< 1 Rois 17 >

1 Or, Elie le prophète thesbite, de Thesba en Galaad, dit à Achab: Vive le Seigneur, Dieu des armées, Dieu d'Israël, devant qui je suis, il n'y aura en ces années ni rosée ni pluie, sinon à ma voix.
To, Iliya mutumin Tishbe, daga Tishbe a Gileyad, ya ce wa Ahab, “Muddin Ubangiji, Allah na Isra’ila wanda nake bauta wa yana a raye, ba za a yi raɓa ko ruwan sama a’yan shekaru masu zuwa ba, sai ko na faɗa haka.”
2 Et la parole du Seigneur vint à Élie, disant:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya, ta ce,
3 Va-t'en d'ici du côté de l'orient, et cache-toi dans le torrent de Chorrath, en face du Jourdain.
“Ka bar nan, ka nufi wajajen gabas, ka ɓuya a Rafin Kerit, gabas da Urdun.
4 Tu boiras de l'eau du torrent, et j'ordonnerai aux corbeaux de te nourrir en ce lieu.
Za ka sha daga rafin, zan kuma umarci hankaki su ciyar da kai a can.”
5 Et Elie fit selon la parole du Seigneur; il s'établit dans le torrent de Chorrath, en face du Jourdain.
Saboda haka sai Iliya ya yi abin da Ubangiji ya faɗa masa. Ya tafi Rafin Kerit, gabas da Urdun, ya zauna a can.
6 Et les corbeaux lui apportèrent des pains à l'aurore, et des chairs le soir; et il but de l'eau du torrent.
Hankaki suka riƙa kawo masa abinci da nama, safe da yamma, ya kuma sha daga rafin.
7 Quelque temps après le torrent se tarit, car il n'y eut point de pluie sur la terre.
Ana nan sai rafin ya bushe saboda ba a yi ruwan sama a ƙasar ba.
8 Et la parole du Seigneur vint à Elie, disant:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Iliya cewa,
9 Lève-toi et va-t'en à Sarepta chez les Sidoniens; là, j'ai prescrit à une femme veuve de te nourrir.
“Je ka, nan take, zuwa Zarefat na Sidon, ka zauna a can. Na umarci wata gwauruwa a can tă ciyar da kai.”
10 Et il se leva, et il partit pour Sarepta; arrivé devant les portes de la ville, il y vit une femme veuve qui ramassait du bois. Et Elie cria après elle, et il lui dit: Prends un peu d'eau dans une cruche, et je boirai.
Saboda haka sai ya tafi Zarefat. Sa’ad da ya isa ƙofar gari, sai ga wata gwauruwa tana tattara’yan itace. Sai ya kira ta, ya ce, “Ki kawo mini ɗan ruwa a tulu don in sha.”
11 Elle en alla prendre; puis, le prophète cria après elle, et il lui dit: Apporte-moi un morceau du pain que tu as en ta maison.
Da ta kama hanya za tă tafi tă kawo, sai ya sāke kiranta ya ce, “Ina roƙonki, ki kuma kawo mini ɗan abinci.”
12 Mais la femme répondit: Vive le Seigneur ton Dieu! je n'ai pas un seul pain cuit, je n'ai qu'un peu de farine dans la maie et quelques gouttes d'huile dans la fiole; je vais ramasser deux petits morceaux de bois; puis, je rentrerai, et je pétrirai pour moi et mes enfants; nous mangerons, et après nous mourrons.
Sai ta ce masa, “Na rantse da Ubangiji Allahnka, ba ni da wani abinci, sai dai ɗan gari hannu guda a tulu, da kuma ɗan mai a kwalaba. Ina tattara’yan itacen nan ne don in kai gida in yi abinci wa kaina da ɗana, don mu ci, mu mutu.”
13 Elie répliqua: Rassure-toi; rentre et fais ce que tu viens de dire; fais de plus pour moi un petit pain; tu me l'apporteras d'abord, tu en feras ensuite pour toi et pour tes enfants.
Iliya ya ce mata, “Kada ki ji tsoro. Ki tafi gida, ki yi yadda kika ce. Amma da farko ki yi mini’yar wainar burodi daga abin da kike da shi ki kawo mini, sa’an nan ki yi wani abu wa kanki da kuma ɗanki.
14 Car voici ce que dit le Seigneur: La maie ne manquera plus de farine, et l'huile ne baissera plus dans la fiole, jusqu'au jour où le Seigneur donnera de la pluie à la terre.
Gama abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila ya ce, ‘Tulun garin ba zai ƙare ba, kwalabar man kuma ba zai bushe ba sai ranar da Ubangiji ya bayar da ruwan sama a ƙasar.’”
15 Et la femme s'en alla; elle pétrit, elle mangea; et le prophète et ses enfants mangèrent.
Sai ta tafi, ta yi yadda Iliya ya faɗa mata. Saboda haka aka kasance da abinci kowace rana wa Iliya da kuma don macen da iyalinta.
16 Et la maie ne manqua plus de farine, et l'huile ne baissa pas dans la fiole, selon la parole que le Seigneur avait dite par la voix d'Elie.
Gama tulun garin bai ƙare ba, kwalabar man kuma bai bushe ba, kamar yadda Ubangiji ya faɗa wa Iliya.
17 Après cela, le fils de la femme maîtresse de la maison tomba malade, et sa maladie fut très violente; enfin le souffle de la vie se retira de lui.
Ana nan sai ɗan matan, wato, gwauruwan nan ya fara ciwo. Ciwon ya ƙara muni, daga ƙarshe sai ya daina numfashi.
18 Et la femme dit à Elie: Qu'y a-t-il entre moi et toi, homme de Dieu? Es-tu venu chez moi pour rappeler le souvenir de mes péchés, et pour faire mourir mon fils?
Sai ta ce wa Iliya, “Mutumin Allah, yaya haka? Ka zo ne domin ka nuna wa Allah zunubaina, ka kuma jawo mutuwar ɗana?”
19 Et le prophète répondit à la femme: Donne-moi ton fils. Et il le prit de son sein; et il le porta dans la chambre où il demeurait, et il l'étendit sur sa couche.
Iliya ya ce, “Ki miƙa mini ɗanki.” Sai ya ɗauke shi daga hannuwanta, ya kai shi ɗakin sama inda yake zama, ya kwantar da shi a gadonsa.
20 Là, il cria et il dit: Malheur à moi, Seigneur! je vous prends à témoin en faveur de cette veuve chez qui j'habite; vous l'avez affligée en faisant mourir son fils.
Sa’an nan ya yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, don me ka kawo wannan masifa a kan gwauruwan nan? Kai ka ce in zauna tare da ita, ga shi yanzu ɗanta ya mutu.”
21 Ensuite, il souffla trois fois sur l'enfant, il invoqua le Seigneur, et il dit: Seigneur mon Dieu, que l'âme de cet enfant revienne en lui.
Sai ya kwanta, ya miƙe kansa a kan yaron sau uku, ya kuma yi kuka ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji Allahna, ka mai da ran yaron nan!”
22 Et il en fut ainsi. L'enfant jeta un grand cri;
Ubangiji kuwa ya ji kukan Iliya, sai ran yaron ya dawo masa, ya kuma rayu.
23 Et Elie descendit de sa chambre dans la maison, et il le rendit à sa mère; et il lui dit: Regarde, ton enfant est en vie.
Iliya ya ɗauki yaron ya sauko da shi daga ɗakin sama zuwa cikin gida. Ya ba da shi ga mahaifiyarsa, ya ce, “Duba, ɗanki yana da rai!”
24 Et la femme dit à Elie: Je reconnais que tu es un homme de Dieu; la parole de Dieu dans ta bouche est véritable.
Sai matar ta ce wa Iliya, “Yanzu na san cewa kai mutumin Allah ne, Ubangiji kuma yana magana ta wurinka.”

< 1 Rois 17 >