Sa’ad da Ubangiji ya aike ku daga Kadesh Barneya ya ce, “Ku haura ku mallaki ƙasar da na ba ku.” Amma kuka yi tawaye ga umarnin Ubangiji Allahnku. Ba ku amince da shi, ko ku yi masa biyayya ba.
24 Vous avez été désobéissants envers le Seigneur, à partir du jour où il s'est fait connaître à vous.
Kun yi ta tawaye wa Ubangiji tun ran da na san ku.
25 Et je priai devant le Seigneur quarante jours et quarante nuits, le même temps que la première fois, car le Seigneur menaçait de vous exterminer.
Na kwanta rubda ciki a gaban Ubangiji waɗannan yini arba’in da dare arba’in domin Ubangiji ya ce zai hallaka ku.
26 Et je priai Dieu, et je dis: Seigneur, roi des dieux, n'exterminez pas votre peuple, votre héritage que vous avez racheté, et que vous avez fait sortir de l'Egypte par votre grande force, par votre main puissante et votre bras très-haut.
Na yi addu’a ga Ubangiji na ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, kada ka hallaka mutanenka, gādon kanka, da ka fansa ta wurin ikonka mai girma, ka kuma fitar da su daga Masar da hannu mai ƙarfi.
27 Souvenez-vous d'Abraham, d'Isaac et de Jacob, vos serviteurs, à qui vous avez juré par vous-même; n'attachez point vos regards sur l'endurcissement de ce peuple, sur ses impiétés, sur ses péchés.
Ka tuna da bayinka Ibrahim, Ishaku da Yaƙub. Kada ka kula da taurinkan, mugunta da kuma zunubin wannan mutane.
28 Prenez garde que les habitants de la terre d'où vous l'avez fait sortir ne disent: C'est parce qu'il n'a pu les introduire dans la terre dont il leur avait parlé, c'est aussi parce qu'il les avait en haine, que le Seigneur les a conduits dans le désert afin de les faire périr.
In ba haka ba, ƙasar da ka fitar da mu, za tă ce, ‘Domin Ubangiji bai iya kai su cikin ƙasar da ya yi musu alkawari ba ne, kuma domin ya ƙi su, shi ya sa ya fitar da su ya kashe su a hamada.’
29 Ce peuple est votre peuple, votre héritage, vous l'avez fait sortir d'Egypte par votre grande force, votre main puissante et votre bras très-haut.
Amma su mutanenka ne, gādonka da ka fitar ta wurin ikonka mai girma, da kuma hannunka mai ƙarfi.”

< Deutéronome 9 >