< Matthieu 15 >

1 Alors les scribes et les pharisiens de Jérusalem viennent à Jésus, disant:
Sai wadansu Farisawa da malamai suka zo wurin Yesu daga Urushalima. Su ka ce,
2 Pourquoi tes disciples transgressent-ils la tradition des anciens, car ils ne lavent pas leurs mains quand ils mangent du pain?
“Meyasa almajiranka suke karya al'adar dattawa? Don ba su wanke hannayen su kafin su ci abinci.”
3 Mais lui, répondant, leur dit: Et vous, pourquoi transgressez-vous le commandement de Dieu à cause de votre tradition?
Yesu ya amsa masu ya ce, “Kuma don me ku ke karya dokar Allah saboda al'adunku?
4 car Dieu a commandé, disant: « Honore ton père et ta mère »; et: « que celui qui médira de père ou de mère, meure de mort »;
Domin Allah ya ce, 'Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka; 'Shi wanda ya yi muguwar magana ga mahaifinsa ko mahaifiyarsa, lallai zai mutu.
5 mais vous, vous dites: Quiconque dira à son père ou à sa mère: Tout ce dont tu pourrais tirer profit de ma part est un don,
Amma kun ce, “Duk wanda ya ce wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa, “Kowanne taimako da za ka samu daga gare ni yanzu baiko ne ga Allah,'”
6 – et il n’honorera point son père ou sa mère. Et vous avez annulé le commandement de Dieu à cause de votre tradition.
wannan mutum ba ya bukatar ya girmama mahaifinsa. Ta wannan hanya kun maida maganar Allah wofi saboda al'adunku.
7 Hypocrites! Ésaïe a bien prophétisé de vous, disant:
Ku munafukai, daidai ne Ishaya ya yi annabci akan ku da ya ce,
8 « Ce peuple m’honore des lèvres, mais leur cœur est fort éloigné de moi;
“Wadannan mutane girmama ni da baki kawai suke yi, amma zukatansu nesa suke da ni.
9 mais ils m’honorent en vain, enseignant comme doctrines des commandements d’hommes ».
Suna mani sujada a banza, domin suna koyar da dokokin mutane a matsayin rukunansu.”
10 Et ayant appelé la foule, il leur dit: Écoutez et comprenez:
Sai ya kira taron mutane zuwa gare shi ya ce masu, “Ku saurara ku fahimta,
11 ce n’est pas ce qui entre dans la bouche qui souille l’homme; mais ce qui sort de la bouche, c’est là ce qui souille l’homme.
ba abin da ke shiga baki ke kazantar da mutum ba. Sai dai, abin da ke fitowa daga baki, wannan shi ya ke kazantar da mutum.”
12 Alors ses disciples, s’approchant, lui dirent: Sais-tu que les pharisiens ont été scandalisés en entendant cette parole?
Sai al'majiran suka zo suka ce masa, “Ka san Farisawa ba su ji dadi ba da suka ji maganan nan?”
13 Mais lui, répondant, dit: Toute plante que mon Père céleste n’a pas plantée sera déracinée.
Yesu ya amsa ya ce, “Kowace shuka wadda ba Ubana na sama ya shuka ba za a tuge ta.
14 Laissez-les; ce sont des aveugles, conducteurs d’aveugles: et si un aveugle conduit un aveugle, ils tomberont tous deux dans une fosse.
Ku kyale su kawai, su makafin jagora ne. In makaho ya ja wa wani makaho gora dukan su za su fada rami.”
15 Et Pierre, répondant, lui dit: Expose-nous cette parabole.
Bitrus ya amsa ya ce wa Yesu, “Ka bayyana wannan misali a garemu,”
16 Et il dit: Et vous aussi, êtes-vous encore sans intelligence?
Yesu ya ce, “Ku ma har yanzu ba ku da fahimta?
17 N’entendez-vous pas encore que tout ce qui entre dans la bouche va dans le ventre, et passe ensuite dans les lieux d’aisances?
Ko baku gani ba duk abin da ke shiga baki zuwa ciki ta haka yake fita zuwa salga?
18 Mais les choses qui sortent de la bouche viennent du cœur, et ces choses-là souillent l’homme.
Amma abubuwan da ke fita daga baki suna fitowa ne daga zuciya. Su ne abubuwan da ke kazantar da mutum.
19 Car du cœur viennent les mauvaises pensées, les meurtres, les adultères, les fornications, les vols, les faux témoignages, les injures:
Domin daga zuciya mugayen tunani suke fitowa, kisan kai, zina, fasikanci, sata, shaidar zur, da zage-zage.
20 ce sont ces choses qui souillent l’homme; mais de manger avec des mains non lavées ne souille pas l’homme.
Wadannan su ne abubuwan da ke kazantar da mutum. Amma ci da rashin wanke hannu baya kazantar da mutum.”
21 Et Jésus, partant de là, se retira dans les quartiers de Tyr et de Sidon.
Sai Yesu ya tafi daga nan ya nufi yankin biranen Taya da Sidon.
22 Et voici, une femme cananéenne de ces contrées-là, sortant, s’écria, lui disant: Seigneur, Fils de David, aie pitié de moi; ma fille est cruellement tourmentée d’un démon.
Sai wata mace Bakan'aniya ta zo daga wannan yanki. Ta daga murya ta ce,” Ka yi mani jinkai, Ubangiji, Dan Dauda; 'yata tana cikin bakar azaba da aljani.”
23 Et il ne lui répondit mot. Et ses disciples, s’approchant, le prièrent, disant: Renvoie-la, car elle crie après nous.
Amma Yesu bai ce mata kome ba. Almajiransa suka zo suka roke shi, suna cewa, “Ka sallame ta, domin tana bin mu da ihu.”
24 Mais lui, répondant, dit: Je ne suis envoyé qu’aux brebis perdues de la maison d’Israël.
Amma Yesu ya amsa ya ce, “Ba a aike ni gun kowa ba sai dai ga batattun tumakin gidan Isra'ila.”
25 Et elle vint et lui rendit hommage, disant: Seigneur, assiste-moi.
Amma ta zo ta durkusa a gabansa, tana cewa, “Ubangiji ka taimake ni.”
26 Et lui, répondant, dit: Il ne convient pas de prendre le pain des enfants et de le jeter aux chiens.
Ya amsa ya ce, “Ba daidai bane a dauki gurasar yara a jefa wa kananan karnuka.
27 Et elle dit: Oui, Seigneur; car même les chiens mangent des miettes qui tombent de la table de leurs maîtres.
Ta ce, “I, Ubangiji, amma ko kananan karnuka suna cin barbashin da ke fadowa daga teburin maigida.”
28 Alors Jésus, répondant, lui dit: Ô femme, ta foi est grande; qu’il te soit fait comme tu veux. Et dès cette heure-là sa fille fut guérie.
Sai Yesu ya amsa ya ce mata, “Mace, bangaskiyarki tana da girma. Bari ya zamar maki yadda ki ke so.”'Yarta ta warke a lokacin.
29 Et Jésus, étant parti de là, vint près de la mer de Galilée; et montant sur une montagne, il s’assit là.
Yesu ya bar wurin ya tafi kusa da tekun Galili. Sai ya hau tudu ya zauna a can.
30 Et de grandes foules vinrent à lui, ayant avec elles des boiteux, des aveugles, des muets, des estropiés, et beaucoup d’autres; et elles les jetèrent à ses pieds, et il les guérit;
Taro mai yawa suka zo gunsa. Suka kawo masa guragu, makafi, bebaye da nakasassun mutane da yawa, da wadansu marasa lafiya. Suka kawo su gaban Yesu, sai ya warkar da su.
31 de sorte que les foules s’étonnèrent en voyant les muets parler, les estropiés guérir, les boiteux marcher, et les aveugles voir; et elles glorifièrent le Dieu d’Israël.
Don haka mutane da yawa suka yi mamaki a lokacin da suka ga bebaye suna magana, nakasassu sun warke, guragu suna tafiya, makafi suna gani. Sai suka daukaka Allah na Isra'ila.
32 Et Jésus, ayant appelé à lui ses disciples, dit: Je suis ému de compassion envers la foule, car voici trois jours déjà qu’ils demeurent auprès de moi, et ils n’ont rien à manger; et je ne veux pas les renvoyer à jeun, de peur qu’ils ne défaillent en chemin.
Yesu ya kira almajiransa zuwa gun sa sai ya ce, “Ina jin tausayin taron, sun kasance tare da ni kwana uku ke nan kuma ba su da abin da za su ci. Bana so in sallame su ba tare da sun ci abinci ba, domin kada su suma a hanya.”
33 Et ses disciples lui disent: D’où aurions-nous dans le désert assez de pains pour rassasier une si grande foule?
Almajiran suka ce masa, “A ina zamu sami isasshiyar gurasa a wannan wuri da babu kowa har ta ishi babban taron nan.”
34 Et Jésus leur dit: Combien avez-vous de pains? Et ils dirent: Sept, et quelques petits poissons.
Yesu ya ce masu, “Gurasa nawa ku ke da ita?” Suka ce, “Bakwai da 'yan kifi marasa yawa.”
35 Et il commanda aux foules de s’asseoir sur la terre.
Sai Yesu ya umarci taron su zauna a kasa.
36 Et ayant pris les sept pains et les poissons, il rendit grâces et les rompit et les donna à ses disciples, et les disciples à la foule.
Ya dauki gurasar nan bakwai da kifin, bayan ya yi godiya, ya kakkarya gurasar ya bada ita ga almajiran Sai almajiran suka ba taron.
37 Et ils mangèrent tous et furent rassasiés; et ils ramassèrent, des morceaux qui étaient de reste, sept corbeilles pleines.
Jama'a duka suka ci suka koshi. Suka tattara gutsattsarin abincin da ya rage, kwando bakwai cike.
38 Or ceux qui avaient mangé étaient 4 000 hommes, outre les femmes et les enfants.
Wadanda suka ci su dubu hudu ne maza, banda mata da yara.
39 Et ayant renvoyé les foules, il monta dans un bateau et vint dans la contrée de Magadan.
Sai Yesu ya sallami taron ya shiga cikin jirgin ruwa ya tafi yankin Magadan.

< Matthieu 15 >