< Luc 1 >

1 Puisque plusieurs ont entrepris de rédiger un récit des choses qui sont reçues parmi nous avec une pleine certitude,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 comme nous les ont transmises ceux qui, dès le commencement, ont été les témoins oculaires et les ministres de la parole,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 il m’a semblé bon à moi aussi, qui ai suivi exactement toutes choses depuis le commencement, très excellent Théophile, de te [les] écrire par ordre,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 afin que tu connaisses la certitude des choses dont tu as été instruit.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Aux jours d’Hérode, roi de Judée, il y avait un certain sacrificateur, nommé Zacharie, de la classe d’Abia; et sa femme était des filles d’Aaron, et son nom était Élisabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Et ils étaient tous deux justes devant Dieu, marchant dans tous les commandements et dans toutes les ordonnances du Seigneur, sans reproche.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Et ils n’avaient pas d’enfant, parce qu’Élisabeth était stérile; et ils étaient tous deux fort avancés en âge.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Or il arriva, pendant qu’il exerçait la sacrificature devant Dieu dans l’ordre de sa classe,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 que, selon la coutume de la sacrificature, le sort lui échut d’offrir le parfum en entrant dans le temple du Seigneur.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 Et toute la multitude du peuple priait dehors, à l’heure du parfum.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Et un ange du Seigneur lui apparut, se tenant au côté droit de l’autel du parfum.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Et Zacharie, le voyant, fut troublé, et la crainte le saisit.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Et l’ange lui dit: Ne crains pas, Zacharie, parce que tes supplications ont été exaucées, et ta femme Élisabeth t’enfantera un fils, et tu appelleras son nom Jean.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Et il sera pour toi un sujet de joie et d’allégresse, et plusieurs se réjouiront de sa naissance;
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 car il sera grand devant le Seigneur, et il ne boira ni vin ni cervoise; et il sera rempli de l’Esprit Saint déjà dès le ventre de sa mère.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 Et il fera retourner plusieurs des fils d’Israël au Seigneur leur Dieu.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 Et il ira devant lui dans l’esprit et la puissance d’Élie, pour faire retourner les cœurs des pères vers les enfants, et les désobéissants à la pensée des justes, pour préparer au Seigneur un peuple bien disposé.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Et Zacharie dit à l’ange: Comment connaîtrai-je cela? car moi, je suis un vieillard, et ma femme est fort avancée en âge.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 Et l’ange, répondant, lui dit: Moi, je suis Gabriel, qui me tiens devant Dieu, et j’ai été envoyé pour te parler et pour t’annoncer ces bonnes nouvelles.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Et voici, tu seras muet et tu ne pourras point parler jusqu’au jour où ces choses arriveront, parce que tu n’as pas cru mes paroles qui s’accompliront en leur temps.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Et le peuple attendait Zacharie; et ils s’étonnaient de ce qu’il tardait tant dans le temple.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Et quand il fut sorti, il ne pouvait pas leur parler: et ils reconnurent qu’il avait vu une vision dans le temple; et lui-même leur faisait des signes, et il demeura muet.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Et il arriva que, quand les jours de son ministère furent accomplis, il s’en alla dans sa maison.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Or après ces jours, Élisabeth sa femme conçut, et elle se cacha cinq mois, disant:
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Le Seigneur m’a ainsi fait aux jours où il m’a regardée, pour ôter mon opprobre parmi les hommes.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Et au sixième mois, l’ange Gabriel fut envoyé par Dieu dans une ville de Galilée, nommée Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 à une vierge, fiancée à un homme dont le nom était Joseph, de la maison de David; et le nom de la vierge était Marie.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 Et l’ange étant entré auprès d’elle, dit: Je te salue, toi que [Dieu] fait jouir de sa faveur! Le Seigneur est avec toi; tu es bénie entre les femmes.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Et elle, le voyant, fut troublée à sa parole; et elle raisonnait en elle-même sur ce que pourrait être cette salutation.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 Et l’ange lui dit: Ne crains pas, Marie, car tu as trouvé grâce auprès de Dieu.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Et voici, tu concevras dans ton ventre, et tu enfanteras un fils, et tu appelleras son nom Jésus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Il sera grand et sera appelé le Fils du Très-haut; et le Seigneur Dieu lui donnera le trône de David son père;
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 et il régnera sur la maison de Jacob à toujours, et il n’y aura pas de fin à son royaume. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Et Marie dit à l’ange: Comment ceci arrivera-t-il, puisque je ne connais pas d’homme?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 Et l’ange répondant, lui dit: L’Esprit Saint viendra sur toi, et la puissance du Très-haut te couvrira de son ombre; c’est pourquoi aussi la sainte chose qui naîtra sera appelée Fils de Dieu.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Et voici, Élisabeth ta parente, elle aussi a conçu un fils dans sa vieillesse, et c’est ici le sixième mois pour celle qui était appelée stérile;
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 car rien ne sera impossible à Dieu.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Et Marie dit: Voici l’esclave du Seigneur; qu’il me soit fait selon ta parole. Et l’ange se retira d’auprès d’elle.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Et Marie, se levant en ces jours-là, s’en alla en hâte au pays des montagnes, dans une ville de Juda.
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 Et elle entra dans la maison de Zacharie et salua Élisabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Et il arriva, comme Élisabeth entendait la salutation de Marie, que le petit enfant tressaillit dans son ventre; et Élisabeth fut remplie de l’Esprit Saint,
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 et elle s’écria à haute voix et dit: Tu es bénie entre les femmes, et béni est le fruit de ton ventre!
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Et d’où me vient ceci, que la mère de mon Seigneur vienne vers moi?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Car voici, dès que la voix de ta salutation est parvenue à mes oreilles, le petit enfant a tressailli de joie dans mon ventre.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Et bienheureuse est celle qui a cru; car il y aura un accomplissement des choses qui lui ont été dites de la part du Seigneur.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Et Marie dit: Mon âme magnifie le Seigneur,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 et mon esprit s’est réjoui en Dieu mon Sauveur,
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 car il a regardé l’humble état de son esclave; car voici, désormais toutes les générations me diront bienheureuse;
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 car le Puissant m’a fait de grandes choses, et son nom est saint;
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 et sa miséricorde est de générations en générations sur ceux qui le craignent.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Il a agi puissamment par son bras; il a dispersé les orgueilleux dans la pensée de leur cœur;
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 il a fait descendre les puissants de leurs trônes, et il a élevé les petits;
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 il a rempli de biens ceux qui avaient faim, et il a renvoyé les riches à vide;
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 il a pris la cause d’Israël, son serviteur, pour se souvenir de sa miséricorde
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 (selon qu’il avait parlé à nos pères) envers Abraham et envers sa semence, à jamais. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 – Et Marie demeura avec elle environ trois mois; et elle s’en retourna en sa maison.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Or le temps où elle devait accoucher fut accompli pour Élisabeth, et elle mit au monde un fils.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Et ses voisins et ses parents apprirent que le Seigneur avait magnifié sa miséricorde envers elle, et ils se réjouirent avec elle.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Et il arriva qu’au huitième jour ils vinrent pour circoncire le petit enfant; et ils l’appelaient Zacharie, du nom de son père.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 Et sa mère, répondant, dit: Non, mais il sera appelé Jean.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 Et ils lui dirent: Il n’y a personne dans ta parenté qui soit appelé de ce nom.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Et ils firent signe à son père [qu’il déclare] comment il voulait qu’il soit appelé.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Et ayant demandé des tablettes, il écrivit, disant: Jean est son nom. Et ils en furent tous étonnés.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Et à l’instant sa bouche fut ouverte et sa langue [déliée]; et il parlait, louant Dieu.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Et tous leurs voisins furent saisis de crainte; et on s’entretenait de toutes ces choses par tout le pays des montagnes de la Judée;
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 et tous ceux qui les entendirent, les mirent dans leur cœur, disant: Que sera donc cet enfant? Et la main du Seigneur était avec lui.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 Et Zacharie, son père, fut rempli de l’Esprit Saint, et prophétisa, disant:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Béni soit le Seigneur, le Dieu d’Israël, car il a visité et sauvé son peuple,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 et nous a suscité une corne de délivrance dans la maison de David son serviteur,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 selon ce qu’il avait dit par la bouche de ses saints prophètes, qui ont été de tout temps, (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 une délivrance de nos ennemis et de la main de tous ceux qui nous haïssent;
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 pour accomplir la miséricorde envers nos pères et pour se souvenir de sa sainte alliance,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 du serment qu’il a juré à Abraham notre père, de nous accorder,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 étant libérés de la main de nos ennemis, de le servir sans crainte,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 en sainteté et en justice devant lui, tous nos jours.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 Et toi, petit enfant, tu seras appelé prophète du Très-haut: car tu iras devant la face du Seigneur pour préparer ses voies,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 pour donner la connaissance du salut à son peuple, dans la rémission de leurs péchés,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 par les entrailles de miséricorde de notre Dieu, selon lesquelles l’Orient d’en haut nous a visités,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 afin de luire à ceux qui sont assis dans les ténèbres et dans l’ombre de la mort, pour conduire nos pieds dans le chemin de la paix.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 Et l’enfant croissait et se fortifiait en esprit; et il fut dans les déserts jusqu’au jour de sa manifestation à Israël.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luc 1 >