< 1 Samuel 20 >

1 Et David s'enfuit de Navath en Rhama; il alla trouver Jonathan, et il lui dit: Qu'ai-je fait? Quelle est ma faute? En quoi ai-je péché contre ton père, pour qu'il en veuille à ma vie?
Sai Dawuda ya gudu daga Nayiwot a Rama ya je wurin Yonatan ya ce, “Me na yi? Wane laifi ne na yi? Ta wace hanya ce na yi wa mahaifinka laifi har da yake neman yă kashe ni?”
2 Et Jonathan lui dit: Éloigne cette pensée: tu ne mourras point. Vois donc, mon père ne fait aucune chose, petite ou grande, sans me la confier; pourquoi me cacherait-il ce dessein? Cela ne peut être.
Yonatan ya ce, “Faufau, ba za ka mutu ba! Ka ji nan, mahaifina ba ya yin kome ba tare da ya shawarce da ni ba. Me ya sa ya ɓoye mini wannan? Ba zai yiwu ba.”
3 David répondit à Jonathan: Ton père n'ignore pas que j'ai trouvé grâce devant tes yeux, et il s'est dit: Ne faisons point connaître ce dessein à Jonathan, de peur qu'il ne refuse d'y consentir; mais vive le Seigneur et vive ton âme! ce que je t'ai dit est vrai; il n'y a plus d'intervalle entre moi et la mort.
Sai Dawuda ya rantse ya ce, “Mahaifinka ya san cewa, na sami tagomashi a gare ka, domin haka ba zai sanar maka da wannan ba, don kada yă baƙanta maka rai. Na rantse da Ubangiji, da kai kuma, taki ɗaya kaɗai ya rage tsakanina da mutuwa.”
4 Jonathan repartit: Que désire ton âme, et que ferai-je pour toi?
Sai Yonatan ya ce, “Duk abin da kake so in yi maka zan yi.”
5 Et David reprit: C'est demain la nouvelle lune; je ne m'assoirai point pour manger, tu me feras sortir, et je me cacherai dans les champs jusqu'au soir.
Dawuda ya ce, “Gobe fa shi ne Bikin Sabon Wata, ya kamata in ci tare da sarki amma bari in tafi fili in ɓuya har jibi da yamma.
6 Et, si ton père me cherche, tu lui diras: David m'a demandé avec instance de courir jusqu'à Bethléem, sa ville, parce que toute sa tribu y fait le sacrifice du jour.
In mahaifinka bai gan ni ba, ka gaya masa cewa, ‘Dawuda ya nemi izinina domin yă hanzarta yă tafi garinsa a Betlehem saboda ana hadaya ta shekara-shekara don dukan zuriyarsa.’
7 Et s'il répond: C'est bien, ton serviteur aura retrouvé la paix; mais s'il te répond durement, crois que le mal en lui touche à sa consommation.
In ya yi na’am, to, bawanka ya tsira. Amma in ka ga ya damu, to, ka tabbata ya yi niyya yă kashe ni.
8 Tu seras donc miséricordieux envers ton serviteur, parce qu'entre lui et toi tu as voulu que soit faite l'alliance de Dieu. Mais s'il est quelque iniquité en ton serviteur, mets-le toi-même à mort; car, en ce cas, qu'est-il besoin que tu me conduises jusqu'à ton père?
Kai kuma, ka nuna alheri ga bawanka, gama ka riga ka yi yarjejjeniya da ni a gaban Ubangiji, in kuwa na yi laifi ne sai ka kashe ni da kanka. Don me za ka bashe ni ga mahaifinka?”
9 Jonathan répondit: Éloigne cette pensée car si je reconnais que mon père va consommer quelque méchanceté contre toi, quand même ce serait ailleurs qu'en ta ville, je te le dirai.
Yonatan ya ce, “Labudda! In na ji ƙishin-ƙishin, cewa mahaifina yana neman yă kashe ka ashe, ba zan gaya maka ba?”
10 Et David reprit: Qui m'apprendra si ton père a répondu durement?
Dawuda ya ce, “Wa zai gaya mini idan mahaifinka ya amsa maka da amsa marar daɗi?”
11 Jonathan lui dit: Pars et attends-moi aux champs. Or bientôt, tous les deux se retrouvèrent dans les champs.
Yonatan ya ce, “Zo mu fita zuwa fili.” Sai suka tafi tare.
12 Et Jonathan dit à David: Le Seigneur Dieu d'Israël sait que, selon l'opportunité, je sonderai les sentiments de mon père avant trois jours; s'il est bien disposé pour toi, je ne t'enverrai personne aux champs.
Sai Yonatan ya ce wa Dawuda, “Na yi rantse da Ubangiji, Allah na Isra’ila cewa war haka jibi, zan yi ƙoƙari in ji daga mahaifina, idan ya yi magana mai kyau game da kai, zan gaya maka.
13 Si tu as à craindre quelque mal, que Dieu me punisse et me punisse encore, si je ne te le dévoile pas; alors, je te ferai échapper, tu t'en iras en paix; et le Seigneur sera avec toi, comme il était avec mon père.
Amma in mahaifina ya sa zuciya yă cuce ka, Ubangiji yă hukunta ni da hukunci mai tsanani in ban gaya maka ba, in kuma sa ka ka tafi lafiya. Ubangiji yă kasance tare da kai kamar yadda ya kasance da mahaifina.
14 Si je suis encore vivant, tu seras miséricordieux pour moi, et si je meurs,
Amma ka nuna mini alheri marar ƙarewa iri ta Ubangiji dukan rayuwata don kada a kashe ni.
15 Ni toi ni les tiens ne priverez ma famille de votre miséricorde à jamais. Oui, si je ne t'avertis; lorsque le Seigneur fera disparaître un à un de la face de la terre les ennemis de David,
Kada kuma ka yanke alherinka ga iyalina ko da Ubangiji ya hallaka dukan maƙiyin Dawuda a duniya.”
16 Que le nom de Jonathan se trouve du nombre, et que le Seigneur punisse les ennemis de David.
Saboda haka Yonatan ya yi yarjejjeniya da gidan Dawuda cewa Ubangiji yă kawo dukan maƙiyin Dawuda ga mutuwa.
17 Et Jonathan réitéra le serment qu'il avait prêté à David, parce qu'il aimait du fond de l'âme celui qui l'aimait tant lui-même.
Yonatan kuwa ya sa Dawuda ya sāke tabbatar masa rantsuwansa game da abokantakarsa da shi, gama yana ƙaunar Dawuda kamar ransa.
18 Et Jonathan dit: Demain nouvelle lune, on te cherchera, et l'on examinera ton siège.
Sai Yonatan ya gaya wa Dawuda cewa, “Gobe ne Bikin Sabon Wata, za a rasa ka, da yake kujerarka za tă kasance ba kowa a kai.
19 Tu attendras trois jours attentif à toutes choses, et tu te tiendras où tu te retires habituellement dans les jours de travail, près de la roche d'Ergab.
Jibi wajajen yamma, ka tafi wurin da ka ɓuya lokacin da wannan matsala ta fara, ka tsaya kusa da dutsen Etsel.
20 Et moi, je lancerai trois fois des flèches dans la direction d'Amattari.
Zan harbi kibiya uku ta wajen, sai ka ce dai ina harbin baka.
21 Et j'enverrai un jeune serviteur, disant: Va, retrouve-moi ma flèche. Et si je lui dis: Voici la flèche [à ta droite ou à ta gauche], ramasse-la; toi, David, tu pourras approcher, la paix est avec toi, il n'y a rien à craindre, vive le Seigneur!
Sa’an nan zan aiki yaro in ce masa, ‘Je ka nemo kibiyoyin.’ In na ce masa, ‘Duba, kibiyoyin suna wannan gefen da kake, kawo su,’ sai ka fito, wato, tabbatacce muddin Ubangiji yana raye, ka tsira, ba wani hatsari.
22 Mais si je dis au jeune homme: Voilà la flèche plus loin devant toi; pars, le Seigneur t'envoie plus loin.
Amma in na ce wa yaron, ‘Duba, kibiyoyin suna gaba da kai,’ sai ka tafi, gama Ubangiji ya sallame ka.
23 Je prends à témoin le Seigneur à jamais de ce que nous venons de nous dire.
Game da al’amarin da muka tattauna da ni da kai kuwa, ka tuna fa Ubangiji ne shaida tsakanina da kai har abada.”
24 Et David se cacha dans le champ, et il y eut une nouvelle lune, et le roi se mit à table pour manger.
Dawuda ya tafi ya ɓuya a fili. Sa’ad da ranar Bikin Sabon Wata ta zo, sarki ya zauna don yă ci.
25 Il s'assit comme d'habitude sur son siège qui était appuyé au mur; il avait passé avant Jonathan, et Abner s'assit à côté de Saül; or, la place du fils de Jessé était vide.
Ya zauna a kujeransa inda ya saba zama kusa da bango yana fuskantar Yonatan, Abner kuma ya zauna kusa da sarki. Amma kujeran Dawuda ba kowa.
26 Saül, ce jour-là, ne dit rien, ayant cette pensée: C'est évidemment la marque qu'il n'est point pur, parce qu'il ne s'est point purifié.
Shawulu bai ce kome ba a ranar domin ya yi tsammani wataƙila wani abu ya faru da Dawuda ya mai da shi marar tsarki, tabbatacce ba shi da tsarki.
27 Vint ensuite le lendemain de la pleine lune, le second jour, et la place du fils de Jessé était vide. Ce que voyant Saül, il dit à Jonathan, son fils: Pourquoi David ne s'est-il pas mis à table hier ni aujourd'hui?
Amma kashegari, rana ta biyu ga wata, kujeran Dawuda kuma ba kowa, sai Shawulu ya ce wa ɗansa Yonatan, “Me ya sa ɗan Yesse bai zo cin abinci, jiya da yau ba?”
28 Jonathan répondit: David m'a demandé d'aller jusqu'à Bethléem, sa ville;
Yonatan ya ce, “Dawuda ya nemi izinina don yă tafi Betlehem.
29 Il m'a dit: Permets-le-moi, je t'en conjure; parce que toute notre tribu offre dans la ville un sacrifice; mes frères m'ont invité; maintenant donc, si j'ai trouvé grâce devant tes yeux, j'irai et je verrai mes frères. Voilà pourquoi il ne s'est point assis à la table du roi.
Ya ce, ‘Bari in tafi gama iyalinmu suna miƙa hadaya a gari,’yan’uwana kuwa sun gayyace ni in kasance a can. In na sami yardarka, bari in tafi in ga’yan’uwana.’ Dalilin ke nan da bai zo ci da sarki ba.”
30 Et Saül s'enflamma de colère contre Jonathan; il lui dit: Fils de filles éhontées, ne savais-je pas que tu étais l'associé du fils de Jessé, à ta honte et à la honte de ta mère?
Fushin Shawulu ya ƙuna a kan Yonatan, sai ya ce masa, “Kai shege ne, haihuwar banzan mace; ai, na san kana goyon bayan ɗan Yesse don ka wulaƙantar da kanka da mahaifinka.
31 Tant que le fils de Jessé vit sur la terre, ta royauté n'a pas de consistance. Maintenant donc, envoie quelqu'un prendre ce jeune homme, car il est fils de la mort.
Muddin ɗan Yesse yana da rai a duniya, ba za ka kahu ba. Sarautarka kuma ba za tă kahu ba. Yanzu sai ka je ka kawo mini shi. Dole yă mutu.”
32 Mais, Jonathan répondit à Saül: Pourquoi mourrait-il? qu'a-t-il fait?
Yonatan ya ce wa mahaifinsa, “Me ya sa zai mutu? Me ya yi?”
33 Et Saül leva sa javeline contre Jonathan pour le tuer; Jonathan reconnut ainsi que la méchanceté de son père contre David touchait à sa consommation, et qu'il voulait le faire périr.
Amma Shawulu ya jefe shi da māshi don yă kashe shi. A nan ne Yonatan ya san lalle mahaifinsa ya yi niyya yă kashe Dawuda.
34 Plein de courroux, il quitta brusquement la table, et, le second jour de la lune, il ne prit aucun aliment, parce qu'il était accablé de douleur à cause de David, et que la violence de son père contre celui-ci avait éclaté.
Yonatan ya tashi daga tebur cin abincin da fushi. A rana ta biyun kuwa bai ci abinci ba, gama yana baƙin ciki game da rashin kunyar mahaifinsa game da Dawuda.
35 Le matin venu, Jonathas sortit dans la plaine comme il en était convenu avec David, et il emmena un jeune garçon.
Da safe Yonatan ya tafi domin yă sadu da Dawuda a fili. Ya tafi tare da wani ƙaramin yaro.
36 Et il dit à l'enfant: Cours, trouve-moi les flèches que j'ai lancées. Le serviteur courut, et Jonathan tira une seconde flèche plus loin que la première.
Ya ce wa yaron, “Yi ruga da gudu ka nemo kibiyoyin da na harba.” Da yaron ya ruga sai ya harba kibiya a gaba da shi.
37 Et l'enfant arriva où était celle-ci. Et Jonathan lui cria: L'autre flèche est plus loin;
Da yaron ya isa wurin da kibiyan Yonatan ya fāɗi, Yonatan ya kira shi ya ce, “Kibiyan na gabanka fa.”
38 Et Jonathan lui cria: vite, hâte-toi, ne t'arrête point. Et l'enfant ramassa les flèches de Jonathan, et il les rapporta à son maître.
Sai ya tā da murya ya ce, “Maza, yi sauri kada ka tsaya.” Yaron ya ɗauko kibiya ya kawo wa maigidansa.
39 Or, l'enfant ne savait rien; il n'y avait d'informés que Jonathan et David.
(Yaron kuwa bai san kome game da wannan abu ba, sai Yonatan da Dawuda kawai.)
40 Et Jonathan donna au serviteur son arc et ses flèches, et il dit: Va- t'en, retourne à la ville.
Yonatan ya ba wa yaron makaman ya ce, “Ka ɗauka ka koma gari.”
41 Comme l'enfant y arrivait, David sortit des rochers, tomba la face contre terre, et adora trois fois Jonathan; ensuite, ils se baisèrent tous les deux, et ils pleurèrent tous les deux jusqu'à ce qu'ils se séparassent.
Da yaron ya tafi, sai Dawuda ya tashi daga inda ya ɓuya kusa da tarin duwatsu, ya rusuna har sau uku. Sa’an nan suka sumbaci juna, suka yi kuka, Dawuda kuwa ya yi kuka sosai.
42 Et Jonathan dit à David: Va en paix, que notre mutuel serment subsiste; car nous avons juré, au nom du Seigneur, quand nous avons dit: Le Seigneur sera témoin pour toujours entre toi et moi, entre ma postérité et la tienne. David s'éloigna donc, et Jonathan rentra dans la ville.
Yonatan ya ce wa Dawuda, “Sauka lafiya, mun riga mun yi rantsuwar abokantaka da juna a cikin sunan Ubangiji cewa, ‘Ubangiji ne shaida tsakanina da kai, tsakanin zuriyarka da zuriyata har abada.’” Sai Dawuda ya tafi, Yonatan kuwa ya koma gari.

< 1 Samuel 20 >