< Jérémie 7 >

1 Parole qui fut adressée à Jérémie de la part de l’Eternel comme suit:
Maganar da ta zo wa Irmiya ke nan daga Ubangiji.
2 "Place-toi à la porte de la maison de l’Eternel, et prononce là le discours que voici en disant: Ecoutez la parole de l’Eternel, vous tous, gens de Juda, qui entrez par ces portes pour vous prosterner devant l’Eternel!
“Ka tsaya a ƙofar gidan Ubangiji, a can kuwa ka yi shelar wannan saƙo. “‘Ku ji maganar Ubangiji, dukanku mutanen Yahuda waɗanda suke shiga ta waɗannan ƙofofi don yin sujada ga Ubangiji.
3 Ainsi parle l’Eternel-Cebaot, Dieu d’Israël: Amendez vos voies et vos oeuvres, et je vous laisserai résider en ce lieu.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allahna Isra’ila, yana cewa ku gyara hanyoyinku da ayyukanku, zan kuwa bar ku ku zauna a wannan wuri.
4 Ne vous fiez pas à cette formule trompeuse: "C’Est ici le sanctuaire de l’Eternel, le sanctuaire de l’Eternel, le sanctuaire de l’Eternel!"
Kada ku dogara ga maganganun nan na ruɗarwa cewa, “Wannan shi ne haikalin Ubangiji, haikalin Ubangiji, haikalin Ubangiji!”
5 Car si vous corrigez sérieusement vos voies et vos oeuvres, si vous pratiquez une justice sévère dans vos relations réciproques;
In dai kuka canja hanyoyinku da ayyukanku kuma kuna aikata adalci da junanku,
6 si vous vous abstenez d’opprimer l’étranger, l’orphelin et la veuve, de répandre du sang innocent en ce lieu, et de suivre des dieux étrangers, pour votre malheur,
in ba ku zalunci baƙo, maraya ko gwauruwa ba kuma in ba ku zub da jinin marar laifi a wannan wuri ba, in kuma ba ku bi waɗansu alloli da za su cuce ku ba,
7 alors seulement je vous laisserai résider ici, dans le pays que j’ai donné à vos ancêtres, de siècle en siècle.
to, zan bar ku ku zauna a wannan wuri, a ƙasar da na ba kakanninku har abada abadin.
8 Mais voici! Vous vous fiez à des formules trompeuses, dont la valeur est nulle.
Amma ga shi, kuna dogara ga maganganu na ruɗami marasa amfani.
9 Eh quoi! Vous allez voler, tuer, commettre des adultères, faire de faux serments, encenser Baal et suivre des dieux étrangers, que vous ne connaissez point;
“‘Za ku yi sata da kisa, ku yi zina da rantsuwar ƙarya, kuna ƙone turare wa Ba’al kuna kuma bin waɗansu allolin da ba ku sani ba,
10 puis, vous venez vous présenter devant moi, dans ce temple qui porte mon nom, vous écriant: "Nous sommes sauvés!" pour pratiquer encore toutes ces mêmes abominations!
sa’an nan ku zo ku tsaya a gabana a wannan gida, wanda ake kira da Sunana, kuna cewa, “An cece mu,” mun dace mu aikata waɗannan abubuwa banƙyama?
11 Mais elle est donc devenue à vos yeux une caverne de brigands, cette maison qui porte mon nom! Eh bien, moi aussi, j’ai vu les choses de cette façon, dit l’Eternel.
Wannan gidan da ake kira da Sunana ya zama kogon’yan fashi ne a gare ku? Amma ina kallo! In ji Ubangiji.
12 Mais rendez-vous donc à la demeure que j’avais à Silo, où tout d’abord j’avais fait résider mon nom, et voyez comment je l’ai traitée à cause de la perversité de mon peuple Israël!
“‘Yanzu ku fita zuwa Shilo inda na fara maishe shi wurin zama don Sunana, ku ga abin da na yi masa saboda muguntar mutanen Isra’ila.
13 Et maintenant, puisque vous commettez tous ces actes, dit l’Eternel, que je me suis adressé à vous sans cesse, et dès la première heure, sans être écouté par vous, que je vous ai appelés sans obtenir de réponse,
Yayinda kuke yin dukan waɗannan abubuwa, in ji Ubangiji, na yi muku magana sau da sau, amma ba ku ji ba; na kira ku, amma ba ku amsa ba.
14 je traiterai la maison qui porte mon nom et vous inspire cette confiance ainsi que la résidence que je vous ai assurée, à vous et à vos ancêtres, comme j’ai traité Silo;
Saboda haka, abin da na yi wa Shilo shi ne yanzu zan yi wa gidan da ake kira da Sunana, haikalin da kuka dogara a kai, wurin da na ba ku da kuma kakanninku.
15 je vous rejetterai de devant ma face, comme j’ai rejeté tous vos frères, toute la race d’Ephraïm.
Zan kore ku daga gabana, kamar yadda na yi ga dukan’yan’uwanku, mutanen Efraim.’
16 Quant à toi, n’intercède pas pour ce peuple, ne profère en sa faveur ni supplication ni prière, ne cherche pas à me fléchir, car je ne t’écouterai pas.
“Saboda haka kada ka yi addu’a don wannan mutane ko ka yi wani kuka ko roƙo dominsu, gama ba zan ji ka ba.
17 Ne vois-tu pas ce qu’ils font dans les villes de Juda et dans les rues de Jérusalem?
Ba ka gani abin da suke yi a biranen Yahuda da kuma a titunan Urushalima?
18 Les enfants ramassent du bois, leurs pères allument le feu et les femmes pétrissent de la pâte pour confectionner des gâteaux en l’honneur de la reine des cieux, pour faire des libations aux dieux étrangers, avec l’intention de me blesser.
Yara sukan tara itace, iyaye suka hura wuta, mata kuma sukan kwaɓa kullu don su yi wa Sarauniyar Sama waina. Sukan miƙa hadayun sha ga waɗansu alloli don su tsokane ni in yi fushi.
19 Mais est-ce moi qu’ils blessent? dit l’Eternel; n’est-ce pas plutôt eux-mêmes, à leur propre confusion?
Amma ni ne suke tsokana? In ji Ubangiji Ashe, ba kansu ne suke cuta, suna kunyata kansu ba?
20 C’Est pourquoi ainsi parle l’Eternel: "Voici, ma colère enflammée va fondre sur ces lieux, sur les hommes et les animaux, sur les arbres des champs et les fruits de la terre; elle brûlera sans s’éteindre.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa fushina da hasalata za su kwarara a wannan wuri, a kan mutum da dabba, a kan itatuwan fili da a kan amfanin gona, za su yi ta kuna, ba kuwa za a kashe ba.
21 Ainsi parle l’Eternel-Cebaot, Dieu d’Israël: "Joignez vos holocaustes à vos autres sacrifices et mangez-en la chair.
“‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa ci gaba, ku ƙara hadayun ƙonawarku da sauran sadakoki ku kuma yi ta cin naman!
22 Car je n’ai rien dit, rien ordonné à vos ancêtres, le jour où je les ai fait sortir du pays d’Egypte, en fait d’holocauste ni de sacrifice.
Gama sa’ad da na fitar da kakanninku daga Masar na kuma yi musu magana, ban ba su dokoki kawai game da hadayun ƙonawa da sadakoki ba,
23 Mais voici l’ordre que je leur ai adressé, savoir: "Ecoutez ma voix, et je serai votre Dieu et vous serez mon peuple; suivez de tout point la voie que je vous prescris, afin d’être heureux."
amma na ba su wannan umarni cewa ku yi mini biyayya, zan kuwa zama Allahnku ku kuma ku zama mutanena. Ku yi tafiya cikin dukan hanyoyin da na umarce ku, don ku zauna lafiya.
24 Or, ils n’ont point obéi, point prêté l’oreille; ils ont suivi leurs inspirations, tes instincts de leur coeur vicieux, ils ont rétrogradé au lieu d’avancer.
Amma ba su saurara ba, ba su kuwa kula ba; a maimako, suka bi shawarar kansu da ta taurare muguwar zukatansu. Su ja da baya a maimakon yin gaba.
25 Depuis le jour où vos ancêtres sortirent du pays d’Egypte jusqu’à présent, je vous ai envoyé tous mes serviteurs, les prophètes, je les ai envoyés journellement, chaque matin;
Daga lokacin da kakanninku suka bar Masar har yă zuwa yau, kullum na yi ta aikan bayina annabawa.
26 mais ils ne m’ont pas écouté, ils n’ont pas prêté l’oreille; ils ont raidi leur nuque, ils ont fait pis que leurs pères.
Amma ba su saurare ni ba, ba su kula ba. Sai suka taurare zukatansu suka aikata mugun abu fiye da na kakanninsu.’
27 Et tu leur diras toutes ces choses, mais ils ne t’écouteront point; et tu les interpelleras, mais ils te laisseront sans réponse.
“Sa’ad da ka faɗa musu wannan duka, ba za su saurare ka ba; sa’ad da ka kira su, ba za su amsa ba.
28 Tu leur diras alors: "Voici le peuple qui est sourd à la voix de l’Eternel, son Dieu, et rebelle aux remontrances; chez lui la fidélité est morte, elle est bannie de sa bouche!"
Saboda haka ka faɗa musu cewa, ‘Wannan ce al’ummar da ba tă yi biyayya ga Ubangiji Allahnta ba, ba kuwa ta karɓi gyara ba. Gaskiya ta ƙare; ta ɓace gaba ɗaya daga leɓunansu.
29 Coupe ta belle chevelure et jette-la à terre, exhale tes plaintes sur les hauteurs, car l’Eternel repousse, abandonne la race qui a encouru sa colère.
“‘Ku aske gashin kanku ku zubar; ku yi makoki a filayen tuddai, gama Ubangiji ya ƙi’yan zamanin nan ya kuma rabu da su saboda fushin da suka ba shi.
30 Oui, les enfants de Juda ont fait ce que je réprouve, dit l’Eternel, ils ont placé leurs idoles immondes dans la maison qui porte mon nom, pour la profaner.
“‘Mutanen Yahuda sun yi mugunta a gabana, in ji Ubangiji. Sun kafa gumakansu masu banƙyama a gidan da ake kira da Sunana suka ƙazantar da shi.
31 Ils ont bâti les hauts-lieux du Tofèt, dans la vallée de Ben-Hinnom, pour brûler leurs fils et leurs filles par le feu, chose que je n’ai point commandée et qui est loin de ma pensée.
Sun gida masujadan Tofet a Kwarin Ben Hinnom don miƙa’ya’yansu maza da mata a wuta, abin da ban yi umarni ba, ba kuwa yi tunaninsa ba.
32 C’Est pourquoi, voici que des jours viennent, dit l’Eternel, où il sera question, non plus de Tofèt ni de vallée de Ben-Hinnom, mais de vallée d’égorgement, et où l’on enterrera les morts à Tofèt, faute de place.
Saboda haka ku yi hankali, kwanaki suna zuwa in ji Ubangiji, sa’ad da mutane ba za su ƙara kira wurin Tofet ko Kwarin Ben Hinnom ba, amma Kwarin Kisa, gama za su binne matattu a Tofet sai har ba sauran wuri.
33 Et les cadavres de ce peuple serviront de pâture aux oiseaux du ciel et aux bêtes de la terre, sans que personne les trouble.
Sa’an nan gawawwakin wannan mutane za su zama abinci ga tsuntsayen sama da kuma namun jeji, ba za a kuwa sami wani da zai kore su ba.
34 Et je ferai disparaître des villes de Juda et des rues de Jérusalem les cris de joie et les chants d’allégresse, la voix du fiancé et la voix de la fiancée, car ce pays sera devenu un désert.
Zan kawo ƙarshen muryar murna da farin ciki da muryar amarya da ango a garuruwan Yahuda da kuma a titunan Urushalima, gama ƙasar za tă zama kufai.

< Jérémie 7 >