< Abdias 1 >

1 Vision d’Obadia. Ainsi parle le Seigneur Dieu au sujet d’Edom: Nous avons entendu une annonce de la part de l’Eternel, un messager a été envoyé parmi les nations: "Debout! Levons-nous contre lui pour combattre!"
Wahayin Obadiya. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce a kan Edom. Mun ji saƙo daga wurin Ubangiji cewa, An aiki jakada zuwa ga al’ummai yă faɗa musu cewa, “Ku tashi, mu tafi mu yi yaƙi da ita.”
2 Voici, je te fais petit parmi les peuples, tu es méprisable au possible.
“Duba, zan maishe ki ƙarama a cikin al’ummai; za a rena ki ƙwarai.
3 L’Infatuation de ton cœur t’a égaré, ô toi qui habites les pentes des rochers, qui as établi ta demeure sur les hauteurs et qui dis en toi-même: "Qui pourrait me faire descendre à terre?"
Fariyar zuciyarki ta yaudare ki, ke da kike zama can bisa duwatsu kika kuma yi gidanki a kan ƙwanƙoli, ke da kike ce wa kanki, ‘Wa zai iya saukar da ni ƙasa?’
4 Quand même tu fixerais ton aire aussi haut que l’aigle et la placerais dans la région des étoiles, je t’en précipiterais, dit l’Eternel.
Ko da yake kina firiya kamar gaggafa kin kuma yi sheƙarki a can cikin taurari, daga can zan saukar da ke,” in ji Ubangiji.
5 Si ce sont des voleurs qui viennent contre toi, des détrousseurs de nuit, comme tu seras éperdu! Ne pilleront-ils pas tout ce qu’ils pourront? Si ce sont des vendangeurs qui viennent contre toi, que laisseront-ils sinon de quoi grappiller?
“In ɓarayi suka zo miki, in kuma’yan fashi suka shigo gidan da dare, kash, bala’i zai jira ki ba abin da suke so ne kawai za su sata ba? In kuma masu tsinka’ya’yan inabi suka zo miki, ba sukan bar’ya’yan inabi kaɗan ba?
6 Ah! comme Esaü est fouillé en tous sens! comme ses retraites mystérieuses sont mises à découvert!
Amma za a washe Isuwa ƙaƙaf, a kuma yaye ɓoyayyiyar dukiyarsa!
7 Ils te poursuivent jusqu’aux frontières, tous ceux qui étaient tes alliés; ils te trompent, ils te maîtrisent, tes prétendus amis! Le pain qu’ils t’apportent, c’est un piège sous tes pas, et tu ne l’as pas compris!
Dukan waɗanda kike tarayya da su, za su kore ki zuwa iyaka; abokanki kuma za su yaudare ki, su kuma sha ƙarfinki; waɗanda suke cin abincinki, za su sa miki tarko, amma ba za ki gane ba.
8 Certes, en ce jour, dit l’Eternel, je ferai disparaître les sages en Edom et la prudence sur le mont d’Esaü.
“A wannan rana,” in jin Ubangiji, “zan hallaka masu hikimar Edom, zan shafe mutane masu fahima a duwatsun Isuwa.
9 Tes guerriers, ô Têmân, seront paralysés, de sorte que tout homme sur le mont d’Esaü soit exterminé lors du carnage.
Jarumawanki, ya Teman, za su razana, za a kashe kowane mutum a duwatsun Isuwa.
10 A cause de ta cruauté à l’égard de ton frère Jacob, tu seras couvert de honte, et ta ruine sera éternelle.
Saboda halin kama-karyar da kika yi wa ɗan’uwanka Yaƙub, za ki sha kunya; za a hallaka ki har abada.
11 Le jour où tu te postas comme spectateur, alors que les barbares emmenaient son armée captive, que l’étranger envahissait ses portes et partageait Jérusalem au sort, toi aussi tu fus comme l’un d’eux.
A ranan nan kin tsaya kawai kina zuba ido yayinda baƙi suke washe dukiyar ɗan’uwanki, baƙi kuma suka shiga ta ƙofofinsa suka jefa ƙuri’a don a rarraba Urushalima, kin tsaya kina kallo kamar ɗaya daga cikin abokan gābansa.
12 Ah! cesse donc d’être un témoin complaisant du jour de ton frère, du jour de son malheur, de triompher des fils de Juda au jour de leur ruine et d’ouvrir aussi grande ta bouche au jour de la détresse!
Bai kamata ki rena ɗan’uwanki a ranar masifarsa ba, ko ki yi farin ciki a kan mutanen Yahuda a ranar hallakarsu, ko ki yi fariya sosai a ranar wahalarsu.
13 Cesse de franchir la porte de mon peuple au jour du revers; au jour du revers, ne te repais point, toi aussi, du spectacle de ses maux; au jour du revers ne fais pas main basse sur ses richesses!
Bai kamata ki bi ta ƙofofin mutanena a ranar bala’insu ba, ko ki rena su a cikin masifarsu a ranar bala’insu, ko ki ƙwace dukiyarsu a ranar bala’insu ba.
14 Ne monte pas la garde à l’angle des routes pour achever ses fuyards, pour livrer ses débris au jour de l’angoisse!
Bai kamata ki tsaya a mararraba don ki kashe waɗanda suke ƙoƙarin tserewa ba, ko ki ba da waɗanda suka tsere ga hannun maƙiyansu a ranar wahalarsu ba.
15 Quand approchera le jour du Seigneur pour toutes les nations, comme tu as fait il te sera fait, tes œuvres retomberont sur ta tête.
“Ranar Ubangiji ta yi kusa don dukan al’ummai. Kamar yadda kuka yi, haka za a yi muku; ayyukanku za su koma a kanku.
16 Oui, comme vous avez bu sur ma montagne sainte, ainsi les nations boiront sans discontinuer; elles boiront et en perdront la raison, elles seront comme si elles n’avaient jamais été.
Kamar yadda kuka sha a kan tuduna mai tsarki, haka dukan al’ummai za su yi ta sha, za su sha, su kuma sha su zama sai ka ce ba su taɓa kasancewa ba.
17 Mais sur le mont Sion un débris subsistera et sera une chose sainte, et la maison de Jacob rentrera en possession de son patrimoine.
Amma a kan Dutsen Sihiyona za a sami ceto; Dutsen zai zama mai tsarki, gidan Yaƙub kuma zai mallaki gādonsa.
18 La maison de Jacob sera un feu, la maison de Joseph une flamme, la maison d’Esaü un amas de chaume: ils le brûleront, ils le consumeront, et rien ne survivra de la maison d’Esaü: c’est l’Eternel qui le dit.
Gidan Yaƙub zai zama kamar wuta, gidan Yusuf kuma kamar harshen wuta; gidan Isuwa zai zama kamar tattaka, za a kuma sa masa wuta yă ƙone. Babu wanda zai tsira daga gidan Isuwa.” Ni Ubangiji na faɗa.
19 Le Midi héritera de la montagne d’Esaü, et la Plage, du territoire des Philistins; ils reprendront la campagne d’Ephraïm et la campagne de Samarie, et Benjamin le pays de Galaad.
Mutane daga Negeb za su mamaye duwatsun Isuwa, mutane kuma daga gindin tuddai za su mallaki ƙasar Filistiyawa. Za su mamaye filayen Efraim da Samariya, Benyamin kuwa zai mallaki Gileyad.
20 Et les exilés de cette légion d’enfants d’Israël, répandus depuis Canaan jusqu’à Çarefat, et les exilés de Jérusalem, répandus dans Sefarad, possèderont les villes du Midi.
Wannan ƙungiyar Isra’ilawan da aka kwashe zuwa bauta da suke a Kan’ana za su mallaki ƙasar har zuwa Zarefat; waɗannan da aka kwashe zuwa bauta daga Urushalima da suke a Sefarad za su mallaki garuruwan Negeb.
21 Et des libérateurs monteront sur la montagne de Sion, pour se faire les justiciers du mont d’Esaü; et la royauté appartiendra à l’Eternel.
Masu kawo ceto za su haura zuwa Dutsen Sihiyona don su yi mulkin duwatsun Isuwa. Ubangiji ne zai yi mulki.

< Abdias 1 >