< 2 Chroniques 30 >

1 Ezéchias envoya un message à tout Israël et Juda; il écrivit aussi des lettres à Ephraïm et Manassé, les invitant à venir au temple de l’Eternel à Jérusalem, pour célébrer la Pâque en l’honneur de l’Eternel, Dieu d’Israël.
Sai Hezekiya ya aika wa dukan Isra’ila da Yahuda, ya kuma rubuta wasiƙu zuwa Efraim da Manasse, yana gayyatarsu su zo haikalin Ubangiji a Urushalima, su kuma yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji, Allah na Isra’ila.
2 Le roi et ses chefs et toute la communauté de Jérusalem furent d’avis de célébrer la Pâque au second mois.
Sarki da fadawansa da dukan taro a Urushalima suka yanke shawara su yi Bikin Ƙetarewa a wata na biyu.
3 Car ils n’avaient pu la célébrer en ce temps-là, parce que les prêtres ne s’étaient pas sanctifiés en nombre suffisant et que le peuple ne s’était pas réuni à Jérusalem.
Ba su iya yinsa a daidai lokacinsa ba domin babu isashen firistocin da suka tsarkake kansu, mutane kuma ba su taru a Urushalima ba.
4 La chose plut aux yeux du roi et aux yeux de toute l’assemblée,
Shirin ya yi kyau ga sarki da kuma dukan taron.
5 et ils décidèrent de proclamer par tout Israël, de Bersabée à Dan, qu’on eût à venir célébrer la Pâque en l’honneur de l’Eternel, Dieu d’Israël, à Jérusalem, car on ne l’avait pas de longtemps célébrée ainsi qu’il était écrit.
Suka yanke shawara su yi shelar a ko’ina a Isra’ila, daga Beyersheba zuwa Dan, suna kiran mutane su zo Urushalima, suka kuma yi Bikin Ƙetarewa ga Ubangiji Allah na Isra’ila. Ba a yi bikin da mutane masu yawa bisa ga abin da aka rubuta ba.
6 Les courriers partirent, nantis des lettres de la main du roi et de ses chefs, dans tout Israël et Juda, pour dire, conformément à l’ordonnance du roi: "Enfants d’Israël, revenez à l’Eternel, Dieu d’Abraham, d’Isaac et d’Israël, afin qu’il revienne à ce reste de vous qui a pu échapper à la main des rois d’Assyrie.
Bisa ga umarnin sarki, sai’yan aika suka tafi ko’ina a Isra’ila da Yahuda da wasiƙu daga sarki da kuma daga fadawansa, wasiƙar tana cewa, “Mutanen Isra’ila, ku dawo ga Ubangiji Allah na Ibrahim, Ishaku da Isra’ila, domin yă dawo gare ku, ku da kuka tafi, ku da kuka kuɓuce daga hannun sarakuna Assuriya.
7 Ne soyez point semblables à vos pères et à vos frères, qui furent infidèles à l’Eternel, Dieu de leurs pères, de sorte qu’il les livra à la désolation, comme vous le voyez.
Kada ku zama kamar iyayenku da’yan’uwanku, waɗanda suka yi rashin aminci ga Ubangiji Allah na kakanninsu, har ya mai da su abin tsoro, yadda kuke gani.
8 A présent, ne roidissez pas votre nuque comme vos pères; tendez la main vers l’Eternel, venez dans son sanctuaire, qu’il a consacré à jamais, servez l’Eternel, votre Dieu, afin qu’il détourne de vous le feu de sa colère.
Kada ku yi taurinkai, yadda iyayenku suka yi; ku miƙa kai ga Ubangiji. Ku zo wuri mai tsarki, wanda ya tsarkake har abada. Ku bauta wa Ubangiji Allahnku, domin fushi mai zafi yă juye daga gare ku.
9 C’Est par votre retour à l’Eternel que vos frères et vos enfants trouveront de la pitié auprès de leurs ravisseurs, de façon à retourner dans ce pays, car clément et miséricordieux est l’Eternel, votre Dieu, et il ne détournera pas sa face de vous, si vous revenez à lui."
In kuka dawo wurin Ubangiji, sa’an nan waɗanda suka kama’yan’uwanku da’ya’yanku za su nuna musu tausayi, su kuma dawo wannan ƙasa, gama Ubangiji Allahnku mai alheri ne mai jinƙai kuma. Ba zai kau da fuskarsa daga gare ku ba, in kuka dawo gare shi.”
10 Les courriers passèrent de ville en ville dans le pays d’Ephraïm et de Manassé jusqu’en Zabulon, mais on se railla d’eux et on les bafoua.
’Yan aika suka tafi gari-gari a cikin Efraim da Manasse, har zuwa Zebulun, amma mutane suka yi musu dariyar reni, suka kuma yi musu ba’a.
11 Seuls des hommes d’Aser, de Manassé et de Zabulon s’humilièrent et vinrent à Jérusalem.
Duk da haka, waɗansu mutanen Asher, Manasse da Zebulun suka ƙasƙantar da kansu suka tafi Urushalima.
12 En Juda aussi la main de Dieu agit pour leur donner un même cœur, afin d’accomplir l’ordre du roi et des chefs selon la prescription de l’Eternel.
Haka ma a Yahuda, hannun Allah yana a kan mutane don yă ba su zuciya ɗaya su yi abin da sarki da fadawansa suka umarta, suna bin maganar Ubangiji.
13 Une population nombreuse se réunit à Jérusalem pour célébrer la fête des azymes au second mois; ce fut une affluence énorme.
Taron mutane mai girma ya haɗu a Urushalima don Bikin Burodi Marar Yisti a wata na biyu.
14 Ils se levèrent, ôtèrent les autels qui se trouvaient à Jérusalem; ils enlevèrent aussi les encensoirs et les jetèrent au torrent du Cédron.
Suka kawar da bagadai a Urushalima suka fid da bagadan turare suka zubar da su a Kwarin Kidron.
15 Puis ils immolèrent le sacrifice pascal le quatorze du second mois; les prêtres et les Lévites eurent honte, se sanctifièrent et apportèrent des holocaustes au temple de l’Eternel.
Suka yanka ɗan ragon Bikin Ƙetarewa a rana ta goma sha huɗu na wata na biyu. Firistoci da Lawiyawa suka ji kunya suka tsarkake kansu, suka kawo hadayun ƙonawa a haikalin Ubangiji.
16 Ils se tinrent à leur place selon leur règle, conformément à la loi de Moïse, homme de Dieu; les prêtres versaient le sang que leur passaient les Lévites.
Sa’an nan suka ɗauki matsayinsu na kullum yadda yake a Dokar Musa mutumin Allah. Firistoci suka yayyafa jinin da Lawiyawa suka ba su.
17 Car il y en avait beaucoup dans l’assemblée qui ne s’étaient point sanctifiés, et les Lévites étaient chargés d’immoler les sacrifices pascaux pour tous ceux qui n’étaient pas purs, afin de les consacrer à l’Eternel.
Da yake da yawa cikin taron ba su tsarkake kansu ba, dole Lawiyawa su yanka’yan ragunan Bikin Ƙetarewa domin dukan waɗanda ba su da tsarki, ba su kuma iya tsarkake ragunansu ga Ubangiji ba.
18 Une grande partie du peuple, beaucoup de gens d’Ephraïm et de Manassé, d’Issachar et de Zabulon, ne s’étaient pas purifiés; ils avaient mangé l’agneau pascal sans égard aux prescriptions; mais Ezéchias avait intercédé pour eux, disant: "L’Eternel, qui est bon, absoudra
Ko da yake yawancin mutanen da suka zo daga Efraim, Manasse, Issakar da Zebulun ba su tsarkake kansu ba, duk da haka suka ci Bikin Ƙetarewa, ba tare da bin abin da yake a rubuce ba. Amma Hezekiya ya yi addu’a dominsu cewa, “Bari Ubangiji, wanda yake nagari, yă gafarta wa kowa
19 quiconque aura disposé son cœur à rechercher l’Eternel, Dieu de ses pères, même sans la purification de sainteté."
wanda ya sa zuciyarsa ga neman Allah, Ubangiji Allah na kakanninsa, ko da shi marar tsarki ne bisa ga dokokin wuri mai tsarki.”
20 L’Eternel exauça Ezéchias et pardonna au peuple.
Ubangiji kuwa ya ji Hezekiya ya kuma warkar da mutane.
21 Les enfants d’Israël se trouvant à Jérusalem célébrèrent donc la fête des Azymes sept jours, en grande joie, et les Lévites et les prêtres louèrent l’Eternel jour par jour, avec des instruments puissants en l’honneur de l’Eternel.
Isra’ilawan da suka kasance a Urushalima suka yi Bikin Burodi Marar Yisti kwana bakwai da farin ciki mai girma, yayinda Lawiyawa da firistoci suke rera ga Ubangiji kowace rana, haɗe da kayan kiɗin yabon Ubangiji.
22 Ezéchias adressa des encouragements à tous les Lévites qui se montraient très entendus au service de l’Eternel. Ils consommèrent les repas de la fête durant les sept jours, offrant des sacrifices d’actions de grâces et rendant hommage à l’Eternel, Dieu de leurs pères.
Hezekiya ya yi magana mai ƙarfafawa ga dukan Lawiyawa waɗanda suka nuna ganewar fasaha a hidimar Ubangiji. Kwana bakwai suka ci rabonsu da aka tsara, suka miƙa hadayun salama, suka kuma yabi Ubangiji Allah na kakanninsu.
23 Toute l’assemblée fut d’accord pour célébrer sept autres jours, et ils célébrèrent sept jours de réjouissances.
Dukan mutanen suka yarda su ƙara kwana bakwai kuma, sai suka ci gaba da bikin cikin farin ciki har waɗansu kwana bakwai kuma.
24 Car Ezéchias, roi de Juda, avait prélevé pour l’assemblée mille taureaux et sept mille moutons, les chefs avaient prélevé pour l’assemblée mille taureaux et dix mille moutons et des prêtres s’étaient sanctifiés en grand nombre.
Hezekiya sarkin Yahuda ya tanada bijimai dubu ɗaya da tumaki da kuma awaki dubu bakwai wa taron, fadawa kuma suka tanada musu bijimai dubu da kuma tumaki da awaki dubu goma. Firistoci masu yawa suka tsarkake kansu.
25 Toute l’assemblée de Juda se réjouit, ainsi que les prêtres, les Lévites, toute la foule venue du pays d’Israël et les étrangers, ceux qui étaient venus du pays d’Israël et ceux qui résidaient en Juda.
Taron gaba ɗaya na Yahuda suka yi farin ciki, tare da firistoci da kuma Lawiyawa da dukan waɗanda suka taru daga Isra’ila, har ma da baƙi waɗanda suka zo daga Isra’ila da waɗanda suke zama a Yahuda.
26 Il y eut une grande joie à Jérusalem, car depuis le temps de Salomon, fils de David, roi d’Israël, il n’y avait rien eu de semblable à Jérusalem.
Aka yi farin ciki mai girma a Urushalima, gama tun zamanin Solomon ɗan Dawuda sarkin Isra’ila, ba a taɓa yin wani abu kamar haka a Urushalima ba.
27 Les prêtres et les Lévites se levèrent et bénirent le peuple; leur voix fut entendue et leur prière parvint au séjour de Sa sainteté, aux cieux.
Firistoci da Lawiyawa suka tsaya suka albarkace mutane, Allah kuma ya ji su, gama addu’arsu ya kai sama, mazauninsa mai tsarki.

< 2 Chroniques 30 >