< Joël 1 >

1 Parole de Yahweh qui fut adressée à Joël, fils de Phatuel.
Maganar Ubangiji wadda ta zo wurin Yowel ɗan Fetuwel.
2 Écoutez ceci, vieillards; prêtez l'oreille, vous tous habitants du pays! Pareille chose est-elle arrivée de vos jours, ou bien dans les jours de vos pères?
Ku ji wannan, ku dattawa, ku kasa kunne, dukan waɗanda suke zaune a ƙasar. Ko wani abu makamancin haka ya taɓa faruwa a kwanakinku ko a kwanakin kakanninku?
3 Faites-en le récit à vos enfants, et vos enfants à leurs enfants, et leurs enfants à une autre génération.
Ku faɗa wa’ya’yanku, bari kuma’ya’yanku su faɗa wa’ya’yansu,’ya’yansu kuma su faɗa wa tsara ta gaba.
4 Ce qu'a laissé le gazam, la sauterelle l'a dévoré; ce qu'a laissé la sauterelle, le yéleq l'a dévoré; ce qu'a laissé le yéleq, le chasil l'a dévoré.
Abin da ɗango ya bari fāri masu girma sun cinye; abin da fāri masu girma suka bari, burduduwa ta cinye; abin da burduduwa ta bari sauran kwari sun cinye.
5 Réveillez-vous, ivrognes, et pleurez; vous tous, buveurs de vin, lamentez-vous, à cause du vin nouveau; car il vous est retiré de la bouche.
Ku farka, ku bugaggu, ku yi kuka! Ku yi kuka da ƙarfi, ku dukan mashayan ruwan inabi; ku yi kuka mai ƙarfi saboda sabon ruwan inabi, gama an riga an ƙwace ta daga leɓunanku.
6 Car un peuple est monté sur mon pays, puissant et innombrable; ses dents sont des dents de lion, et il a des mâchoires de lionne.
Wata al’umma ta mamaye ƙasata, tana da ƙarfi ba ta kuma ƙidayuwa; tana da haƙoran zaki, da zagar zakanya.
7 Il a dévasté ma vigne, et mis en morceaux mon figuier; il les a pelés complètement et abattus; les rameaux sont devenus tout blancs.
Ta mayar da kuringar inabina kango ta kuma lalatar da itatuwan ɓaurena. Ta ɓamɓare bayansu duka ta kuma jefar da su ta bar rassansu fari fat.
8 Désole-toi comme une vierge revêtue du sac, pour pleurer l'époux de sa jeunesse.
Ku yi makoki kamar budurwa a cikin tsummoki tana baƙin ciki domin mijinta na ƙuruciyarta.
9 Offrandes et libations ont été retranchées de la maison de Yahweh; ils sont dans le deuil les prêtres, ministres de Yahweh!
Hadayun hatsi da hadayun sha an yanke su daga gidan Ubangiji. Firistoci suna makoki, su waɗanda suke yi wa Ubangiji hidima.
10 Les champs sont ravagés, le sol est dans le deuil; car le blé est détruit, le vin nouveau est dans la confusion, l'huile languit.
Filaye sun zama marasa amfani, ƙasa ta bushe; an lalatar da hatsi, sabon ruwan inabin ya bushe, mai kuma ba amfani.
11 Soyez confus, laboureurs, lamentez-vous, vignerons, à cause du froment et de l'orge; car la moisson des champs est anéantie.
Ku fid da zuciya, ku manoma, ku yi ihu, ku masu noma inabi; ku yi baƙin ciki saboda alkama da sha’ir, saboda an lalata girbin filaye.
12 La vigne est dans la confusion, et les figuiers languissent; le grenadier, et aussi le palmier et le pommier, tous les arbres des champs sont desséchés; la joie s'est retirée confuse, loin des enfants des hommes.
Kuringar inabin ta bushe itacen ɓaure kuma ya yi yaushi,’ya’yan rumman, itacen dabino da itacen gawasa, dukan itatuwan filaye, sun bushe. Tabbatacce farin cikin’yan adam ya bushe.
13 Prêtres, ceignez-vous et poussez des plaintes; lamentez-vous, ministres de l'autel! Venez, passez la nuit vêtus du sac, ministres de mon Dieu; car l'offrande et la libation sont retenues loin de la maison de votre Dieu.
Ku sa tsummoki, ya firistoci, ku yi makoki; ku yi ihu, ku da kuke yin hidima a gaban bagade. Zo, ku kwana saye da tsummoki, ku waɗanda kuke yi wa Allahna hidima, gama an yanke hadayun hatsi da hadayun sha daga gidan Allahnku.
14 Publiez un jeûne, convoquez une assemblée; réunissez les anciens, tous ceux qui habitent le pays, dans la maison de Yahweh, votre Dieu,
Ku yi shelar azumi mai tsarki; ku kira tsarkakan taro. Ku kira dattawa da kuma dukan mazaunan ƙasar zuwa gidan Ubangiji Allahnku, ku kuma yi kuka ga Ubangiji.
15 et criez à Yahweh: " Ah! quel jour!... " Car le jour de Yahweh est proche! Il vient comme un ravage, de la part du Tout-Puissant!
Kaito saboda wannan rana! Gama ranar Ubangiji ta kusa, za tă zo kamar hallaka daga wurin Maɗaukaki.
16 La nourriture n'a-t-elle pas été retranchée sous nos yeux, ainsi que la joie et l'allégresse, de la maison de notre Dieu?
Ba a yanke abinci a idanunmu, farin ciki da kuma murna daga gidan Allahnmu ba?
17 Les semences ont séché sous leurs mottes; les greniers sont vides, les magasins tombent en ruines, parce que le blé est dans la confusion.
Iri suna ta yanƙwanewa a busasshiyar ƙasa Ɗakunan ajiya sun lalace, an rurrushe rumbunan hatsin, gama hatsi ya ƙare.
18 Comme les bêtes gémissent! Les troupeaux de bœufs sont effarés, parce qu'ils n'ont point de pâture; même les troupeaux de brebis pâtissent.
Ji yadda dabbobi suke nishi! Garkunan shanu sun ruɗe saboda ba su da ciyawa, har garkunan tumaki ma suna shan wahala.
19 Je crie vers vous, Yahweh; car le feu a dévoré les pâturages du désert, la flamme a brûlé tous les arbres des champs.
A gare ka, ya Ubangiji, nake kira, gama wuta ta cinye wurin kiwo harshen wuta kuma ya ƙone dukan itatuwan jeji.
20 Les bêtes sauvages mêmes brament après vous, parce que les courants d'eau sont à sec, et que le feu a dévoré les pâturages du désert.
Har ma namun jeji suna haki gare ka; rafuffuka sun bushe wuta kuma ta cinye wurin kiwo a jeji.

< Joël 1 >