< Luc 16 >

1 Il dit aussi à ses disciples: « Il y avait un homme riche qui avait un gérant. On lui reprocha que cet homme gaspillait ses biens.
Yesu ya ce wa almajiransa, “An yi wani mai arziki wanda aka yi wa manajansa zargin yin banza da dukiyarsa.
2 Il l'appela et lui dit: « Qu'est-ce que j'entends dire de toi? Rends compte de ta gestion, car tu ne peux plus être gérant.
Sai ya kira manajan, ya tambaye shi, ‘Me nake ji haka a kanka? Ka kawo lissafin aikinka, domin ba za ka iya cin gaba da aikinka ba.’
3 « Le gérant se dit en lui-même: « Que vais-je faire, puisque mon seigneur m'enlève le poste de gérant? Je n'ai pas la force de creuser. J'ai honte de mendier.
“Sai manajan ya ce cikin tunaninsa, ‘Maigidana zai kore ni daga aiki, me zan yi? Ba ni da ƙarfin noma, kuma ina jin kunyan yin bara.
4 Je sais ce que je ferai, afin que, lorsque je serai relevé de mes fonctions, on me reçoive dans sa maison.
Na san abin da zan yi, don mutane su karɓe ni a gidajensu, bayan an kore ni daga aiki a nan.’
5 Appelant chacun des débiteurs de son maître, il dit au premier: « Combien dois-tu à mon maître? »
“Sai ya kira kowane ɗaya da maigidansa yake bin bashi. Ya tambayi na farkon ya ce, ‘Nawa ne maigidana yake bin ka?’
6 Il répondit: « Cent batos d'huile ». Il lui dit: « Prends ton billet, assieds-toi vite et écris cinquante ».
“Ya amsa ya ce, ‘Garwar mai na zaitun guda ɗari tara.’ “Manajan ya ce, ‘Ga takardarka, ka zauna maza ka mai da shi ɗari huɗu.’
7 Il dit ensuite à un autre: « Combien dois-tu? Il répondit: « Cent cors de blé ». Il lui dit: « Prends ta note, et écris quatre-vingts.
“Ya kuma tambayi na biyun, ‘Kai fa, nawa ne ake bin ka?’ “Sai ya amsa ya ce, ‘Buhunan alkama dubu.’ “Ya ce, ‘Ga takardarka, ka mai da shi ɗari takwas.’
8 « Son seigneur a félicité le gérant malhonnête parce qu'il avait agi avec sagesse, car les enfants de ce monde sont, dans leur propre génération, plus sages que les enfants de la lumière. (aiōn g165)
“Maigidan kuwa ya yabi manajan nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama’yan duniyan nan suna da wayon yin hulɗa da junansu fiye da’yan haske. (aiōn g165)
9 Je vous le dis, faites-vous des amis au moyen de mammon inique, afin que, lorsque vous échouerez, ils vous reçoivent dans les tentes éternelles. (aiōnios g166)
Ina gaya muku, ku yi amfani da dukiya na wannan duniya, domin ku sami wa kanku abokai. Saboda bayan dukiyar ta ƙare, za a karɓe ku a wuraren zama da sun dawwama. (aiōnios g166)
10 Celui qui est fidèle en peu de chose l'est aussi en beaucoup. Celui qui est malhonnête pour peu de choses est aussi malhonnête pour beaucoup.
“Duk wanda ana amincewa da shi cikin ƙaramin abu, ana kuma amincewa da shi cikin babba. Kuma duk marar gaskiya cikin ƙaramin abu, zai zama marar gaskiya cikin babba.
11 Si donc vous n'avez pas été fidèles dans les richesses injustes, qui vous confiera les véritables richesses?
In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiya ta wannan duniya ba, wa zai amince muku da dukiya ta gaskiya?
12 Si tu n'as pas été fidèle dans ce qui appartient à autrui, qui te donnera ce qui t'appartient en propre?
In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiyar wani ba, wa zai ba ku dukiya naku, na kanku?
13 Aucun serviteur ne peut servir deux maîtres, car ou bien il haïra l'un et aimera l'autre, ou bien il s'attachera à l'un et méprisera l'autre. Vous ne pouvez pas servir Dieu et Mammon. »
“Babu wani bawa mai iya bauta wa iyayengiji biyu ba. Ko dai ya ƙi ɗaya, ya so ɗayan, ko kuwa ya dāge ga yi wa ɗaya bauta, sa’an nan ya rena ɗayan. Ba za ku iya ku bauta wa Allah tare da bauta wa Mammon (wato, Kuɗi) a lokaci ɗaya ba.”
14 Les pharisiens, qui aimaient l'argent, entendirent aussi toutes ces choses, et ils se moquèrent de lui.
Da Farisiyawa masu son kuɗi suka ji wannan duka, sai suka yi wa Yesu tsaki.
15 Il leur dit: « Vous êtes ceux qui se justifient aux yeux des hommes, mais Dieu connaît vos cœurs. Car ce qui est élevé parmi les hommes est une abomination aux yeux de Dieu.
Ya ce musu, “Ku ne masu mai da kanku marasa laifi a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abu mai daraja a gaban mutane, abin ƙyama ne a gaban Allah.
16 « La loi et les prophètes ont été jusqu'à Jean. Dès lors, la Bonne Nouvelle du Royaume de Dieu est prêchée, et chacun y entre de force.
“An yi shelar Doka da Annabawa har zuwa lokacin Yohanna. Tun daga lokacin nan, bisharar mulkin Allah ne ake wa’azinta, kowa kuma yana ƙoƙarin kutsa kai ya shiga.
17 Mais il est plus facile que le ciel et la terre passent que de faire tomber un petit trait de plume de la loi.
Gama ta fi sauƙi sama da ƙasa su shuɗe, da a ce ɗigo guda ɗaya na rubutun, ya fita ya fāɗi daga cikin Doka.
18 « Quiconque répudie sa femme et en épouse une autre commet un adultère. Celui qui épouse une femme divorcée commet un adultère.
“Duk wanda ya saki matarsa ya auri wata mace, zina ne yake yi. Kuma mutumin da ya auri macen da aka sake, zina ne yake yi.
19 Il y avait là un homme riche, vêtu de pourpre et de fin lin, et vivant chaque jour dans le luxe.
“An yi wani mutum mai arziki wanda yakan sa tufafi masu ruwan shunayya, da kuma na lallausan lilin, yana kuma cikin rayuwar jin daɗi kullum.
20 Un mendiant, nommé Lazare, fut conduit à sa porte, couvert d'ulcères,
A ƙofar gidansa kuma akan ajiye wani mai bara, mai suna Lazarus, wanda jikinsa duk gyambuna ne.
21 et désireux de se nourrir des miettes qui tombaient de la table du riche. Et même les chiens venaient lécher ses plaies.
Shi kuwa yakan yi marmarin cin abin da yakan fāɗi daga tebur na mai arzikin nan. Har karnuka ma sukan zo su lashe gyambunansa.
22 Le mendiant mourut, et il fut emporté par les anges dans le sein d'Abraham. Le riche aussi mourut et fut enseveli.
“Ana nan, sai mai baran ya mutu, kuma mala’iku suka ɗauke shi zuwa gefen Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi.
23 Dans le séjour des morts, il leva les yeux, étant en proie aux tourments, et il vit au loin Abraham, et Lazare dans son sein. (Hadēs g86)
A cikin jahannama ta wuta, inda yana shan azaba, ya ɗaga kai ya hangi Ibrahim can nesa, da kuma Lazarus a gefensa. (Hadēs g86)
24 Il s'écria: « Père Abraham, aie pitié de moi, et envoie Lazare, afin qu'il trempe le bout de son doigt dans l'eau et me rafraîchisse la langue. Car je suis en proie à l'angoisse dans cette flamme.
Sai ya yi masa kira ya ce, ‘Baba, Ibrahim, ka ji tausayina, ka aiki Lazarus ya sa ɗan yatsarsa a ruwa, ya ɗiga mini a harshe saboda in ji sanyi, domin ina shan azaba cikin wannan wuta.’
25 « Mais Abraham dit: 'Mon fils, souviens-toi que toi, de ton vivant, tu as reçu tes bonnes choses, et Lazare, de la même manière, de mauvaises choses. Mais voici qu'il est maintenant réconforté et toi, tu es dans l'angoisse.
“Amma Ibrahim ya ce, ‘Ka tuna fa ɗana, a lokacin da kake duniya, ka sami abubuwa masu kyau naka, Lazarus kuwa ya sami munanan abubuwa. Amma yanzu ya sami ta’aziyya a nan, kai kuwa kana shan azaba.
26 En plus de tout cela, entre nous et vous, un grand fossé est fixé, de sorte que ceux qui veulent passer d'ici à vous ne le peuvent pas, et que personne ne peut passer de là à nous.''
Ban da wannan duka ma, tsakaninmu da kai, akwai wani babban rami da aka yi, yadda waɗanda suke son ƙetarewa daga nan zuwa wurinku, ba za su iya ba, kuma ba mai iya ƙetarewa daga wurinku zuwa wurinmu.’
27 Il dit: « Je te demande donc, père, de l'envoyer dans la maison de mon père -
“Ya amsa ya ce, ‘To, ina roƙonka, ya uba, ka aiki Lazarus zuwa gidan mahaifina,
28 car j'ai cinq frères - afin qu'il leur rende témoignage et qu'ils n'aillent pas eux aussi dans ce lieu de tourments ».
gama ina da’yan’uwana biyar maza. Bari yă ba su gargaɗi, don kada su ma su zo wurin nan mai azaba.’
29 « Mais Abraham lui dit: « Ils ont Moïse et les prophètes. Qu'ils les écoutent.
“Ibrahim ya amsa ya ce, ‘Suna da Musa da Annabawa, ai, sai su saurare su.’
30 « Il répondit: 'Non, père Abraham, mais si quelqu'un leur vient d'entre les morts, ils se repentiront'.
“Sai ya ce, ‘A’a, ya uba, Ibrahim, in dai wani ya tashi daga matattu ya je wurinsu, za su tuba.’
31 « Il lui dit: 'S'ils n'écoutent pas Moïse et les prophètes, ils ne seront pas non plus convaincus si quelqu'un ressuscite d'entre les morts.'"
“Amma ya ce masa, ‘In ba su saurari Musa da Annabawa ba, kai, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su saurare shi ba.’”

< Luc 16 >