< 2 Rois 11 >

1 Et Athalie, mère d'Ochosias, ayant vu que son fils était mort, détruisit toute la race royale.
Da Ataliya mahaifiyar Ahaziya ta ga ɗanta ya mutu, sai ta shiga hallaka dukan iyalin gidan sarauta.
2 Mais Josabeth, fille du roi Joram, sœur d'Ochosias, enleva Joas, fils de son frère; elle le déroba du milieu des fils du roi que l'on massacrait, et le mit, avec sa nourrice, dans une alcôve des chambres à coucher; puis, elle le cacha d'Athalie, et il ne fut point tué.
Amma Yehosheba,’yar Sarki Yoram,’yar’uwar Ahaziya, ta ɗauki Yowash ɗan Ahaziya daga cikin’ya’yan sarkin da ake shiri a kashe, ta ɓoye. Ta ɓoye shi daga Ataliya a wurin mai lura da shi a ɗakin kwana; don kada a kashe shi.
3 Il resta six ans caché avec elle dans le temple du Seigneur, pendant qu'Athalie régnait sur la terre.
Ya kasance a ɓoye, shi da mai lura da shi, a haikalin Ubangiji shekara shida yayinda Ataliya take mulkin ƙasar.
4 Dans la septième année, Joïada envoya des messagers, et convoqua les centeniers des gardes et des coureurs; il les emmena dans le temple du Seigneur, et il fit avec eux l'alliance du Seigneur; il leur fit prêter serment, leur montra le fils du roi,
A shekara ta bakwai sai Yehohiyada ya aika a kira komandodin sojoji ɗari-ɗari, da Keretawa, da matsara, ya sa aka kawo masa su a haikalin Ubangiji. Ya ƙulla yarjejjeniya da rantsuwa da su a haikalin Ubangiji, sa’an nan ya nuna musu ɗan sarki.
5 Et leur donna ses ordres, disant: Voilà ce que vous ferez. Le tiers de vos hommes, entrant en semaine, gardera la porte qui mène au palais du roi;
Ya umarce su cewa, “Ga abin da za ku yi sa’ad da kuka zo aiki a Asabbaci, ku raba kanku kashi uku. Kashi ɗaya za su yi gadin gidan sarki,
6 Un autre tiers gardera la porte de la grande rue, et le dernier tiers la porte derrière les coureurs; vous garderez tous le temple,
kashi ɗaya za su yi gadin Ƙofar Sur, kashi ɗaya kuma za su yi gadin ƙofar da take bayan’yan gadin fada. Dukan waɗannan ƙungiyoyi uku za su yi gadin fadan,
7 Et vous formerez deux troupes; tous ceux qui sortiront de semaine garderont aussi le temple du Seigneur auprès du roi.
ku kuma da kuke a sauran ƙungiyoyi biyu da kun saba hutu a Asabbaci, duk za ku yi gadin haikali don sarki.
8 Ils entoureront le roi les armes à la main; quiconque entrera dans les rangs mourra; ils ne quitteront pas le roi, soit qu'il entre, soit qu'il sorte.
Ku tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makaminsa a hannu. Duk wanda ya kusace ku, ku kashe shi. Ku manne wa sarki duk inda ya tafi.”
9 Et les centeniers firent tout ce que leur avait prescrit le sage Joïada. Chacun d'eux prit ses hommes; et ceux qui entraient en semaine se réunirent à ceux qui en sortaient, et ils s'introduisirent auprès de Joïada le prêtre.
Komandodin sojoji suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowa ya ɗauki mutanensa, waɗanda za su kama aiki Asabbaci da waɗanda za su kama hutun Asabbaci, suka zo wurin Yehohiyada firist.
10 Et le prêtre leur donna les épées et les lances du roi David qui étaient dans le temple du Seigneur.
Sai ya ba komandodin māsu da garkuwoyi da dā suke na Dawuda, waɗanda suke a cikin haikalin Ubangiji.
11 Et chacun des coureurs se tenait, les armes à la main, tant à droite qu'à gauche de l'autel, occupant les deux ailes du temple et entourant le roi.
Matsaran kuma kowa da makaminsa a hannu, suka tsaya kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikalin.
12 Alors, Joïada leur présenta le fils du roi Ochozias; il lui donna la couronne et le livre de la loi, il le proclama roi et il le sacra; et les assistants battirent des mains, et ils crièrent: Vive le roi!
Sai Yehohiyada ya fito da ɗan sarki ya sa masa rawani a kā; ya ba shi shafin alkawari, ya kuma furta shi sarki. Suka shafe shi da mai, mutane kuma suka yi ta tafi suka ihu, suna cewa, “Ran sarki yă daɗe.”
13 Et Athalie entendit la clameur de ceux du peuple qui couraient; elle entra, parmi le peuple, dans le temple du Seigneur.
Sa’ad da Ataliya ta ji surutun matsara da na mutane, sai ta tafi wurin mutanen a haikalin Ubangiji.
14 Elle vit le roi assis sur son trône selon la coutume; puis, autour de lui, les chanteurs, les trompettes. Et tout le peuple de la terre, plein de joie, sonnait de la trompette. Et Athalie déchira ses vêtements, et elle cria: Complot! complot!
Da ta duba sai ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙi, bisa ga al’ada. Hafsoshi da masu busa suna tsaye kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuma suna farin ciki suna busa ƙahoni. Sai Ataliya ta keta tufafinta ta tā da murya tana cewa, “Kai! Wannan cin amana ne! Ai, wannan cin amana ne!”
15 Et le prêtre Joïada donna ses ordres aux centeniers, chefs de l'armée; il leur dit: Entraînez-la hors des rangs; quiconque la suivra, mourra de mort par l'épée. Et le prêtre ajouta: Qu'elle ne meure point dans le temple du Seigneur.
Yehohiyada ya umarci komandodin sojoji waɗanda suke lura da mayaƙa, ya ce, “Ku fitar da ita daga cikinku, ku kuma kashe duk wanda ya bi ta.” Gama firist ɗin ya ce, “Kada a kashe ta a cikin haikalin Ubangiji.”
16 Ils mirent donc la main sur elle; et ils sortirent, prenant le chemin par où passaient les chevaux de la maison du roi, et là, ils la tuèrent.
Saboda haka suka kama ta yayinda ta kai inda dawakai sukan shiga filin fada, a can kuwa aka kashe ta.
17 Et Joïada fit alliance entre le Seigneur et le roi; puis, entre le Seigneur et le peuple, pour que le peuple demeurât le peuple de Dieu; puis, enfin, entre le roi et le peuple.
Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari tsakanin Ubangiji da sarki da kuma mutane cewa za su zama mutanen Ubangiji. Ya kuma yi alkawari tsakanin sarki da mutane.
18 Et tout le peuple de la terre entra dans le temple de Baal; ils le renversèrent, ils brisèrent ses autels et ses images, et ils tuèrent devant l'autel Mathan, prêtre de Baal. Ensuite, Joïada plaça des surveillants dans le temple du Seigneur.
Sai dukan mutanen ƙasar suka tafi haikalin Ba’al suka rushe shi. Suka farfasa bagadai da kuma gumaka, suka kuma kashe Mattan wanda yake firist na Ba’al a gaban bagade. Sa’an nan Yehohiyada firist ya sa matsara a haikalin Ubangiji.
19 Il se mit à la tête des centeniers, des gardes, des coureurs et de tout le peuple de la terre; ils emmenèrent le roi du temple du Seigneur, et ils prirent la rue de la porte des coureurs du roi, et ils le firent asseoir sur le trône royal.
Ya tafi tare da komandodin sojoji, Keretawa, matsara da kuma dukan mutanen ƙasar, tare kuwa suka kawo sarki daga haikalin Ubangiji zuwa cikin fada, ta ƙofar matsara. Sarki kuwa ya ɗauki mazauninsa a bisa kursiyin sarauta,
20 Et tout le peuple de la terre fut en joie; la ville resta calme; Athalie avait péri par l'épée dans le palais du roi.
dukan mutanen ƙasar suka yi murna. Birnin ya sami salama don an kashe Ataliya da takobi a fada.
21 Joas avait sept ans quand commença son règne.
Yowash yana da shekara bakwai sa’ad da ya fara mulki.

< 2 Rois 11 >