< 1 Samuel 9 >

1 Et il y avait parmi les fils de Benjamin un homme appelé Cis, fils d'Abiel, fils de Jared, fils de Bachir, fils d'Aphec, fils d'un puissant Jéminéen. C'était un homme puissant et fort.
An yi wani mutum, attajiri daga kabilar Benyamin, sunansa Kish, ɗan Abiyel, jikan Zeror na iyalin Bekorat daga dangin Afiya.
2 Il avait un fils dont le nom était Saül, homme de grande taille, bon et vaillant; nul des fils d'Israël n'était meilleur que lui, et il dépassait de toute la tête tout le reste du peuple.
Yana da ɗa mai suna Shawulu, wani kyakkyawan saurayi. A cikin mutanen Isra’ila ba wanda ya fi shi kyau, ya kuma fi kowa tsaye.
3 Les ânesses de Cis, père de Saül, s'étaient égarées; et Cis dit à Saül, son fils: Prends avec toi l'un des serviteurs; partez, et cherchez les ânesses.
To, ana nan sai jakunan Kish mahaifin Shawulu suka ɓace. Kish ya ce wa ɗansa, “Tashi ka tafi tare da wani daga cikin bayi, ku nemo jakunan.”
4 Ils traversèrent les montagnes d'Ephraïm; ils traversèrent le territoire de Selcha, et ils ne trouvèrent rien; ils traversèrent le territoire de Ségalim, les ânesses n'y étaient pas; ils traversèrent le territoire de Jamin, et ils ne trouvèrent rien encore.
Suka bi ta ƙasar tudu ta Efraim, suka ratsa ta ƙasar Shalisha amma ba su same su ba. Suka bi ta ƙasar Shalim, a can ma ba su same su ba sai suka bi ta ƙasar Benyamin, a can ma ba su same su ba.
5 Comme ils passaient près de Siph, Saül dit au serviteur qui l'accompagnait: Viens, retournons chez nous, de peur que mon père ne s'inquiète plus de nous que des ânesses.
Da suka iso gunduman Zuf, sai Shawulu ya ce wa bawan da yake tare da shi, “Zo mu koma kada mahaifina yă bar damuwa a kan jakuna, yă shiga damuwa game da mu.”
6 Le serviteur lui répondit: Écoute, il y a en cette ville un homme de Dieu, un homme renommé; tout ce qu'il prédit arrive. Allons-y donc, afin qu'il nous fasse connaître la voie que nous devons prendre.
Amma bawan ya amsa ya ce, “Duba, a wannan gari akwai wani mutumin Allah, ana ganin girmansa ƙwarai kuma duk abin da ya faɗa yakan zama gaskiya. Mu tafi can wurinsa wataƙila zai gaya mana hanyar da za mu bi.”
7 Et Saül dit au serviteur qui l'accompagnait: Je le veux bien, nous irons; mais que porterons-nous à l'homme de Dieu? Il ne nous reste plus rien du pain que nous avions emporté dans nos valises, et nous n'avons rien à offrir à l'homme de Dieu.
Shawulu ya ce wa bawan, “Idan muka isa can, me za mu ba wa mutumin? Ga shi abinci guzurinmu duk ya ƙare, ba mu da wani abin da za mu kai wa mutumin Allahn nan. Me muke da shi?”
8 Le serviteur répondit à Saül, et il lui dit: Je trouve à l'instant sous ma main un quart de sicle d'argent; tu le donneras à l'homme de Dieu, et il nous fera connaître notre chemin.
Bawan ya sāke ce masa, “Duba ina da kwatar azurfar da zan ba wa mutumin Allah don yă gaya mana wace hanya ce za mu bi.”
9 Or, jadis en Israël, tout homme qui allait consulter Dieu, disait: Allons chez le voyant, parce que jadis le peuple donnait au prophète le nom de voyant.
(A dā a Isra’ila, in wani yana so yă nemi nufin Allah, mutumin yakan ce, “Zo mu tafi wajen mai duba.” Gama wanda ake ce da shi annabi a yanzu, a dā ana kiransa mai duba ne.)
10 Saül dit donc à son serviteur: Ton conseil est bon, allons-y. Et ils allèrent à la ville où demeurait l'homme de Dieu.
Shawulu ya ce wa bawansa, “Madalla, zo mu tafi.” Sai suka kama hanya suka nufi birnin da mutumin Allah yake.
11 Comme ils gravissaient le coteau qui monte à la ville, ils rencontrèrent des jeunes filles qui venaient de puiser de l'eau, et ils leur dirent: Le voyant est-il là?
Sa’ad da suke haura tudun zuwa birnin, sai suka sadu da waɗansu’yan mata sun fito za su ɗiban ruwa. Sai suka tambaye su, suka ce, “Mai duba yana nan?”
12 Les jeunes filles leur répondirent: Il y est; le voici devant vous; il est venu à la ville à cause du jour, parce qu'aujourd'hui il y a pour le peuple un sacrifice en Bama.
’Yan matan suka ce, “I, yana nan, ai, ga shi ma a gabanku, ku hanzarta. Shigowarsa ke nan a garin, domin yau mutane za su ba da sadaka a bagade a kan tudu.
13 Lorsque vous serez entrés dans la ville, vous l'y trouverez encore avant qu'il soit monté en Bama pour manger. Le peuple ne mangera pas qu'il ne soit arrivé, car c'est lui qui bénit le sacrifice; après cela, les invités mangent. Montez donc; pendant toute cette journée vous êtes sûrs de le trouver.
Da zarar kun shiga garin, za ku same shi kafin yă tafi cin abinci a wurin yin sadakar, can kan tudu. Gama jama’a ba za su ci ba, sai ya kai can ya sa albarka a sadakar, sa’an nan waɗanda aka gayyata su ci. Ku haura da sauri, za ku same.”
14 Et ils montèrent à la ville; ils étaient déjà au centre de la ville, quand Samuel sortit pour monter en Barra, et ils le rencontrèrent.
Suka haura zuwa birnin, da shigarsu sai ga Sama’ila ya nufo su a hanyarsa ta zuwa kan tudu.
15 La veille de l'arrivée de Saül, le Seigneur l'avait annoncée à Samuel, en disant:
Kafin zuwa Shawulu, Ubangiji ya riga ya bayyana wa Sama’ila ya ce,
16 A pareille heure, demain, j'enverrai auprès de toi un homme de la tribu de Benjamin; tu l'oindras comme roi de tout mon peuple; et il sauvera Israël des mains des Philistins, car j'ai considéré l'abaissement de mon peuple, ses cris sont venus jusqu'à moi.
“Gobe war haka zan aiko maka da wani mutum daga ƙasar Benyamin. Ka keɓe shi shugaban mutanena Isra’ila. Shi zai cece mutanena daga hannun Filistiyawa. Na ga azabar mutanena gama kukansu ya hauro wurina.”
17 Quand Samuel vit Saül, le Seigneur lui dit: Voici l'homme dont je t'ai parlé; c'est lui qui règnera sur mon peuple.
Da Sama’ila ya hangi Shawulu, Ubangiji ya ce masa, “Ga mutumin da na yi maka magana, shi ne zai bi da mutanena.”
18 Et Saül aborda Samuel, au milieu de la ville, et il lui dit: Indique-moi la maison du voyant.
Shawulu ya sami Sama’ila a hanyar shiga gari, sai ya tambaye shi ya ce, “Ina roƙonka ka nuna mini gidan mai duba?”
19 Samuel répondit à Saül, et il lui dit: Je suis le voyant, monte devant moi en Bama; mange aujourd'hui avec moi; demain, je te congédierai, et je te dévoilerai tout ce qui est en ton cœur.
Sama’ila ya ce, “Ni ne mai duban, ka yi gaba zuwa ka tudu, gama yau za ka ci tare da ni, da safe kuma in sallame ka, in gaya muku duk abin da yake a zuciyarku.
20 Ne songe plus aux ânesses qui étaient perdues il y a trois jours; elles sont retrouvées. Et à qui donc seront les choses précieuses d'Israël, si ce n'est à toi et à la maison de ton père?
Game da jakunan da suka ɓace kwana uku kuwa, kada ka damu, an same su. Ga wane ne Isra’ila ta sa dukan zuciya, in ba ga kai da kuma dukan iyalin mahaifinka ba?”
21 Saül répondit, et il dit: Ne suis-je pas des fils de Jéminée, du moindre des cantons d'une tribu d'Israël, du moindre principat de tout Benjamin? Pourquoi m'adresses-tu de telles paroles?
Shawulu ya ce, “Ashe, ni ba mutumin Benyamin ba ne daga ƙaramar kabila ta Isra’ila? Dangina kuma ba shi ba ne mafi kakanni a cikin kabilar Benyamin ba? Yaya za ka faɗa mini irin wannan magana.”
22 Et Samuel prit Saül avec son serviteur, il les introduisit en Rama dans la salle du festin; il leur donna place parmi les premiers des convives, qui étaient environ soixante-dix.
Sa’an nan Sama’ila ya shiga da Shawulu da baransa ya zaunar da su a gaban waɗanda aka gayyata, mutanen sun kai wajen mutum talatin.
23 Et Samuel dit au cuisinier: Apporte-moi l'épaule que je t'ai donnée, et que je t'ai dit de garder chez toi.
Sama’ila ya ce wa mai dahuwa, “Kawo naman da na ba ka, wannan da na ce ka ajiye dabam.”
24 Le cuisinier avait fait cuire l'épaule, il la plaça devant Saül, et Samuel lui dit: Voilà ce qui t'est réservé; prends cette épaule et mange, car on l'a mise auprès de toi pour qu'elle soit un témoignage de préférence aux yeux de tous les autres; coupe et mange. Ce jour-là donc, Saül mangea avec Samuel.
Sai mai dahuwan ya ɗauko cinya da abin da yake bisanta ya kawo ya ajiye a gaban Shawulu. Sama’ila ya ce, “Ga abin da aka ajiye dominka. Ka ci, gama an keɓe shi dominka saboda wannan hidima daga lokacin da na ce, ‘Na gayyaci baƙi.’” Shawulu kuwa ya ci tare da Sama’ila a ranan nan.
25 Ensuite, il revint du haut lieu à la ville, où l'on fit pour Saül un lit sur la terrasse, et il y dormit.
Bayan suka gangaro daga tudu zuwa cikin gari, Sai Sama’ila ya yi magana da Shawulu a ɗakin samansa.
26 Lorsque le jour vint à poindre, Samuel appela Saül sur la terrasse, disant: Lève-toi, et je te congédierai. Saül se leva, il sortit avec Samuel, et ils passèrent les portes de la ville.
Da asuba sai suka tashi, Sama’ila ya kira Shawulu daga ɗakin sama ya ce, “Ka shirya, zan sallame ka.” Da Shawulu ya shirya, sai Sama’ila da Shawulu suka fita waje tare.
27 Comme ils descendaient le coteau, Samuel dit à Saül: Ordonne à ton serviteur de s'en aller devant nous, et arrête-toi, afin qu'aujourd'hui tu entendes la parole du Seigneur.
Suna dab da ƙarshen gari, sai Sama’ila ya ce wa Shawulu, “Ka ce wa bawanka yă yi gaba, kai ka ɗan dakata a nan tukuna, domin in ba ka saƙo daga Allah.”

< 1 Samuel 9 >