< Deutéronome 27 >

1 Et Moïse, avec les anciens, continua de donner des ordres à Israël, et il dit: Observez tous les commandements que je vous intime aujourd'hui.
Musa tare da dattawan Isra’ila suka umarci mutane suka ce, “Ku kiyaye dukan umarnai da na ba ku a yau.
2 Le jour où tu auras traversé le Jourdain pour entrer en la terre que le Seigneur ton Dieu te donne, tu dresseras pour toi de grandes pierres que tu recrépiras de chaux.
Sa’ad da kuka haye Urdun zuwa cikin ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ku kakkafa waɗansu manyan duwatsu, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
3 Tu écriras ensuite sur ces pierres tous les articles de la loi, aussitôt que vous aurez tous franchi le Jourdain, et que vous serez entrés en la terre que le Seigneur Dieu de vos pères vous donne, terre où coulent le lait et le miel, comme le Seigneur l'a dit à vos pères.
Ku rubuta dukan waɗannan kalmomin doka a kansu, sa’ad da kuka haye kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, ƙasa mai zub da madara da zuma, kamar dai yadda Ubangiji Allah na kakanninku, ya yi muku alkawari.
4 Dès que vous aurez franchi le Jourdain, vous dresserez ces pierres dont je vous parle, sur le mont Hebal, puis vous les recrépirez de chaux,
Sa’ad da kuma kuka haye Urdun, ku kakkafa waɗannan duwatsu a bisa Dutsen Ebal, kamar yadda na umarce a yau, ku yi musu shafe da farar ƙasa.
5 Et vous bâtirez au même lieu un autel au Seigneur votre Dieu, un autel de pierres, où il n'entrera point de fer.
Ku gina bagade wa Ubangiji Allahnku, bagaden dutse. Kada ku yi amfani da wani kayan aiki na ƙarfe a kansu.
6 Vous le bâtirez de pierres sans défaut, et sur cet autel vous offrirez des holocaustes au Seigneur votre Dieu.
Ku gina bagaden Ubangiji Allahnku da duwatsun fili, ku kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kansa ga Ubangiji Allahnku.
7 Vous offrirez sur cet autel les hosties pacifiques; vous mangerez, vous vous rassasierez, et vous vous réjouirez devant le Seigneur votre Dieu.
Ku miƙa hadayun salama a can, kuna ci, kuna farin ciki a gaban Ubangiji Allahnku.
8 Et sur les pierres vous écrirez toute la loi, très- manifestement.
Za ku kuma rubuta a fayyace dukan kalmomin wannan doka a kan waɗannan duwatsun da kuka kakkafa.”
9 Et Moïse, avec les prêtres lévites, continua de parler à tout Israël, et il dit: Fais silence, écoute, Israël, aujourd'hui tu es devenu le peuple du Seigneur ton Dieu.
Sai Musa da firistoci waɗanda suke Lawiyawa suka ce wa dukan Isra’ila, “Ku yi shiru, ya Isra’ila, ku saurara! Yanzu kun zama mutanen Ubangiji Allahnku.
10 Et tu seras docile à la parole du Seigneur, tu exécuteras ses commandements et ses ordonnances, que je t'intime aujourd'hui.
Ku yi biyayya ga Ubangiji Allahnku, ku bi umarnansa da ƙa’idodin da nake ba ku a yau.”
11 Et ce jour-là même, Moïse donna des ordres au peuple, disant:
A wannan rana Musa ya umarce mutane,
12 Voici ceux qui se tiendront sur le mont Garizim, après avoir passé le Jourdain, pour bâtir le peuple: Siméon, Lévi, Juda, Issachar, Joseph, Benjamin.
Sa’ad da kuka haye Urdun, sai waɗannan kabilai su tsaya a bisa Dutsen Gerizim su sa wa jama’a albarka, wato, kabilar Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar, Yusuf da Benyamin.
13 Voici ceux qui se tiendront sur le mont Hébal, du côté de la malédiction: Ruben, Gad, Aser, Zabulon, Dan et Nephthali.
Waɗannan kabilai kuma za su tsaya a bisa Dutsen Ebal su furta la’ana, wato, kabilar Ruben, Gad, Asher, Zebulun, Dan da Naftali.
14 Et les lévites, parlant à haute voix, diront à tout Israël:
Lawiyawa za su karanta wa dukan mutanen Isra’ila da babbar murya su ce,
15 Maudit soit l'homme qui fera une image sculptée ou jetée en fonte, abomination du Seigneur, ouvrage de la main d'un artisan, et qui la placera en un lieu secret; et le peuple entier répondant, dira: Ainsi soit-il.
“La’ananne ne mutumin da ya sassaƙa siffa, ko ya yi zubin gunki, abar ƙyama ce ga Ubangiji, aikin hannu mai sana’a da aka kafa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
16 Maudit celui qui n'honore pas son père ou sa mère; et tout le peuple dira: Ainsi soit-il.
“La’ananne ne mutumin da ya ƙasƙantar da mahaifinsa ko mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
17 Maudit celui qui déplace les bornes de son voisin; et tout le peuple dira: Ainsi soit-il.
“La’ananne ne mutumin da ya gusar da dutsen da aka kafa don nuna shaidar iyaka.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
18 Maudit celui qui égare l'aveugle dans le chemin; et tout le peuple dira: Ainsi soit-il.
“La’ananne ne mutumin da ya karkatar da makaho daga hanya.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
19 Maudit celui qui fait dévier la justice à regard de l'étranger, de l'orphelin et de la veuve; et tout le peuple dira: Ainsi soit-il.
“La’ananne ne mutumin da ya yi rashin adalci ga baƙo, maraya ko gwauruwa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
20 Maudit celui qui a commerce avec la femme de son père, et soulève la couverture de son père; et tout le peuple dira: Ainsi soit-il.
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da matar mahaifinsa, gama ya ƙasƙantar da gadon mahaifinsa ke nan.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
21 Maudit celui qui a commerce avec une bête; et le peuple entier dira: Ainsi soit-il.
“La’ananne ne mutumin da ya yi jima’i da dabba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
22 Maudit celui qui a commerce avec la sœur de son père ou de sa mère; et le peuple entier dira: Ainsi soit-il.
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da’yar’uwarsa,’yar mahaifinsa ko’yar mahaifiyarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
23 Maudit celui qui a commerce avec sa fille; et tout le peuple dira: Ainsi soit-il. Maudit soit celui qui a commerce avec la sœur de sa femme; et tout le peuple dira: Ainsi soit-il.
“La’ananne ne mutumin da ya kwana da mahaifiyar matarsa.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
24 Maudit celui qui frappe son prochain dans une embuscade; et tout le peuple dira: Ainsi soit-il.
“La’ananne ne mutumin da ya kashe maƙwabcinsa a ɓoye.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
25 Maudit soit celui qui acceptera des présents pour condamner à mort et verser le sang innocent; et tout le peuple dira: Ainsi soit-il.
“La’ananne ne mutumin da ya karɓi cin hanci don yă kashe marar laifi.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”
26 Maudit tout homme qui ne persévèrera pas en tous les articles de cette loi, pour les mettre en pratique; et tout le peuple dira: Ainsi soit-il.
“La’ananne ne mutumin da bai yi na’am da kalmomin wannan doka ta wurin aikata su ba.” Sai dukan mutane su ce, “Amin!”

< Deutéronome 27 >