< 1 Samuel 29 >

1 Les Philistins concentrèrent toutes leurs troupes à Aphek, tandis que les Israélites étaient campés près de la source qui est à Jezreël.
Filistiyawa suka tattara dukan rundunoninsu a Afek. Isra’ila kuwa suka yi sansani kusa da maɓulɓular da take Yezireyel.
2 Les princes des Philistins s’avancèrent avec leurs troupes de cent et de mille; David et ses hommes formaient l’arrière-garde avec Akhich.
Sa’ad da sarakuna Filistiyawa suke wucewa da rundunarsu na mutum ɗari-ɗari da na dubu-dubu. Dawuda da mutanensa suna biye a baya tare da Akish.
3 Les chefs des Philistins dirent: "Qu’est-ce que ces Hébreux?" Akhich leur répondit: "Mais c’est David, le serviteur de Saül, roi d’Israël, qui a été auprès de moi bien des jours et même des années, et chez qui je n’ai rien trouvé à reprendre depuis son arrivée jusqu’à ce jour."
Komandodin Filistiyawa suka ce, “Waɗannan Ibraniyawa kuma fa?” Akish ya ce, “Wannan shi ne Dawuda hafsan Shawulu, sarkin Isra’ila. Yana nan tare da ni shekara guda ke nan. Ban kuwa taɓa samunsa da wani lahani ba tun daga ranar da ya bar Shawulu.”
4 Les chefs des Philistins se mirent en colère contre lui et lui dirent: "Fais repartir cet homme; qu’il retourne à l’endroit que tu lui as assigné, mais qu’il ne nous accompagne pas à la guerre et ne devienne pas un obstacle contre nous dans le combat; car, comment cet homme se ferait-il bien venir de son maître, si ce n’est avec les têtes de nos soldats?
Amma komandodin Filistiyawa suka yi fushi, suka ce, “Ka sa mutumin nan yă koma zuwa wurin da ka ba shi yă zauna. Ba zai bi mu zuwa wurin yaƙi ba. Yana iya juya a kanmu lokacin yaƙin. Zai iya yin amfani da wannan zarafi yă ciccire kawunanmu don yă faranta wa maigidansa rai?
5 N’Est-ce pas ce même David que les chœurs acclamaient en disant: "Saül a battu ses mille, Et David ses myriades?"
Tuna fa, ba shi ne Dawuda ɗin da ake girmama da rawa da waƙoƙi ana cewa, “‘Shawulu ya kashe dubbai, Dawuda kuwa dubbun dubbai ba’?”
6 Akhich appela David et lui dit: "Par le Dieu vivant! Tu es honnête, ta conduite auprès de moi dans l’armée me plaît, et je n’ai rien trouvé à te reprocher depuis le jour de ton arrivée chez moi jusqu’à ce jour; mais tu n’es pas agréable aux princes.
Saboda haka Akish ya kira Dawuda ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, na amince da kai tun daga ranar da ka zo wurina har yă zuwa yau, ban same ka da wani laifi ba, na kuma yi farin ciki in sa ka a cikin sojojina don ka yi mini aiki. Amma masu mulki nawa ba su yarda da kai ba.
7 Repars donc et va en paix, pour ne pas mécontenter les princes des Philistins.
Sai ka juya ka koma ka isa lafiya ba tare da ɓata wa masu mulkin Filistiyawa rai ba.”
8 Mais, dit David à Akhich, qu’ai-je fait et qu’as-tu trouvé en ton serviteur, du jour où j’ai paru devant toi jusqu’à présent, pour que je ne puisse aller me battre contre les ennemis de mon seigneur le roi?"
Dawuda ya ce wa Akish, “Me na yi? Ka taɓa samun bawanka da laifi tun daga ranar da na zo har zuwa yanzu? Ina dalilin da ba zan tafi tare da kai in yaƙi maƙiyin ranka yă daɗe, sarki ba?”
9 Akhich, reprenant la parole, dit à David: "Je le sais, tu me plais autant que le ferait un ange de Dieu; mais les chefs des Philistins ont dit: Il ne doit pas aller en guerre avec nous.
Akish ya ce, “A ganina kai marar laifi ne kamar mala’ikan Allah, duk da haka shugabannin sojojin Filistiyawa sun ce, ‘Ba zai tafi yaƙi tare da mu ba.’
10 Donc, lève-toi demain de bonne heure avec les serviteurs de ton maître, venus avec toi; vous vous lèverez matin, et, le jour venu, vous partirez."
Ka tashi da sassafe, kai da bayin shugabanka da suka zo tare da kai. Da gari ya waye sai ku kama hanya.”
11 Et David se leva de bonne heure ainsi que ses hommes pour se mettre en route le matin et retourner au pays des Philistins, tandis que ceux-ci montaient vers Jezreël.
Gari na wayewa tun da sassafe Dawuda da mutanensa suka tashi suka kama hanyar komawa ƙasar Filistiyawa. Filistiyawa kuwa suka haura zuwa Yezireyel.

< 1 Samuel 29 >