< Luc 8 >

1 Peu après, il parcourut les villes et les villages, prêchant et apportant la bonne nouvelle du Royaume de Dieu. Il avait avec lui les douze,
Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
2 et quelques femmes qui avaient été guéries d'esprits mauvais et d'infirmités: Marie, dite de Magdala, de laquelle étaient sortis sept démons,
da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
3 Jeanne, femme de Chuzas, intendant d'Hérode, Susanne, et plusieurs autres qui les servaient de leurs biens.
Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
4 Comme une grande foule s'assemblait et que des gens de toutes les villes venaient à lui, il parla par une parabole:
Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
5 « Le fermier sortit pour semer sa semence. Comme il semait, une partie de la semence tomba le long du chemin; elle fut piétinée, et les oiseaux du ciel la dévorèrent.
“Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
6 Une autre partie de la semence tomba sur le rocher; à peine avait-elle poussé qu'elle se desséchait, faute d'humidité.
Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
7 Une autre est tombée au milieu des épines; les épines ont poussé avec elle et l'ont étouffée.
Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
8 Une autre est tombée dans la bonne terre; elle a poussé et donné cent fois plus de fruits. » En disant cela, il cria: « Que celui qui a des oreilles pour entendre entende! »
Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
9 Alors ses disciples lui demandèrent: « Que signifie cette parabole? »
Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
10 Il dit: « Il vous a été donné de connaître les mystères du Royaume de Dieu, mais aux autres, cela a été donné en paraboles, afin qu'en voyant ils ne voient pas et qu'en entendant ils ne comprennent pas.
Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
11 « Voici la parabole: La semence, c'est la parole de Dieu.
“Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
12 Ceux qui sont sur le chemin, ce sont ceux qui entendent; puis le diable vient et enlève la parole de leur cœur, afin qu'ils ne croient pas et ne soient pas sauvés.
Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
13 Ceux qui sont sur le rocher sont ceux qui, lorsqu'ils entendent, reçoivent la parole avec joie; mais ceux-là n'ont pas de racine. Ils croient pour un temps, puis tombent au moment de la tentation.
Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
14 Ceux qui sont tombés parmi les épines, ce sont ceux qui ont entendu la parole, mais qui, en poursuivant leur chemin, sont étouffés par les soucis, les richesses et les plaisirs de la vie, et ils ne portent pas de fruit à maturité.
Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
15 Ceux qui sont dans la bonne terre, ce sont ceux qui, d'un cœur honnête et bon, ayant entendu la parole, la retiennent fermement et portent du fruit avec persévérance.
Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
16 Personne, après avoir allumé une lampe, ne la couvre d'un récipient ou ne la met sous un lit; mais il la met sur un support, afin que ceux qui entrent voient la lumière.
“Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
17 Car il n'y a rien de caché qui ne doive être révélé, ni de secret qui ne doive être connu et mis en lumière.
Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
18 Prenez donc garde à la manière dont vous entendez. Car celui qui a, on lui donnera; et celui qui n'a pas, on lui ôtera même ce qu'il croit avoir. »
Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
19 Sa mère et ses frères vinrent le voir, mais ils ne purent s'approcher de lui à cause de la foule.
Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
20 Des gens lui dirent: « Ta mère et tes frères sont dehors, ils veulent te voir. »
Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
21 Mais il leur répondit: « Ma mère et mes frères sont ceux qui entendent la parole de Dieu et la mettent en pratique. »
Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
22 Or, un de ces jours, il monta dans une barque, lui et ses disciples, et il leur dit: « Passons de l'autre côté du lac. » Ils se mirent donc à l'eau.
Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
23 Mais comme ils naviguaient, il s'endormit. Une tempête de vent s'abattit sur le lac, et ils prenaient une quantité d'eau dangereuse.
Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
24 Ils s'approchèrent de lui et le réveillèrent en disant: « Maître, Maître, nous sommes en train de mourir. » Il se réveilla et menaça le vent et le déchaînement de l'eau; alors ils cessèrent, et le calme revint.
Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
25 Il leur dit: « Où est votre foi? » Effrayés, ils étaient dans l'étonnement et se disaient les uns aux autres: « Qui donc est celui-ci, pour qu'il commande même aux vents et aux eaux, et qu'ils lui obéissent? ».
Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
26 Ils arrivèrent ensuite dans le pays des Gadaréniens, qui est en face de la Galilée.
Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
27 Lorsque Jésus mit pied à terre, un homme de la ville qui avait des démons depuis longtemps vint à sa rencontre. Il ne portait pas de vêtements, et n'habitait pas dans une maison, mais dans les tombeaux.
Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
28 Voyant Jésus, il poussa un cri, se prosterna devant lui et dit d'une voix forte: « Qu'ai-je à faire avec toi, Jésus, Fils du Dieu Très-Haut? Je t'en prie, ne me tourmente pas! »
Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
29 Car Jésus ordonnait à l'esprit impur de sortir de cet homme. Car l'esprit impur s'était souvent emparé de cet homme. On le gardait sous bonne garde et on le liait avec des chaînes et des entraves. En brisant les liens, il a été poussé par le démon dans le désert.
Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
30 Jésus lui demanda: « Quel est ton nom? » Il dit: « Légion », car beaucoup de démons étaient entrés en lui.
Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
31 Ils le supplièrent de ne pas leur ordonner d'aller dans l'abîme. (Abyssos g12)
Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos g12)
32 Or, il y avait là un troupeau de porcs nombreux qui paissaient sur la montagne, et ils le supplièrent de leur permettre d'entrer dans ceux-là. Et il le leur permit.
A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
33 Les démons sortirent de l'homme et entrèrent dans les porcs, et le troupeau se précipita du haut de la rive escarpée dans le lac et fut noyé.
Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
34 Lorsque ceux qui les nourrissaient virent ce qui était arrivé, ils s'enfuirent et le racontèrent dans la ville et dans les campagnes.
Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
35 Les gens sortirent pour voir ce qui s'était passé. Ils s'approchèrent de Jésus et trouvèrent l'homme d'où étaient sortis les démons, assis aux pieds de Jésus, habillé et sain d'esprit; et ils eurent peur.
Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 Ceux qui avaient vu cela leur racontèrent comment celui qui avait été possédé par des démons avait été guéri.
Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
37 Tous les habitants du pays d'alentour, les Gadaréniens, le prièrent de s'éloigner d'eux, car ils avaient très peur. Alors il monta dans la barque et s'en retourna.
Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
38 L'homme d'où étaient sortis les démons le pria de l'accompagner, mais Jésus le renvoya en disant:
Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
39 « Retourne dans ta maison, et annonce les grandes choses que Dieu a faites pour toi. » Il s'en alla, proclamant dans toute la ville les grandes choses que Jésus avait faites pour lui.
“Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
40 Lorsque Jésus revint, la foule l'accueillit, car tous l'attendaient.
Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
41 Voici qu'arrive un homme nommé Jaïrus. C'était un chef de la synagogue. Il se jeta aux pieds de Jésus et le pria d'entrer dans sa maison,
Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
42 car il avait une fille unique, âgée d'environ douze ans, et elle était mourante. Mais, comme il s'en allait, la foule se pressait contre lui.
domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
43 Une femme qui avait un flux de sang depuis douze ans, qui avait dépensé tout son argent en médecins et qui ne pouvait être guérie par aucun d'eux,
A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
44 vint derrière lui et toucha la frange de son manteau. Aussitôt, le flux de son sang s'arrêta.
Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
45 Jésus dit: « Qui m'a touché? » Comme tous le niaient, Pierre et ceux qui étaient avec lui dirent: « Maître, la foule te presse et te bouscule, et tu dis: « Qui m'a touché? »".
Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
46 Mais Jésus dit: « Quelqu'un m'a touché, car je me suis aperçu qu'une force était sortie de moi. »
Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
47 La femme, voyant qu'elle n'était pas cachée, vint en tremblant; et, se jetant à terre devant lui, elle lui déclara, en présence de tout le monde, la raison pour laquelle elle l'avait touché, et comment elle avait été guérie aussitôt.
Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
48 Il lui dit: « Ma fille, réjouis-toi. Ta foi t'a guérie. Va en paix. »
Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
49 Comme il parlait encore, quelqu'un de la maison du chef de la synagogue vint lui dire: « Ta fille est morte. Ne trouble pas le maître. »
Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
50 Mais Jésus, l'entendant, lui répondit: « N'aie pas peur. Crois seulement, et elle sera guérie. »
Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
51 Lorsqu'il arriva à la maison, il ne laissa entrer personne, si ce n'est Pierre, Jean, Jacques, le père de l'enfant et sa mère.
Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
52 Tous pleuraient et la pleuraient. Mais il dit: « Ne pleurez pas. Elle n'est pas morte, mais elle dort. »
Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
53 Ils se moquaient de lui, sachant qu'elle était morte.
Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
54 Mais il les fit tous sortir, et, la prenant par la main, il l'appela en disant: « Enfant, lève-toi! »
Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
55 Son esprit revint, et elle se leva aussitôt. Il ordonna qu'on lui donne quelque chose à manger.
Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
56 Ses parents furent stupéfaits, mais il leur ordonna de ne rien dire à personne de ce qui s'était passé.
Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.

< Luc 8 >