< 2 Rois 10 >

1 Il y avait alors en Samarie soixante-dix fils d'Achab: Jéhu écrivit une lettre qu'il envoya dans Samarie aux chefs, aux anciens de la ville et aux gardiens des enfants d'Achab; il leur disait:
To, akwai’ya’ya maza saba’in na gidan Ahab a Samariya. Saboda haka Yehu ya rubuta wasiƙu, ya aika su Samariya, zuwa ga shugabannin Yezireyel, da kuma ga masu lura da’ya’yan Ahab. Ya ce,
2 Aussitôt que cette lettre vous sera parvenue, vous qui avez avec vous les fils de votre maître, et des chars, et des forteresses, et des armes,
“Da zarar wasiƙan nan ta sadu da ku, da yake’ya’yan maigidanku suna tare da ku, kuna kuma da kekunan yaƙi da dawakai, da birni mai katanga da makamai,
3 Vous considèrerez quel est le meilleur et le plus droit des fils de votre maître, vous le placerez sur le trône de son père, et vous combattrez pour la maison de votre maître.
sai ku zaɓi mafi cancanta a cikin’ya’yan maigidanku ku sa shi a kan kursiyin mahaifinsa. Sa’an nan ku yi yaƙi don gidan maigidanku.”
4 Or, ils eurent crainte, et ils dirent: Si deux rois n'ont pu tenir devant lui, comment lui résisterons-nous?
Amma suka razana suka ce, “Idan sarakuna biyu ba su iya yin tsayayya da shi ba, wane mu?”
5 Et les chefs du palais, ceux de la ville, ainsi que les anciens et les gardiens des enfants, envoyèrent des messagers à Jéhu, disant: Nous aussi nous sommes tes serviteurs; tout ce que tu nous diras nous le ferons; nous ne proclamerons point de roi, nous ferons ce que bon te semblera.
Saboda haka sarkin fada, da gwamnan birnin, da dattawa, da kuma masu lura da’ya’yan suka aika da saƙo ga Yehu, cewa, “Mu bayinka ne, za mu kuma yi duk abin da ka ce. Ba za mu naɗa kowa sarki ba; sai ka yi abin da ka ga ya fi kyau.”
6 Jéhu leur écrivit une seconde lettre, où il disait: Si vous êtes à moi, si vous êtes dociles à mes ordres, prenez les têtes des hommes fils de votre maître, et apportez-les-moi demain, à pareille heure, en Jezraël. Or, les fils du roi étaient au nombre de soixante-dix, et les premiers de la ville les élevaient.
Sai Yehu ya sāke rubuta musu wasiƙa ta biyu, ya ce, “In a gefena kuke, to, sai ku yi biyayya da ni, ku fille kawunan’ya’yan maigidanku, ku kawo mini a Yezireyel war haka gobe.” To,’ya’yan sarki, su saba’in, suna tare da manyan birni waɗanda suke lura da su.
7 Dès que la lettre leur fut parvenue, ils prirent les fils du roi et ils les égorgèrent au nombre de soixante-dix. Puis, ils mirent les têtes dans des paniers, et ils les envoyèrent à Jéhu en Jezraël.
Sa’ad da wasiƙar ta iso, sai mutanen nan suka ɗauki dukan’ya’yan sarkin nan saba’in, suka kashe su, suka sa kawunansu cikin kwanduna, suka aika wa Yehu a Yezireyel.
8 Et le messager de Jéhu revint, et il fit son rapport, disant: Ils ont apporté les têtes des fils du roi. Et Jéhu dit: Faites-en deux monceaux, et laissez-les jusqu'à demain matin des deux côtés de la porte de la ville.
Da ɗan saƙon ya iso, sai aka ce wa Yehu, “Sun kawo kawunan’ya’yan sarki.” Sai Yehu ya ce, “Ku ajiye su kashi biyu a ƙofar gari har safiya.”
9 L'aurore parut, et il sortit; il s'arrêta, et il dit à tout le peuple: Vous êtes justes: voilà que je me suis révolté contre mon maître, je l'ai tué; mais qui donc à frappé tous ceux-ci?
Da gari ya waye, sai Yehu ya fita ya tsaya a gaban dukan jama’a ya ce, “Ba ku da laifi. Ni ne na ƙulla wa maigidana maƙarƙashiya, na kuma kashe shi, amma wa ya karkashe dukan waɗannan?
10 Vous le voyez, nulle des paroles que le Seigneur a dites contre la maison d'Achab ne devait tomber à terre; le Seigneur a exécuté tout ce qu'il nous avait dit par Elie, son serviteur.
Ku sani fa, ba kalmar da Ubangiji ya faɗa game da gidan Ahab da ba za tă cika ba. Ubangiji ya yi abin da ya alkawarta ta bakin bawansa Iliya.”
11 Et Jéhu extermina tout ce qu'il y avait encore de la maison d'Achab en Jezraël, et tous ses hommes éminents, tous ses amis et ses prêtres; pas un seul ne fut épargné.
Saboda haka Yehu ya kashe duk waɗanda suka rage na iyalin Ahab a Yezireyel, tare da dukan fadawansa da aminansa da firistocinsa, ba a bar masa kowa ba.
12 Puis, il se mit en marche pour Samarie; il était dans la maison des bergers, sur la route,
Sa’an nan Yehu ya nufi Samariya. Da ya kai Bet-Eked na Makiyaya,
13 Quand il rencontra les frères d'Ochozias, roi de Juda, et il leur dit: Qui êtes-vous? Ils répondirent: Nous sommes les frères d'Ochozias, et nous sommes partis pour saluer les fils du roi et les fils de la reine.
sai ya gamu da waɗansu daga dangin Ahaziya sarkin Yahuda, sai ya tambaye su, ya ce, “Ku, su wane ne?” Suka ce, “Mu dangin Ahaziya ne, mun kuma zo ne mu gai da iyalan sarki da kuma mahaifiyar sarauniya.”
14 Aussitôt, il dit: Prenez-les vifs. On les prit, et on les égorgea dans la maison des bergers: quarante-deux hommes! il n'en resta pas un seul.
Sai ya umarta ya ce, “A kama su da rai!” Aka kuwa kama su aka yayyanka kusa da rijiyar Bet-Eked, su arba’in da biyu. Ba a bar wani da rai ba.
15 Et, s'étant éloigné de ce lieu, il rencontra Jonadab, fils de Rhéchab; celui-ci le bénit, et Jéhu lui dit: Ton cœur est-il sincèrement avec le mien, comme mon cœur est avec le tien? Jonadab répondit: Il l'est. Jéhu reprit: S'il l'est, donne-moi la main. Jonadab lui donna la main, et Jéhu le fit monter à côté de lui sur son char.
Bayan ya bar wurin, sai ya gamu da Yehonadab ɗan Rekab wanda yake kan hanyarsa don yă sadu da shi. Sai Yehu ya gaishe shi, ya ce, “Ka amince da ni yadda na amince da kai?” Yehonadab ya ce, “I.” Yehu ya ce, “To, in haka ne ka ba ni hannunka.” Sai ya miƙa masa, Yehu kuwa ya ja shi cikin keken yaƙin.
16 Et il lui dit: Viens avec moi, tu verras mon zèle pour le Seigneur. Puis, il le fit asseoir sur le siège.
Yehu ya ce, “Zo tare da ni ka ga himmata saboda Ubangiji.” Sa’an nan ya sa suka tafi tare cikin keken yaƙinsa.
17 Et il entra dans Samarie, et il extermina tout ce qui restait d'Achab, jusqu'à ce qu'il l'eût effacé, selon la parole que le Seigneur avait dite par la bouche d'Elie.
Da Yehu ya isa Samariya, sai ya karkashe dukan sauran iyalin Ahab, ya hallaka su, bisa ga maganar da Ubangiji ya faɗa ta bakin Iliya.
18 Ensuite, Jéhu rassembla tout le peuple, et il leur dit: Achab a servi faiblement Baal, Jéhu le servira magnifiquement.
Sa’an nan Yehu ya tattara dukan jama’a ya ce musu, “Ahab ya bauta wa Ba’al kaɗan ne kawai; amma Yehu zai bauta masa sosai.
19 Maintenant donc, vous tous prophètes de Baal, convoquez ici tous ses serviteurs et tous ses prêtres, sans qu'il manque un seul homme, car je vais faire un grand sacrifice à Baal; quiconque se cachera sera mis à mort. Or, Jéhu usait d'artifice pour détruire tous les serviteurs de Baal.
Yanzu sai ku kira dukan annabawan Ba’al, dukan masu yin masa hidima da kuma dukan firistocinsa. Ku tabbata ba a manta da wani ba, gama zan yi wa Ba’al babbar hadaya. Duk wanda bai zo ba, a bakin ransa.” Amma Yehu yana wayo ne domin yă hallaka masu yi wa Ba’al sujada.
20 Il ajouta: Sanctifiez le sacerdoce de Baal. Et on fit une proclamation.
Yehu ya ce, “Ku kira jama’a don a girmama Ba’al.” Saboda haka suka yi shela.
21 Et Jéhu envoya des messagers en tout Israël, disant: Que de tous ses serviteurs, de tous ses prêtres, de tous ses prophètes, aucun ne fasse défaut, car je prépare un grand sacrifice. Celui qui ne viendra point ne restera pas en vie. Et tous les serviteurs de Baal vinrent, ainsi que tous ses prêtres et tous ses prophètes; il n'y eut pas un homme qui ne vînt. Et ils entrèrent dans le temple de Baal, et le temple de Baal fut rempli d'un bout à l'autre.
Sa’an nan ya aika saƙo ko’ina a Isra’ila, dukan masu yi wa Ba’al hidima kuwa suka tattaru, ba mutumin da bai zo ba. Suka yi cincirindo a haikalin Ba’al har sai da ya cika makil.
22 Et Jéhu dit au gardien des vêtements du temple: Apporte des robes pour tous les serviteurs de Baal. Et le gardien leur en donna.
Sai Yehu ya ce wa mai ajiyar tufafi, “Ka kawo riguna domin dukan masu yi wa Ba’al hidima.” Sai ya fito musu da riguna.
23 Et Jéhu, avec Jonadab, fils de Rhéchab, entra dans le temple de Baal, et il dit aux serviteurs de Baal: Cherchez, voyez s'il y a parmi vous des serviteurs du Seigneur, ou seulement des serviteurs de Baal.
Sa’an nan Yehu da Yehonadab ɗan Rekab, suka shiga haikalin Ba’al. Yehu ya ce wa masu yi wa Ba’al sujada, “Ku dudduba ku tabbatar cewa babu wani bawan Ubangiji a nan tare da ku, sai masu hidimar Ba’al kawai.”
24 Puis, il pénétra plus loin pour offrir l'encens et les holocaustes. Or, il avait aposté dehors quatre-vingts de ses hommes, leur disant: Celui qui laissera échapper l'un de ceux que je livre entre vos mains, paiera de sa vie celle qu'il aura sauvée.
Saboda haka suka shiga don su miƙa hadayu da kuma hadaya ta ƙonawa. To, Yehu ya riga ya ba wa mutane takwas wannan kashedi a waje cewa, “In waninku ya bar ɗaya daga cikin mutanen nan da nake danƙa a hannunku ya tsere, to, a bakin ransa.”
25 Après qu'il eut consumé l'holocauste, Jéhu dit à ses gardes et à ses officiers: Entrez, frappez-les, n'en laissez pas sortir un seul. Et ils les passèrent an fil de l'épée; ils les jetèrent sur le chemin; et, du temple de Baal, ils retournèrent à la ville.
Nan da nan sa’ad da Yehu ya gama yin hadayar, sai ya umarci masu gadin da hafsoshi, “Ku shiga ku karkashe su; kada ku bar wani yă tsere.” Saboda haka suka karkashe su da takobi. Masu gadin da hafsoshin suka wuwwurga gawawwakinsu waje, suka kuma shiga ciki cikin haikalin Ba’al ɗin,
26 Et ils emportèrent la colonne de Baal, et ils la brûlèrent.
suka fitar da dutsen tsafi daga haikalin Ba’al, suka kuma ƙone shi.
27 Ils abattirent les colonnes de Baal, et, du temple, ils firent des latrines, qui existent encore de nos jours.
Suka farfasa dutsen tsafin Ba’al, suka kuma rushe haikalin, mutane suka mai da wurin salga har yă zuwa yau.
28 Jéhu effaça Baal de la terre d'Israël.
Ta haka Yehu ya hallaka butar Ba’al a Isra’ila.
29 Seulement, il ne se retira pas du péché de Jéroboam, fils de Nabat, du péché où il avait fait tomber Israël; il conserva les génisses d'or de Béthel et de Dan.
Duk da haka, bai rabu da zunuban Yerobowam ɗan Nebat, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba, wato, yin sujada ga siffofin maruƙa na zinariya a Betel da kuma Dan.
30 Le Seigneur dit à Jéhu: En récompense de ce que tu as fait d'agréable à mes yeux, de ce que tu as traité selon mon cœur la maison d'Achab, tes fils régneront sur Israël jusqu'à la quatrième génération.
Ubangiji ya ce wa Yehu, “Tun da yake ka aikata abin da yake mai kyau a idanuna, ka kuma yi wa gidan Ahab dukan abin da yake a zuciyata, ina yin maka alkawari cewa zuriyarka za su yi mulkin Isra’ila har tsara ta huɗu.”
31 Mais Jéhu ne fut pas attentif à marcher de tout son cœur selon la loi du Seigneur Dieu d'Israël; il ne se retira pas du péché de Jéroboam, du péché où il avait fait tomber tout le peuple.
Duk da haka, Yehu bai mai da hankali ya kiyaye dokokin Ubangiji, Allah na Isra’ila da dukan zuciyarsa ba. Bai rabu da zunubin Yerobowam, wanda ya sa Isra’ila ta aikata ba.
32 Et, en ces jours-là, le Seigneur commença de châtier Israël; Azaël le vainquit sur toutes ses frontières,
A kwanakin sai Ubangiji ya fara rage girman Isra’ila, Hazayel ya yi nasara a bisa Isra’ila a ko’ina a yankinsu
33 Jusqu'à la rive orientale du Jourdain; il envahit toute la terre de Galaad, savoir: les tribus de Gad et de Ruben, et le territoire de Manassé, à partir d'Aroer, qui est sur les bords du torrent d'Anion, et Galaad et Basan.
gabas da Urdun, cikin dukan ƙasar Gileyad (yankin Gad, da na Ruben, da na Manasse), daga Arower wajen Kwarin Arnon ya ratsa Gileyad zuwa Bashan.
34 Quant au reste de l'histoire de Jéhu, aux actions qu'il fit en sa puissance et à ses combats, ne sont-ils pas écrits au livre des Faits et gestes des rois d'Israël?
Game da sauran ayyukan mulkin Yehu, da dukan abin da ya yi, a rubuce suke a cikin littafin tarihin sarakunan Isra’ila.
35 Et Jéhu s'endormit avec ses pères; on l'ensevelit en Samarie, et son fils Joachaz régna à sa place.
Yehu ya huta tare da kakanninsa, aka binne shi a Samariya. Yehoyahaz kuma ya ci sarauta bayansa.
36 Jéhu avait régné vingt ans sur Israël en Samarie.
Yehu ya yi sarautar Isra’ila a Samariya shekara ashirin da takwas.

< 2 Rois 10 >