< 2 Samuel 17 >

1 Et Achitophel dit à Absalon: Je vais choisir douze mille hommes, et je partirai, et je poursuivrai David cette nuit.
Ahitofel ya ce wa Absalom, “Zan zaɓi mutum dubu goma sha biyu su fita a daren nan in fafari Dawuda.
2 Il sera fatigué, énervé, quand je l'attaquerai et le remplirai de trouble; tout le peuple qui l'entoure fuira, et je frapperai le roi dès qu'il sera seul.
Zan fāɗa masa sa’ad da yake cikin gajiya da karayar zuciya. Zan firgita shi, mutanen da suke tare da shi kuwa za su gudu. Sarki ne kaɗai zan kashe
3 Ensuite, je te ramènerai tout le peuple, et il te reviendra comme revient une épouse auprès de son mari; puisque tu n'en veux qu'à la vie d'un seul homme, tout le peuple sera en paix.
in dawo da dukan mutanen a gare ka. Mutuwar wanda kake nema zai zama dawowar duka; dukan mutanen ba za su cutu ba.”
4 Le conseil parut excellent à Absalon et à tous les anciens d'Israël.
Wannan shawara ta gamshi Absalom da dukan dattawan Isra’ila.
5 Et Absalon dit: Appelez Chusaï d'Arach; sachons ce que celui-là aussi pourra nous dire.
Amma Absalom ya ce, “A kira mini Hushai mutumin Arkitawan nan shi ma, mu ji abin da zai ce.”
6 Chusaï entra donc auprès d'Absalon, et Absalon lui dit: Voici comme a parlé Achitophel; ferons-nous ce qu'il a conseillé? Si ce n'est pas ton avis, parle à ton tour.
Da Hushai ya zo wurinsa, sai Absalom ya ce, “Ahitofel ya ba da wannan shawara. Mu yi abin da ya ce? In ba haka ba, sai ka ba mu ra’ayinka.”
7 Pour cette fois, répondit Chusaï, le conseil d'Achitophel n'est pas bon.
Hushai ya ce wa Absalom, “Shawarar da Ahitofel ya bayar a wannan lokaci kam, ba ta da kyau.
8 Et Chusaï ajouta: Tu connais ton père et ses hommes; ils sont très vaillants, et leur âme est pleine d'amertume. Ils ressemblent à l'ours à qui, dans les champs, on a enlevé ses petits, ou au sanglier hérissé de la plaine; ton père est un guerrier, et il ne laisse pas son armée prendre de repos.
Ka san mahaifinka da mutanensa mayaƙa ne, suna cikin fushi kamar mugun beyar da aka ƙwace mata’ya’ya. Ban da haka ma, mahaifinka gogagge ne a yaƙi; ba zai kwana da rundunar ba.
9 Maintenant, il est à couvert dans les montagnes ou dans quelque autre lieu, et vous ne l'aurez pas plutôt assailli qu'un bruit se répandra, et que l'on dira: Il y a eu un massacre de ceux qui suivent Absalon.
Kai, ko yanzu ma, ya riga ya ɓuya cikin kogo ko kuma a wani wuri. In har ya fara kai wa rundunarka hari duk wanda ya ji, zai ce, ‘An yi kaca-kaca da rundunar da suka bi Absalom.’
10 Et même le fils de la vaillance, dont le cœur est comme le cœur du lion, défaillira; car tout Israël sait que ton père est un homme vaillant, et qu'il est entouré de fils vaillants.
Kai, ko jarumi mai zuciya kamar na zaki ma, zai narke don tsoro, gama dukan Isra’ila sun sani mahaifinka mayaƙi ne, sun kuma san cewa waɗanda suke tare da shi jarumawa ne.
11 C'est pourquoi voici ce que je préfère de beaucoup: rassemble auprès de toi tout Israël, depuis Dan jusqu'à Bersabée, aussi nombreux que le sable du rivage de la mer; et mets-toi en campagne au milieu de, cette multitude.
“Saboda haka ina ba ka shawara, bari a tara maka dukan Isra’ila, daga Dan zuwa Beyersheba da yawansu ya yi kamar yashin bakin teku, kai kanka ka jagorance su zuwa fagen fama.
12 Alors, nous marcherons contre lui en l'un des lieux où nous pensons le trouver; nous tomberons sur lui à l'improviste, comme la rosée tombe sur la terre, et nous n'épargnerons ni lui ni un seul des hommes qui l'accompagnent.
Sa’an nan za mu fāɗa masa duk inda yake, za mu fāɗa masa kamar yadda raɓa takan fāɗo a bisa ƙasa. Da shi da mutanensa babu ko ɗaya da za a bari da rai.
13 Et s'il s'est réfugié avec ses gens en quelque ville, tout Israël apportera des câbles devant cette ville, et nous en entraînerons les débris jusqu'au torrent, afin qu'il n'en reste pas une pierre.
In ma ya janye zuwa cikin birni, sai dukan Isra’ila su kawo igiyoyi wa wannan birni, su ja shi zuwa kwari yă wargaje, yadda ba za a bar wani dutse a kan wani ba.”
14 Absalon et tout Israël s'écrièrent: Le conseil de Chusaï d'Arach vaut mieux que le conseil d'Achitophel. Et le Seigneur voulut que le sage dessein d'Achitophel fût confondu, afin que le Seigneur fit tomber sur Absalon toute sorte de maux.
Absalom da dukan mutanen Isra’ila suka ce, “Shawarar Hushai mutumin Arkitawa ta fi ta Ahitofel kyau.” Gama Ubangiji ya ƙudura yă wofinta kyakkyawar shawarar Ahitofel, don yă jawo wa Absalom masifa.
15 Et Chusaï d'Arach dit aux prêtres Sadoc et Abiathar: Voilà ce qu'avait conseillé Achitophel à Absalon et aux anciens du peuple; voilà ce que je leur ai conseillé.
Hushai ya ce wa Zadok da Abiyatar, firistoci, “Ahitofel ya ba wa Absalom da dattawan Isra’ila shawara su yi kaza da kaza, amma na ba su shawara su yi haka, su yi haka.
16 Maintenant, faites-le rapidement savoir à David; qu'on lui dise: Ne passe pas la nuit à Araboth dans le désert; hâte-toi de traverser le Jourdain, de peur que le roi et tous les siens ne périssent.
Yanzu sai ku aika wa Dawuda saƙo nan da nan ku ce masa, ‘Kada ka kwana a mashigai cikin hamada; ka tabbata ka haye ba faci, in ba haka ba sarki da dukan mutanensa za su hallaka.’”
17 Or, Jonathan et Achimaas étaient restés vers la fontaine de Rhogel; une servante y courut et leur transmit le message; eux-mêmes partirent pour le porter au roi David; car il n'était pas possible qu'on les eût vus entrer dans Jérusalem.
Yonatan da Ahimawaz suna zaune a En Rogel. Wata baranya ce za tă je ta faɗa musu, su kuma su tafi su gaya wa Sarki Dawuda don suna tsoro kada a ga suna shiga birnin.
18 Mais un jeune serviteur les vit en marche, et il l'alla rapporter à Absalon. Cependant, ils s'étaient hâtés, et ils étaient déjà dans la maison d'un homme de Bahurim, qui avait dans sa cour une citerne, où ils descendirent.
Amma wani saurayi ya gan su, ya gaya wa Absalom. Sai dukansu biyu suka tashi da sauri suka shiga gidan wani mutum a Bahurim. Yana da rijiya a cikin gida, sai suka shiga cikinta.
19 Alors, la femme de cet homme étendit une couverture sur l'orifice de la citerne; elle y mit sécher du blé, et la chose ne fut point découverte.
Matarsa mutumin kuwa ta kawo tabarma ta shimfiɗa a bakin rijiyar, sai ta kawo hatsi ta baza a kanta. Ba kuwa wanda ya san abin da ta yi.
20 Les serviteurs d'Absalon vinrent dans la maison vers la femme, et ils lui dirent Où sont Achimaas et Jonathan? Elle répondit: Ils ont passé un peu au delà du torrent. Et les serviteurs cherchèrent; et, ne les ayant pas trouvés, ils retournèrent à Jérusalem.
Da mutanen Absalom suka zo wurin matan a gidan, suka ce, “Ina Yonatan da Ahimawaz?” Matar ta ce, “Tuni, sun haye rafi.” Sai mutanen suka yi ta nemansu amma ba su ga kowa, sai suka koma Urushalima.
21 Lorsqu'ils se furent éloignés, les deux jeunes gens sortirent de leur citerne, s'en allèrent, et dirent tout à David; puis, ils ajoutèrent: Hâte- toi de traverser le fleuve, car voici le conseil qu'a donné contre toi Achitophel.
Bayan mutanen suka tafi, sai su biyun suka fito daga rijiyar suka je suka gaya wa Sarki Dawuda. Suka ce masa, “Maza ka ƙetare kogi; Ahitofel ya ba wa Absalom shawara a yi maka kaza da kaza.”
22 David se leva, ainsi que tout le peuple qui l'accompagnait; ils passèrent le Jourdain jusqu'au lever de l'aurore, et il n'y eut pas un seul des siens qui restât en deçà du fleuve.
Saboda haka Dawuda da dukan mutanen da suke tare da shi suka tashi suka ƙetare Urdun. Kafin wayewar gari, babu wanda ya rage da bai haye ba.
23 Quand Achitophel vit que son conseil n'était pas suivi, il bâta son ânesse, retourna en sa demeure dans sa ville, donna des instructions à sa famille, se pendit, et mourut; on l'ensevelit dans le sépulcre de son père.
Da Ahitofel ya ga ba a bi shawararsa ba, sai ya hau jakinsa ya koma gidansa a garinsu. Ya kintsa gidansa sa’an nan ya rataye kansa. Ta haka ya mutu, aka kuma binne shi a kabarin mahaifinsa.
24 Cependant, David passa en Manaïm, et Absalon franchit à son tour le Jourdain avec tout Israël.
Dawuda kuwa ya tafi Mahanayim. Absalom kuma ya ƙetare Urdun tare da dukan mutanen Isra’ila.
25 Et Absalon mit à la tête de l'armée, à la place de Joab, Amessaï, fils d'un homme qui se nommait Jéther le Jezraélite; celui-ci l'avait eu d'Abigail, fille de Naas, sœur de Sarvia, mère de Joab.
Absalom ya riga ya naɗa Amasa a kan sojoji a maimakon Yowab. Amasa kuwa ɗan wani mutum mai suna Itra ne, mutumin Ishmayel wanda ya auri Abigiyel,’yar Nahash,’yar’uwar Zeruhiya mahaifiyar Yowab.
26 Or, tout Israël et Absalon campèrent en la terre de Galaad.
Isra’ilawa da Absalom suka kafa sansani a ƙasar Gileyad.
27 Lorsque David était arrivé en Manaïm, Uesbi, fils de Naas, de Rhabbath, ville des fils d'Aramon, Machis, fils d'Amiel de Ladabar, et Berzelli le Galaadite, de Rhogellim,
Sa’ad da Dawuda ya zo Mahanayim, sai Shobi ɗan Nahash daga Rabba ta Ammonawa, da Makir ɗan Ammiyel daga Lo Debar, da Barzillai mutumin Gileyad daga Rogelim
28 Lui apportèrent dix tapis laineux des deux côtés, dix marmites, des vases d'argile, du froment, de l'orge, de la pâte, de la farine, des fèves, des lentilles,
suka kawo wa Dawuda da mutanensa tabarmai, da kwanoni, da kayayyakin da aka yi da yumɓu. Suka kuma kawo alkama da sha’ir, da gari, da soyayyen hatsi, da wake, da waken barewa,
29 Du miel, du beurre, des moutons et du fromage de vache; ils offrirent tout cela à David et au peuple qui l'accompagnait; car ils s'étaient dit: Ce peuple a faim, il est exténué et il souffre de la soif dans le désert.
da zuma, da kindirmo, da tumaki, da cukun madarar shanu wa Dawuda da mutanensa su ci. Gama sun ce, “Mutanen suna jin yunwa, sun kuma gaji, ga ƙishirwa a hamada.”

< 2 Samuel 17 >