< Luc 5 >

1 Or, un jour que pressé par la foule qui voulait entendre la parole de Dieu, il se tenait sur le bord du lac de Génésareth,
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 il vit deux barques qui stationnaient près du rivage; les pêcheurs étaient descendus pour laver leurs filets.
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 Il monta donc dans une de ces barques, qui était à Simon, et le pria de s’éloigner un peu de terre; puis, s’étant assis, il enseigna le peuple de dessus la barque.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 Lorsqu’il eut cessé de parler, il dit à Simon: « Avance en pleine mer, et vous jetterez vos filets pour pêcher. »
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 Simon lui répondit: « Maître, toute la nuit nous avons travaillé sans rien prendre; mais, sur ta parole, je jetterai le filet. »
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 L’ayant jeté, ils prirent une si grande quantité de poissons, que leur filet se rompait.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 Et ils firent signe à leurs compagnons, qui étaient dans l’autre barque, de venir à leur aide. Ils y vinrent, et ils remplirent les deux barques, au point qu’elles enfonçaient.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 Ce que voyant Simon Pierre, il tomba aux pieds de Jésus en disant: « Éloignes-toi de moi, Seigneur, parce que je suis un pécheur. »
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 Car l’effroi l’avait saisi, lui et tous ceux qui l’accompagnaient, à cause de la capture de poissons qu’ils avaient faite;
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 il en était de même de Jacques et de Jean, fils de Zébédée, les associés de Simon. Et Jésus dit à Simon: « Ne crains pas, car désormais ce sont des hommes que tu prendras. »
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 Aussitôt, ramenant leurs barques à terre, ils quittèrent tout et le suivirent.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 Comme il était dans une ville, voici qu’un homme tout couvert de lèpre, apercevant Jésus, se prosterna la face contre terre, et le pria en disant: « Seigneur, si tu le veux, tu peux me guérir. »
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 Jésus, étendant la main, le toucha et lui dit: « Je le veux, sois guéri »; et à l’instant sa lèpre disparut.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 Et il lui défendit d’en parler à personne; mais: « Va, dit-il, te montrer au prêtre, et offre pour ta guérison ce qu’a prescrit Moïse, pour l’attester au peuple. »
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 Sa renommée se répandait de plus en plus, et l’on venait par troupes nombreuses pour l’entendre et pour être guéri de ses maladies.
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 Pour lui, il se retirait dans les déserts et priait.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 Un jour qu’il enseignait, il y avait là, assis autour de lui, des Pharisiens et des docteurs de la Loi, venus de tous les villages de la Galilée, ainsi que de la Judée et de Jérusalem, et la puissance du Seigneur se manifestait par des guérisons.
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 Et voilà que des gens, portant sur un lit un homme paralysé, cherchaient à le faire entrer et à le mettre devant lui.
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 Et n’en trouvant pas le moyen à cause de la foule, ils montèrent sur le toit et, à travers les tuiles, descendirent le malade avec sa couchette au milieu de tous, devant Jésus.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 Voyant leur foi, il dit: « Homme, tes péchés te sont remis. »
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 Alors les scribes et les Pharisiens se mirent à raisonner et à dire: « Qui est celui-ci qui profère des blasphèmes? Qui peut remettre les péchés, si ce n’est Dieu seul? »
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 Jésus, connaissant leurs pensées, prit la parole et leur dit: « Quelles pensées avez-vous en vos cœurs?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Lequel est le plus facile de dire: Tes péchés te sont remis, ou de dire: Lève-toi et marche?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 Or, afin que vous sachiez que le Fils de l’homme a sur la terre le pouvoir de remettre les péchés: Je te le commande, dit-il au paralytique, lève-toi, prends ta couchette et va dans ta maison. »
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 A l’instant, celui-ci se leva devant eux, prit le lit sur lequel il était couché, et s’en alla dans sa maison en glorifiant Dieu.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 Et tous étaient frappés de stupeur; ils glorifiaient Dieu, et, remplis de crainte, ils disaient: « Nous avons vu aujourd’hui des choses merveilleuses. »
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 Après cela, Jésus sortit, et ayant vu un publicain nommé Lévi, assis au bureau du péage, il lui dit: « Suis-moi. »
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 Et lui, quittant tout, se leva et le suivit.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 Lévi lui donna un grand festin dans sa maison; et une foule nombreuse de publicains et d’autres personnes étaient à table avec eux.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 Les Pharisiens et leurs scribes murmuraient et disaient à ses disciples: « Pourquoi mangez-vous et buvez-vous avec les publicains et les pécheurs? »
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 Jésus leur répondit: « Ce ne sont pas les bien portants qui ont besoin de médecin, mais les malades.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 Je ne suis pas venu appeler les justes à la pénitence, mais les pécheurs. »
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 Alors ils lui dirent: « Pourquoi, tandis que les disciples de Jean et ceux des Pharisiens jeûnent et prient souvent, les vôtres mangent-ils et boivent-ils? »
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 Il leur répondit: « Pouvez-vous faire jeûner les amis de l’Epoux, pendant que l’Epoux est avec eux?
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 Viendront des jours où l’Epoux leur sera enlevé: ils jeûneront ces jours-là. »
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 Il leur proposa encore cette comparaison: « Personne ne met à un vieux vêtement un morceau pris à un vêtement neuf: autrement on déchire le neuf, et le morceau du neuf con vient mal au vêtement vieux.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 Personne non plus ne met du vin nouveau dans de vieilles outres: autrement, le vin nouveau rompant les outres, il se répandra, et les outres seront perdues.
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 Mais il faut mettre le vin nouveau dans des outres neuves, et tous les deux se conservent.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 Et personne après avoir bu du vieux vin, ne veut aussitôt du nouveau; car on dit: Le vieux vin est meilleur. »
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Luc 5 >